Sooraj Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Maman Teddy Category :  Adventure

Chapter   14 / 47

39K to 42K   out of 140.6K words

har mota biyu.  Alhaji Ilyass (maƙocin Sooraj)  dake laɓe jikin gate ɗin gidansa, yana ganin ƴan sanda ya ƙaraso garesu haryana jin tuntuɓe, aruɗe yace.   "Yauwa ranka ya daɗe kun ƙaraso? Ni ne nan naƙiraku, tabbas naji ƙaran harbin bindiga awannan gidan har sau biyu, saboda haka duk yanda akayi babu lafiya!" yafaɗi haka yana me sharce gumin dake yankowa ta gaban goshinsa, gaba ɗaya atsorace yake, ƙiran ƴan sandan ma da yayi baƙaramin Jahadi yake ganin yayi ba, saboda tsorone cike fal aransa. 

Cike da rashin tsoro haka ƴan sandannan suka rarrabu, kowanne daga cikinsu ya saita kunamar bindigarsa, ƙiris sukejira su saki harsasai,  haka sukayi cikin gidan Sooraj,  ahankali suka tura ƙofar falon suka shiga, ganin bakowa acikin falon yasa suka shiga ƴan dube dube, yayinda wasu daga cikinsu suka nufi bedrooms ɗin dake cikin falon, ɗaya bayan ɗaya haka suka shiga suna dubawa, ɗaya daga cikin ƴan sandan ne idanunsa suka sauƙa akan jinin dake kwance ya daskare akan tiles, jawo ogansu yayi ya nuna masa jinin,  aikuwa suna leƙa bayan kujera sukaga mutum yashe aƙasa, gaba ɗaya jini ya ɓata jikinsa, aɗan razane sukayi kanshi, daidai lokacin sauran ƴan sandan suka dawo cikin falon.   "Sir gaba ɗaya fa mungama duba gidannan bakowa acikinsa" suka faɗa suna mai kallon Sooraj dake yashe aƙasa.   Shiru ogannasu yayi tare da ciro wayarshi acikin aljihunsa ya danna ƙiran asibiti.  Kallon sauran ƴan sandan yayi yace subi hanya duk wanda suka gani sukamashi.  hakan kuwa akayi duk suka watse yazama saura mutane ƴan ƙalilan.  Ƙarar jiniyan ambulance ne yacika gidan.    Ɗaukan Sooraj akayi aka sanyashi acikin ambulance ɗin, suka wuce asibiti.
Babban asibitin dake cikin garin Lagos suka wuce dashi, direct ɗakin bada taimakon gaggawa aka nufa dashi, duk da cewa basu da tabbacin cewa yana da rai ko bayidashi.   Dr. Femus shine mutumin daya fara cire handglobes ɗin dake hanunshi, kallon sauran abokan aikinnasa yayi yace.  "He is dead!"   Jikinsune gaba ɗaya yayi sanyi, saboda haka suma suka soma ƙoƙarin cire handglobes ɗin dake hanunsu.

