Author : Aisha Aliyu Garkuwa Category : Romance
ka tuna
ya fada yana kallon fuskar Yusuf din harara Yusuf din ya watsa masa gamida cewa toh ni dai ka kama kanka Dan wlh naga alama zaka jamana raini gun yarinyar nan
Yoh raini kuma Na nawa tunda ta ga gadon baccinsa ta kuma yiwa mararsa kallon tsaf ai raini ya qare anan cewar lamido
Kenan
Adam yace bar Dan iska shima zai worene wannan wuri in kasan dadin da ya qunsa ai bakayi taurin kaiba dry sosai lamido yayi
Shi kuma cikin ta kaici yace wallah tallahi kunji Na muku rantsuwar musulmi ko toh wlh ni kam har a bad a bani ba Aysha kam kodako mata sun qare a duniya koda zan rasa rai nane
Adam ya kalleshi cikin mmk yace ni kuma Na tabbatar kana tare da wahala wotarana
Dai2 lkcin suka zazzauna kan kujera cikin jin kunya Amira ta kawo musu dirings masu sanyi ta gaidasu ganin yadda hamma Yusuf din ya murtuqe fuska yasa ta wuce kitchen dinta taci gaba da aikinta
Basu dade ba Yusuf ya miqe yace su tafi gidan Ahmad
A baking gate sukayi qaro dashi yana kokarin shiga mota cikin tsoro da firgici da tsananin kaduwa suka isa gun shi
da sauri Yusuf ya kamo hannushi.......
FAHIMTARWA
Da yawa suna min qorafin basa fahimtar me sunan littafinnan yake nufi sabida ganin sunan da yaren fullancine ana yawan cemin menene ma,anar MI,WASMITI toh
Manar mi wasmiti dai yana nufin
NAYI NADAMA
Fatan masu karatu kun gane sunan novel din nayi Nadama
Kuma insha Allahu zanci gaba da hada sunan da hausan
Ina godiya da kulawarku
KINA RAINA UMMI Garkuwa marubuciyar Jennifer fatan alkhairi a gareni
Gaisuwa ga dukkan marubutanmu inai mana fatan alkhairi
By garkuwan Fulani
[4/9, 2:25 PM] βͺ+234 909 785 3276β¬: πππππππππ
NAYI NADANA
MI,WASMITI page 4β£1β£to4β£3β£ Na Aysha Ali Garkuwa
πππππππππ
Hannunsa Ya riqe cikin mmk da kdma da tsabar firgici cikin kaduwa yace
Biyaye meke damunka ?
Baka da lfy ko?
Shiyasa yau kwana 2 bakaje gidaba ko ?
Shiru dai baiyi mgn ba
Cikin damuwa yace
Haba Ahmad ya ina mgn kayi shiru
Ji yadda gaba daya ka rame
Ase dama shiyasa kake yawan Sa manyan kaya
Dan ka boye yadda ka sauyane ?
Cikin yanayin shi Na sanyin hali da kawaici da haquri yayi murmushi Garfin hali da qoqarin boye halin da yake ciki
Yace
Ni wlh matsala ta da kai kenan saurin
rudewa jifa yadda ka wani gigice kana ta jeromin
Tabbayoyi
Toh wacce tabbaya daya nasan
Zan amsa maka
Adam ne yace ka gaya mana gsky ya fada cikin son gane me Ahmad din ke son boyewa musu
Dry yayi cikin qarfin hali yace
Bani da wata matsala ni kam
Cikin kura masa ido Yusuf yace ka tabbata?