Dr. Fawwaz da bai yarda da abunda Dr.Femus yace ba, yaɗan matso gaf da Sooraj ɗin tare da kama hanunsa ya riƙe, sannan ya ɗaura kansa adai dai saitin ƙirjinsa inda zuciarsa ta ke.  Da sauri ya ɗago da kansa tare da cewa "Bai mutu ba, zuciyarsa na bugawa, muyi sauri mucire masa bullet ɗin dake jikinsa!"   nan suka duƙufa aikin cire bullet ɗin dake jikinsa.    Sunyi masa gwaje gwaje sosai,  inda suka tabbatar da cewa bai mutu ba, amma kuma su kansu basu san awani condition yake ba, abu ɗaya suka sani shine, zai iya wucewa tacan zai kuma iya tashi, duk wannan na Allah Ne.  Duk abun daya kamata suyi mishi sun masa, sannan suka killaceshi awani ɗaki na musamman. 
***
Gaba ɗaya ta hargitsa gadon, sai juye juye take, ta ya mutsa ko ina, gashin kanta gaba ɗaya ya watse akan gadon, yayinda ta sanya hanunta ta damƙi zanin gadon da iya ka ƙarfinta,   duk da cewa sanyin ac na tashi acikin ɗakin, amma ita wani irin gumine ke fitowa daga jikinta.  Arazane ta ware manya manyan idanunta da sukayi jajur dasu, tashi tayi ta zauna tare da dafe ƙirjinta dake bugawa da sauri.   "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!!" tafaɗa cikin wata murya me rauni, kawai saita  samu kanta da fashewa da kuka, kuka tayi sosai wanda itakanta batasan na menene ba, aƙalla taɗauki kusan 40 minute tana kuka harsaida muryarta ta dashe, idanunta ne suka sakeyin jajur dasu,  jin ana ƙiran sallan asuba ne yasata miƙewa ta nufi toilet,  doguwar rigan dake jikinta ta cire tare da tsayawa agaban shower ruwa yashiga dukan ta,   bazata iya tuna mafarkin me tayi ba, amma tabbas tasan taga wani abu wanda yake shirin taɓa rayuwarta,  wani irin bacci tayi wanda adunia bata taɓa bacci marar ɗaɗinsa ba,  MR. HANDSOME shine wanda tunaninsa ya kutso cikin rai da zuciarta,  aƙalla ta ɗauki kusan sama da 15 minute tana tsaye ruwa na dukanta,  da ƙyar ta iya ɗauro alwala tafito, domin gaba ɗaya bata jin ƙarfin jikinta.

Tsayawa tayi agaban madubi tare da kallon kanta, hanu tasanya ta shafi jajayen idanunta wanda suke cike tab da ƙwalla,  ai kuwa take hawayen suka gangaro kan ƙuncinta, ita kanta batasan kukan metakeyi ba, kawai dai tasan tanajin ƙunci acikin zuciyarta, tanajin wani irin babu daɗi acikin ranta, tanajin wani ƙaton rauni ya rataya awuyanta,  gaba ɗaya tuna nin mai taimakone ga cika ranta,  gefe guda kuwa sosai takejin faɗuwar gaba, tana fatan kada wata mummunar ƙaddara tasake
samunta.     Sosai ta jima a raka'an ƙarshe tana kai kukanta ga mai duka, addu'a take kome zai sameta Allah Ya kawo mata shi da sauƙi.  Haka ta zauna akan sallaya har gari yayi haske, ko samun daman sake duba takardan jarabawanta ma batayi ba, gaba ɗaya jin kanta take acikin ƙunci.    Akullum cikin kuzari da ƙarfin jiki ta ke shirya kanta zuwa makaranta, amma yau hakanan take sanya uniform tunani fal ranta.  Jakarta ta saɓa akafaɗa tare da fitowa cikin falon, akullum ta saba haɗawa kanta break fast amma yau batajin zata iyacin komai.     Ba irin tambayan dasu Shukrah basuyi mata ba,  akan tasanar dasu abun dake damunta, amma  tace dasu sam batasan meke damunta ba.    Suna fitowa a exam ta tsaya ajikin wata bishiya,  tare da tsaida idanunta akan hanyar shigowa makarantar, hakanan tasamu kanta da son ganinsa, duk da cewa bawai ta wani damu dashi bane, amma yau da takejin kanta wani iri sai taji tanason ganinsa, tasan ko ma yaya zai iya cireta acikin ƙuncin da take ciki.  Har Kamalu driver yazo tana tsaye ajikin wannan bishian, Saidai kuma har zuwa lokacin  bata ganshiba kamar yanda taso, haka ta koma gida zuciarta ba daɗi.   Indomie ta dafa amma haka ta kasa ci, dole ta zauna jigum tana kallon TV....

LAGOS NIGERIA....  

Ƴan sanda da kansu suka koma gidan Sooraj sukayi bincike, inda suka gano cewa shiɗin cikakken  ma'aikacin CBN ne, don haka direct branch ɗinsu dake Lagos suka nufa, BM ɗin  wajen wanda yakasance tamkar aboki ga Sooraj,  shi suka samu suka sanar dashi gaba ɗaya abundake faruwa,  aikuwa baƙaramin tashi hankalinsa yayi ba,  koda yaje yaga halin da Sooraj yake ciki tamkar gawa, saida ya zubda ƙwalla, nan yaƙira wayan Mas'oud yasanar masa komai da komai, ai Mas'oud tamkar wani zararre haka yazama, wani irin mugun tashin hankali yasamu kanshi aciki, batare daya sanar dasu Abban Sooraj ba ya hawo jirgi yataho Lagos.

Kallon Mas'oud Babban likitan asibitin yayi tare daɗan gyara zamansa yace.  "Inaga basai anfita dashi waje ba ae, amma tunda ka matsa zaku iya fitar dashi, saidai kuma dole muna buƙatar ku ƙara mana sati ɗaya, idan baidawo cikin hayyacinsa ba shikenan sai ku fita dashi"

Shiru Mas'oud yayi tare da sanya hanu ya kama kanshi, adunia ayanzu babu wani mutum dayake tausayi sama da SOORAJ.  Cikin cushashshiyar muryarsa yace.  "Shikenan Dr. Babu damuwa Allah dai ya bashi lafiya!"     da "Ameen" doctor ɗin ya amsa nan sukayi musabaha, Mas'oud ya nufi ɗakin da Sooraj yake kwance, duk da ba abarin kowa ya shiga, amma zaka iya hangoshi ta glass ɗin window'n ɗakin.  Tsayawa yayi ajikin window tare da sauƙe idanunsa akan Sooraj wanda yake kwance flat, bazaka taɓa cewa akwai rai ajikinsaba, saidai na urar dake jikinsa  kawai dake aiki,  wani irin hawayene suka cika idanun Mas'oud, har baisan sanda suka silalo kan ƙuncinsa ba.  "Wani irin ƙaddarori masu girma ne haka suke ɗawainiya da RAJ? yaushe RAJ zai huta? yaushe RAJ zaiyi dariya yayi farinciki kamar kowa? yaushe damuwar RAJ zata yaye?" abun da Mas'oud yake ta tambayar kansa kenan, tausayin SOORAJ yakeji mai tsanani, ayanzu baisan da wani baki zai iya furtawa iyayen Sooraj wannan mummunar labarinba, yace musu ɗansu yana cikin halin rayuwa ko mutuwa, ko kuwa yace musu ɗansu yazama marar amfani, ya zamanto tamkar gawa.   Hanu yasanya ya share hawayen dake kan fuskarsa, aransa yaci alwashin nemo duk wani wanda yake da hanu akan harbin SOORAJ, wayarsa dake ƙara ya ciro ya duba, ganin commisioner'n ƴan sanda ne ke ƙiranshi, yasanyashi fita daga cikin asibitin baki ɗaya bayan ya ɗaga wayar ya kara akan kunnensa.
***
Zaune take akan wani ɗan dakali, yayinda shi kuma yake tsaye abayanta, ɗan ranƙwafo da kansa yayi  daidai saitin kunnenta ahankali yace. 
"Sau ba adadi na faɗa miki banaso ina ganin damuwa akan fuskarki" yaƙare maganar yana mai zagayowa ya zauna aɗan kusa da ita.

Raunannun idanunta ta ɗago ta kalleshi, ga mamakinsa sai kawai yaga hawaye sun gangaro daga cikin idanunta.  Jiyayi wani abu ya soki zuciarsa, lumshe sexy eyes ɗinsa yayi tare da buɗesu alokaci guda. 
"Menene?" yatambayeta cike da kulawa.   Samun kanta tayi da cusa kanta acikin cinyoyinta ta fashe da kuka. Hankalinsa ne yaji ya tashi, cikin yanayi na rashin jin daɗin kukannata yace. "Meke damunkine Baby? wani abu ya samekine? ko wanine ya taɓaki? ko kuma anɓata ranki ne? please dear na faɗamin meke damunki!!" yayi maganar cike da tsantsar nuna kulawarsa gareta.