Yes bani da matsala ya fada yana kamo hannun lamido
Yace on top mu isa kunzo kun tsaidashi a woje
Yusuf ne ya kirashe biyaye
Na,am ya amsa masa
Yace juyo ka kalleni
Cikin dryar tausayawa Kansu da Kansu yace anqi juyo wan
Da sauri Yusuf ya Sha gaban shi yace nace ka kalli qoyar idana ka cemin baka da matsala
Cikin sauri yayi gasa da kanshi
Dan yasan muddin ya bar idon Yusuf cikin nasa toh zai gano halin da yake ciki
Dan su tun suna yara sukan laqanci halin da Dan uwansu yake ta cikin qwayar idan juna koda ko ya boye a fuskarsa
Part dinshi ya nufa riqe da hannun lamido
Cikin karaya da yanayin cushewar tunani Yusuf ya kalli Adam cikin rawar murya yace biyaye inajin tsoro
Wlh tsoro nakeji
Adam kalli yadda Ahmad ya dawo
Adam kasani Na Sani iyayenmu sun Sani su Kansu su Bappa Yaya
Sun San cewa Ahmad Aysha yakeso
Itace burin ranshi
Sun kuwa San zai iya zaucewa in aka hanashi ita
Adam meyasa
Suke son
Sabautamin rayur Dan uwana
Kanshi yake ta jijjigawa da juya idan shi yasa lips enshi Na qasa a baki ya ciza da qarfi
Hawayen da suka cuko a idonsa yakeson su kwaranyo ko zai dainajin nauyin da ya danni qirjinshi
Amman ina abin yaqi
Da qarfi ya riqe hannu Adam yace
Biyaye ni
Banajin kaina banajin Aysha
Dan uwana nakeji
Adam ni
Yanxu Na gama tsara komai Na komawa cshool
Ba Wanda zan gayawa sai kai da Ahmad
Dan banson su Abba su San zan tafi nafiso sai naje Na kirasu Na gaya musu
Amman Adam kaga halin da Ahmad yake ciki
Adam ko dai Na fasa tafiyar Nanne
Adam in natafi Na bar biyaye da kai kadai zaka iya kula dashi
Cikin rawan murya Adam
Yace kaje insha Allahu ba komai yadda zaka barmu lfy haka zaka dawo ka samemu lfy
Duk kulan da kake tunanin zaka bawa Ahmad zan hada da nawa
Cikin murmushi takaici yace
Ya ja hannushi suka bi bayan su a parlo suka yada zaggo suna ta Dan taba hira
Har aka kira sallan LA asar Adam ne ya fara shiga yaje yayi alwala sai lamido yana fita yace
Yusuf kuyi saurifa kunsan innah tanan ca tana jirana kuga dare yanayi
Tare suka miqe Ahmad dinne ya fara shiga yayi alwalan sai Yusuf din ya shiga sauri sauri yayi ya fito
Har yazo baking qofar fita
Sai kuma ya dawo da sauri ganin abin mmk
Da sauri ya fito parlon ya kira Ahmad din hannushi ya jawo har gaban gado ya kalleshi cikin
Tuhuma yace
Biyaye jinin menene wannan a kan shimfidarka har kan pillows dinka ?
Shiru yayi
Cikin kaduwa yace Ahmad tabbayarka fa nakeyi
Cikin inda inda ya kama cewa A.a
Ai dama
Damafa
Biyaye ka Dane inda inda ka gayamin gsky
Lamido ne ya katseshi da cewa wlh kai dai bakaji
Dadiba Yusuf
Ka fiye bincike da qididdigar mutane
Kazo gidan sabbin amare Dan kaga jini a makwancinsu ka tsaya dogon bincike kai Amman dai anyi surkin banxa
Cikin jin dadin zance Ahmad yace qyaleshi dai duk suka fita suna dry Amman banda Yusuf Dan shi ya zargu da jinnan da ya gani
Har zasu fita Adam yace bamufa ga qauwar tamuba
Ras Ahmad yaji gabansa ya fadi har sai da ya fafe qirjinshi danshi har ga Allah mantawa yakeyi da wata a cikin gidan