Ɗago kanta tayi tare da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, ita kanta batasan awani yanayi take ciki ba, batasan meke damunta ba, hakan kawai tasamu kanta da cewa "Yayana ne, yau kusan kwana 10 banganshiba, kuma sannan inayawan jin faɗuwar gaba, inaso naganshi, bansan ina zanganshi ba!" wasu sabbin hawayene suka sake gangarowa daga cikin idanunta.

Ɗan kafeta da idanunsa yayi tare da ɗan yin murmushi,  hakanan yanayin yanda tayi maganar ya burgeshi, yanason mace mai shagwaɓa sosai.   "Kiyi haƙuri kinji Baby na, very soon yayanki zai dawo gareki"

Ɗago idanunta dake cike da ƙwalla tayi ta kalleshi, shima kallon nata yake, cikin wani irin yanayi dayake matuƙar kashe jikin mace, janye idanunta tayi daga kansa, tare da sunkuyar da kanta ƙasa, wasa ta shigayi da yatsun hanunta, aranta tunanin mai taimako ne kawai ke yawo,  duk bayan kowani bugun zuciarta ɗaya da tunaninsa take tafiya.     "Ziyadah!!!" yaƙira sunanta cikin wata cool voice.  Da sauri ta kalleshi cike da mamaki haɗi da yarinta tace.
"A ina kasan sunana?"

Murmushi yayi tare da cewa "Kamar yanda shaƙan numfashi da fitarsa keda matuƙar mahimmanci haka sanin sunanki yake da mahimmanci a wajena, saidai kuma ke ko sau ɗaya baki taɓa tambayar nawa sunan ba why?"

Wani murmushi tayi tare da cewa "To meye sunanka?"

Dariya yayi harsaida fararen haƙwaransa suka bayyana, sosai tambayar tata ta basa daria.  "Sunana FAROUK YUNUS HAMMA ni haifaffen ɗan garin Kano ne, domin har yanzu iyayena acan suke, aiki ne ya kawoni Abuja,  ina zaune a unguwar Wuse zone 2,  ke kuma sunanki Ziyadah kina zaune a unguwar Asokoro,  iya abunda nasani akanki kenan"

Dariya Ziyada tayi tare da kallonsa.  Shima kallonnata yayi, miƙewa tayi ta soma tafiya batare da tace dashi komai ba, da kallo ya bita harta ɓacewa ganinsa, ajiyar zucia ya sauƙe tare da lumshe idanunsa, yanason komai nata, musamman ƴan saffa saffan cute lips ɗinta masu kyau,  ya ɗan jima awajen kafun ya tashi ya shiga motarsa ya tafi......
***
Mas'oud ne keta kai kawo atangamemen falon Alhaji Mai Nasara, gaba ɗaya baya cikin nutsuwarsa, baisan ta ina zai fara ba, baisan taya Alhaji Mai Nasara zai ɗauki maganarsa ba.   
"Mas'oud yana ganka a atsaye? Bismillah kazauna mana" Inji cewar Alh. Mainasara, da fitowarsa kenan daga cikin ɗaki.  Jikin Mas'oud na rawa haka ya zauna akan kujeran tare da sanya hanu ya dafe kanshi.

⚠️NOT EDITED

(Kuyi manage banda enough charge)

*VOTE AND COMMENT*
[4/23, 12:04 PM] +234 814 541 1152: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

            *SOORAJ !!!*

    *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Life (Sardauna)*

*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*

            *WATTPAD*
      @fatymasardauna

#romance

          *Chapter 22*

Jikin Mas'oud na rawa haka ya zauna akan kujeran, tare da sanya hanu ya dafe kanshi. 
Kallonsa Alhaji Mansur Mai Nasara yayi tare da cewa.  "Yanayin ka kaɗai ya tabbatarmin da cewa ba lafiya ba Mas'oud, meke faruwa? wani abu yasamu SOORAJ ne?" Alhaji Mansur Mai Nasara ya tambayi Mas'oud, fuskarsa cike da  damuwa.

Shiru Mas'oud yayi ya kasa cewa komai.   "Tabbas akwai matsala kenan" Inji cewar Alhaji Mansur.

Kai Mas'oud ya kaɗa alamar "Eh"

"Sooraj ne?" ya kuma tambaya.

Kai Mas'oud yasake kaɗawa alamar "Eh"

Hanu Alh.Mansur Mai Nasara yasanya ya dafe daidai saitin zuciyarsa, da ke ɗanyi masa zafi, gaba ɗaya acikin kwanakinnan haka yakejin faɗuwar gaba na ruskarsa, sannan gefe ga Ummu (Hajiya Sulaimiya) ta sameshi da zancen cewa tana yawan mugayen mafarkai akan ɗanta Sooraj.  Lallai tun da yaga Mas'oud a birkice haka, yasan matsalan babbace.   Hular kansa ya cire tare da ajeta agefe, har fargaban tambayar Mas'oud ɗin yake wani hali Sooraj din ke ciki, Sooraj shi kaɗaine ɗansa, sannan kuma yana matuƙar sonsa, sam bayason wani abu ya samu Sooraj, baisan yazaiyi ba, shi ya haifi Sooraj amma baisan Sooraj wani irin mutum bane, komai nasa aɓoye yake,baya bayyana duk wani sirrinsa. kullum cikin ƙunci da damuwa zaka ganshi, ada suna tunanin rashin zama da mace shine  matsalarsa, amma da sukayi masa aure, sai suka ga ashe wannan bashine matsalarsa ba. 

"Abba akwai matsala, Sooraj yana asibitin Lagos baida lafiya,  hari aka kai masa a gidansa dake Lagos!" Mas'oud ya faɗi haka idanunsa suna mai cikowa da ƙwalla. 

Arazane Abba yatashi daga zaunen dayake, tare da rumtse idanunsa. Muryarsa amatuƙar raunane yace.  "Kada kacemin wasu sun cutarmin da Sooraj, Mas'oud, zan iya jure komai, amma banda labari mummuna akan Sooraj, sun kashemin shi ko? " idanun Alhaji Mansur tuni sun ciko da ƙwalla. 

"Ka kwantar da hankalinka Abba, Sooraj bai mutu ba kawai dai yana da buƙatar kulawarku ne ayanzu" Mas'oud yafaɗi haka yana mai ɗan share ƙwallan daya zubo daga cikin idanunsa.

"Kayi mana booking flight Mas'oud, amma banaso Ummu ta sani, yau zamu tafi Lagos" Alh. Mansur yafaɗi haka cike da damuwa. 

Gaba ɗaya Alh. Mansur baya cikin nutsuwarsa, hankalinsa atashe yake sosai, baisan awani hali zaije ya taradda tilon ɗansa ba.  Babban damuwarsa ma itace Ummu, tabbas yasan idan Ummu taji to dole sai ciwonta ya tashi.
***
Yau aɗan acikin nishaɗi ta dawo gida, domin kuwa kwana biyunnan sosai Farouk ke ɗan ɗebe mata kewa, babban abun dayasanya ta shaƙu dashi, shine irin yanda yake kawar mata da damuwarta,  yana sakewa da ita sosai, sannan kuma yana bata dukkan kulawansa, ako da yaushe yakan kashe ayyukansa yazo gareta, hakan yasa tayi sabo dashi.
Gobe zasu kammala jarabawansu, sannan kuma agoben za'a basu hutu.   Fitowarta awanka kenan ta sanya wata doguwar riga ja, kitchine ta wuce, tsaye tayi agaban gas tare dayin shiru, damuwarta ne ta dawo sabuwa fil.  Motsinsa takeson ji acikin gidan, rashin jinsa da kuma rashin ganinsa yana damunta sosai, tanason koda ƙamshinsa ne taji, hakanan takeji ajikinta cewa baya lafiya.  Cikin rashin daɗin rai haka ta soya indomie taci sama sama. Tunda tayi sallah take aikin duba littafin Physics da zasuyi gobe.   Kamar kullum idan ta kwanta mafarkinsa kawai take, yauma hakance ta kasance domin kuwa gaba ɗaya shitake ta gani acikin mafarkinta, yanayin halin da take ganinsa acikin mafarkin sam baya mata daɗi.  

Ƙarfe goma daidai suka fito a exams, direct wajen assembly suka nufa.   Hutun 3 weeks kawai aka basu, duk da haka ɗaliban sunji daɗi sosai. 