Lkci daya kuma yaji kunya ta rufeshi ko ba komai Maryam bata cenceci haka daga gareshiba Dan ba laifinta bane
Muryar tane ta katseshi da tunanin da yakeyi
Cikin Dan sakin fuska tace laa ya Adam Hamma Yusuf ya lamido sannuku da zuwa
Da sauri ta nufi kitchen tana bari Na kawo muku abinci Yaya
Ta fada tana kallon fuskarAhmad din shi kuwa da sauri ya kauda ganinshi daga gareta Dan kunyarta yaji sosa
Yusuf ne yace a a Alhamdulillah mun gaisheku wucewa masallaci zamuyi
Cikin Dan tsoro tace
Ayyah Hamma Yusuf da sauri haka
Ko ruwan Baku shaba
Toh mubar sallan kenan ya fada fuska a daure π‘
A ranshi kuma yace ba gashi ba har sun fara tsare mutane da raini
Cikin sanyin murya tace A,a
Toh Ku gaida su Ummi
Harara ya kuma watsa mata yace suwayen yan Aiken naki mu zaki aika
Kai ta girgiza gudun kar ta kuma mgn ya zama laifi
A ranta tace shi kenan Aysha am ke kam kin kade zama da wannan masifeffen
Tare suka fita
Ahmad Na bayan su
Har yazo baking qofar sai ya kuma komawa yazo dab da ita ya Sa hannushi ya tallabo fuskarta cikin rauni da
sanyin murya yace
Maryama kiyi haquri ki gafarceni
Rau rau tayi da ido alamar kuka da sauri ya zaunar da ita kan kujera yace ki yafemin ba nufina kenan Na cuxguna miki ba kimin afuwa yake yar uwata
Cikin sanyin murya tace
Ni baka min komaiba ya Ahmad kuma ko ka minima Na yafe
Cikin farin ciki ya subbaci goshinta ya
fita yana cewa rabbi ya miki albarka
Amin tace cikin jin dadin addu,arshi gareta
3:30 pm su inna sukayi sallama da su Ummi suka kama hanyar Yola sun tafi suna kewan juna
Yau saura kwana 2 Yusuf ya bar Nigeria
Da yamma su Abba da baba bello Na zaune a harabar gidan nasu Yusuf ne yashi cikin nitsuwa ya isa gunsu
Cikin biyeyya yace sannuku da hutawa baba
Abba yanxu naje hospital baka can anata nemenka kawai suna ganina suka tsareni
Baba bello yace a to kace yau ka Sha aiki kenan
ehh wlh baba har C,S nayiwa wata mata
Ayyah me aka cire
?
Da namiji
Masha Allah rabbi ya raya
amin yace
Ya Dan kalli baba bello yace baba
Yanxu zan wuce mambila Dan Na kwana biyu bamu hadu da Bappa Yaya ba
toh yayi kyau ka gai dasu yaushe zaka dawo ?insha Allahu Gobe zan dawo
Abba yace (Allah yare jam wartira on jam)
Allah ya kaika lafya ya dawo da ku lfy
Ameen ya rabbi yace gamida miqewa ya je ya sallami su Ummi ya kama hanyarshi shi kadai π
Gembu Mambilah
Garfe 6 dai2 ya isa farfajiyar gidan ba kowa sai Dan hirarsu da yake juyowa daga cikin parlon baki ya Dan table gaida cewa badu da aiki sai surutu cikin gajiyar hanya
Ya bude Qofar kenan ita kuma tazo da Dan gudu gudun ta kawai sai ji yayi ta fada cikin girjinshi a take yaji jinin jikin shi ya dauke duk yaji tsikar jikishi Na tashi qoqolwar shi tayi dip duk network dinshi ya dauke
Cikin qarfin halin ya sunkuyar da kanshi Dan ganin wacce wannan
dai dai ya tabbatar ko bai ga wayeba yasan macece Dan yaji suka guda biyu a qirjinsa alamun qirjin macece ya have da NASA
Ido ya zaro woje Dan mmk da ganin....
By garkuwan Fulani
[4/9, 2:25 PM] βͺ+234 909 785 3276β¬: πππππππππ
NAYI NADAMA
MI,WASMITI page
4β£4β£to4β£5β£ Na Aysha Ali Garkuwa
πππππππππ
Yarinyar da ya tsana kamar yadda ya tsani abinda zai cutar da biyayenshi
Da sauri cikin jin haushin ta ya yarfa mata mari
Cikin jin zafi da sauri cikin raxana ta dago
Sosai ta qara tsorita ganin fuskar da bata qaunar gani da sauri ta juya dafe da fuska
Cikin zafi nama ya miqo hannu zai cabkota ya dirka mata Na jaki
Sadiq dake gaban ta
Yace kin banu
Aysha kauce
Da sauri ta ruga
A guje bata tsaya ko inaba sai cikin dakin innayi kan gadon mai rumfanta ta dale tana mai kukan takaici
A parlor kuma zama yayi bai kula kowa ba sai faman murtuqe fuska yake da huci
Bappa Yaya ne ya Dan kalleshi da kyau a ransa yake mmkin halin irin Na Yusuf shi har abada ba,a gane far in cikinsa da baking cikinsa ko yaushe fuska ba walwalah
Cikin kula yace
Kai Dudabe meke damunka kaketa huci
Anyi din
Toh yau kuma da bala,i kazo kenan?
Ehh da bala,i nazo
yanxu kai kuma kana da bakin mgn ne
Bala,I da fitina ya wuce wanda ka janyo mana
An janyo din nace an janyo ko
Aikin kawai Dan kaga ina binka ina sonka
Shine kake son ka samin hawan jini
Ka sawa kanka dai
Innace ta kalleshi cikin tsokana tace ayagi sarkin fada ka iso har ka fara daga shiga
Da dukan matarka kayi slm
Sannan ka sauqo kan Bappa an da kuma kanwa zaka kuma hawa
Kanki zan hau nai ta surface miki bala,i matuqar kika qara kiran waccar yar yarinyar kuma muna fuka a matsayin matata
Innayi ce tace toh dibino gwara muyi axumin mgn in ba so muke a hanamu baccin dare da sababiba
Oho dai can ta matse muku ya fada gami da daga kafada
Bappa Yaya ne yace
Toh tashi mu tfi
Masallahci Dudabe am
Bazan je da kaiba haka kawai kai ta wani kirana 'Dudabe
Nacema bana so Amman taurin kai da son ka konamin rai ya hana ka bari π‘
A haka dai sukaje sukayi sallah
Basu dawoba sai da sukayi insha
A parlor suke ta Dan hira yanxu ya Dan sauqo
Cikin kula ya kalli kakan nashi
Yace Bappa Yaya jibi in Allah ya kaimu zan koma wurin karatuna
Dan an nememu kwanannan
Cikin Dan jin sanyi yace
Ayyah dudabe zaka tafi kuma sai mai Nisan kwana
Ko zaka dawo ka samemu ko kuma shike nan an rabu
Duk da halin irin Na Yusuf yana qaunar kakannishi sosai a ranshi yana sonsu fiye da zaton mutum
Cikin qarfin hali yace ba komai kakana zan dawo Na samemu lfy
Innayi tace hmm Yusuf am ai dolene watara kam ka dawo ka samu bamu kan doron qasa π±
hannun ta ya kama ya hada Dana inna yace insha Allah ba komai
Suna cikin hiran Bappa Yaya ya miqawa Yusuf din phone dinshi yace hingo kamo min babanku
Da sauri ya kalleshi cikin tuhuma yace
Me zaka cemai
Kafasan ni bansan gulma
Dan basu San jibi zan komaba Na kuwa sanka da barin zance yanxu zaka shafa musu zancen
Cikin mmk da Al,ajab yake kallonshi
A ranshi yake cewa wato so yake ya zulle ya bar matar shi a nan toh lallaiko yaro shirinka yayi nitsa
A daqile yace
Ina mgn kayi banza dani
A Dan fir ya dawo daga nunanin da ya tfi
Dry yayi irin ta yaro man kaza kenan
A fili kuma cewa yayi toh Na FASA kiranma ba shike nanba?
ehh gwara kam
Ya fadi tare da miqewa ya nufi dakin innayi yana innayi zo kiban tea
Toh tace gamida bin bayan shi
Suna shiga ya hau kan mairumfanta ya kishin qida yana kallon rumfar gadon da yasha kolliya a ranshi yake cewa tabbas wannan gado yayi a rayuwarta kuma insha Allah sai Na shigarda gadonnan cikin tarihin rayuwa
Haka kawai shi kam yake son gadon kakar tasa haka kawai yake jin nishadi in ya hau gadon da farin ciki
Innayi CE ta katsemai π€da yakeyi tana toh ga shayin ko a kan gadon zakasha ne?