Cikin sanyin jiki ta ɗago idanunta ta kalli Farouk wanda shima kallonta yake, gaba ɗaya idanunsa sunyi wasu narai narai dasu,  harshensa yasanya ya ɗan lashi kan lips ɗinsa.
 "Banason wannan hutun, kwata kwata  banason duk wani abu da zai nesantani da ganinki pretty na, da gaske nake inasonki har acikin zuciyata!!"       jin sauƙar kalaman nasa acikin kunnuwanta, ya sata jin tamkar aradu ce ta sauƙa,  idanunta dake kan fuskarsa ne suka kawo ƙwalla,  "So......na!!" tafaɗa murya asarƙe..

Kallonta shima yayi cikin wani irin yanayi,  ɗan matsowa kusa da ita yayi, tare da kai hanunsa ya kama nata hanun.      "Nasan ke ƙaramar yarinyace, sannan kuma bakisan menene so ba, dan inasonki bawai yana nufin zan cutar dake bane, ban taɓa jin soyayyar wata mace  azuciyata kamar yanda nakejin taki soyayyarba, Inasonki Ziyadah, dan Allah Kada ki ƙini, tun ran da naganki nakamu da Sonki, har abada kuma zan ci gaba da sonki, namiki alƙawari  bazan taɓa rabuwa dake ba!!" Yaƙare maganar cikin wata murya mai sanyi, yayinda gaba ɗaya yanayin   idanunsa suka sauya.    Hawayene suka gangaro daga idanun Ziyada, karo na farko arayuwarta da wani yafurta mata kalmar SO, karo na farko arayuwarta da wani namiji ya tsaya yayi mata magana cikin kulawa har haka,  saidai kuma sam bata fahimci kalamansa ba.  Ganin yanda hawaye yake fita daga idanunta ne ya sanyashi, kai hanunsa fuskarta da niyyar share mata hawayen, da sauri taja da baya, tare da ƙwace hanunta dake cikin nasa.   Juyawa tayi cikin yanayi na gudu gudu sauri sauri tabar wajen, ƙiran sunanta Farouk yake amma ko waiwayosa batayi ba, balle yasa ran tsayuwarta,   ajiyar zuciya mai ƙarfi ya sauƙe, tare da lumshe idanunsa da suka soma sauya kala, har acikin jininsa yana jin son yarinyar, komai nata me kyau ne, kallonta, tafiyarta, nutsuwarta,  sau babu adadi yakan samun kansa cikin wani irin yanayi idan yana tare da ita, da ƙyar ya iya shiga motarsa yabar cikin makarantar.

Ziyada kuwa direct inda su Nasmah ke zaune ta nufa, tana zuwa ta faɗa kan cinyar Shukrah, tare da rumtse idanunta.

Kallon kallo Nasmah da Shukra suka shiga yiwa juna, cike da tsantsar kulawa suka haɗa baki wajen tambaryarta.  "Lafiya Ziyada? meke damunki?"  duk waƴannan tambayoyin sunyi mata shine alokaci guda.

Ɗago kanta dake kan cinyar Shukrah tayi, gaba ɗaya hawaye ya ɓata mata fuska.     Ganin haka yasa suka ƙara ruɗewa.

"Kuka Ziyada, meke faruwane?" Inji cewar Shukra dake ƙoƙarin share mata hawaye.

Kanta taɗan girgiza cikin muryarta mai ɗauke da rauni tace.  "Bansan me yake nufi ba Shukra, bansan menene So ba, bansan ya akeyinsa ba, gaba ɗaya ya juyarmin da tunanina, dan Allah Shukra ki faɗamin menene SO?" taƙare maganar tana mai sakin ɗan guntun hawayen dake maƙale cikin idanunta.

Ajiyar zuciya Shukra tayi tare da ɗanyin murmushi.   "Dama nasan haka zata faru Ziyada, saboda tun randa yasake dawowa nasan ya kamu da sonki ne,  So ba ƙarya bane ba Ziyada, akwaita azuciyar kowa, kuma sannan Allah Ne ke halittarta

14 / 47