A a zan sauqo mana Amman ajiyeshi ya Dan huce
Toh tace gami da dire cup din a qasa
Itako Aysha tunda ta shigo ta.kwanta kan gadon
tana kukan marinta da yayi a.haka bacci ya saceta
Baccinta take cikin jin dadin gadon
Shiko Sam bai lura da ita a kan gadonba
Shiyasa yayi kwanciyarsa
Can cikin bacci ta Dan fara juyi a hankali ta daqo hannuta daya cikin sanyin baccin ta dire hannun kan qirjinshi
Lkci daya kuma ta mirgino da qafarta ta daura kan ququnshi cikin sekon 10 duk ta kanainayeshi
Cikin firgita ya bude idan shi da sauri ya tashi ya zauna har jikin shi Na bari
Cikin takaicin gani wacece ya
Daga hannushi sai da ya dubu kan fuskarta ya watsa mata maruka har 3 ajere cikin kidima da firgici ta saki kuka mai qarfin gami da bin bayan shi ta diro daga kan gadon
Cikin kuka dataje baking qofar ta juyo ta kalleshi cikin tsana tace mugu azzalumi Allah ya isana wlh bazan yafe maka ba ko qabarinka naci da wuta
π³π‘ya zaro mata cikin zafin nama ya diro daga kan gadon yana fadin ke ππ»ni kike zagi ?
Ehh din an zageka azzalumi
Aiko cikin zalumcin ya nufi kanta Dan yana iya babbalata in ya kamata ganin yadda ya nufuta kamar wani ma yunwacin zaki yasa ta arta a guje ππ»ββcikin
Zafin nama ya rufamata baya
bata tsaya ko inaba sai cikin dakin Bappa Yaya
Da sauri ya riqota yana ke Ayshatu lfy kuwa ke da waye
Ita dai ihu take da.iya qarfinta tana
Hamma Yusuf ne Bappa Yaya wlh ka tare shi ka Sani baida imani zai kasheni
Toh me kika masa
Wlh.ni ban masa komaiba shine ya sameni INA baccina kawai yakama dirkata
Shi dai Yusuf huci kawai yake Yayea qoqarin fixgota
Cikin tsawa kakan nasu ya jawata ya turata bayanshi yace je kiyi zamanki kai kuma ficemin a daki ko yanxunnan Na kira ubanka nace kazo dukana
π‘ππ»baki ya ciza gamida kada kai yace wlh zaki shiga hannu Na kuma zaki gane kurenki yayi woje yanata huci
Bayan fitashi ne ya miqowa Aysha woya yace kamo min bello
Karba tayi ta ki rasa sai da ya daga sannnan ta miqa mai ta shige toilet
bayan sun gaisa
Cikin rada rada yace kai bello kasan Dudabe nata shirin tfy jibi jibinnan ko
Ehh yace mai Na Sani Amman shi yana tsamman ban saniba Adam ya zo ya gayamin
Toh batun matarsa fa ?
Ehh ai tare zasu tfi ko baya so Dan yanxu haka Na gama mata shirin tafiyarta kab
Dry yayi cikin jin dadi yace yauwa Allah ya muku albarka daku da zuryarku baki daya
Amin ya rabbi ya fada cikin jin dadi
Sannan yace toh ka kirashi gobe da safe kace ya taho da ita Dan in Nina fada bazai yardaba
Toh shi kenan Bappa
A haka sukayi SLM ya kashe woya yana dryar cin nasara