Mis Wasmiti 1 Complete Hausa Novel

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Romance

Chapter   14 / 38

39K to 42K   out of 112.1K words

/>
Cikin qarfin hali yace

Abba Ku gafarceni ya kuma kallon Nenne da ta fara zama mai daqushewar tunani yace Nenne da sauri ta matsoshi

Yace shin ba INA gaya miki cewar Allah da ya bakini ya fiki sona ba Nenne ya nake ga alamar kareya a idonki da qarfin ta riqo hannushi tace Na yarda Ahmad Na San Wanda ya bani kai ya fini sonka .

Toh Nenne inko hakane addu,arku kawai nakeso

Dan Allah kar ki bin da kuka

Ina ita kam a NEnne tuni ta fashe da kuka

A hankali ya juya kanshi gun baba belle mahaifinshi kenan Cikin murmushin qarfin hali yace

Baba Na zan tafi Na barka

Ga Nenne Na ka kulanmin da ita

hannushi ya kuma riwewa

Baba ka gafarceni idan Na taba yima wani laifin

Cikin qarfin hali baba belli ya daga kanshi yace Ahmad baka min komai ba Kuma koda kamin Na yafe maka duniya da lahira

Ahmad Allah ya bada Sa,an tafiya

Cikin sanyi yakira Abba

Abba Na kuka kake min ? Ya tabba yeshi

Kai Abban ya jinjina Cikin kuka tsosai yace a a Ahmad kaina nake yiwa kuka Ahmad kaina nake kokawa

Da qer ya daga hannushi ya goge qollah😭 da ke bin fuskar Abban yanan murmushi

Cikin sanyi yace Abba Dan Allah INA da tabbayoyin da zan muku

A yau dinnan Ku daure Ku bani amsar su

Kai ya geda yace INA jinka Ahmad tabba yeni matuqar Na sani to zan gaya maka

Cikin gajiyar hrt yace Abba meyasa kuka hanani Auren Aysha?

Meyasa kukace Aure ya haramta a tsakanin mu?

Abba meyasa kuka hadata da Yusuf bayan shi uwa daya uba daya suke da ita ?

Kuma yaushe aka daura Auren Aysha da Yusuf?

A hankali ya kamo hannushi yace wadannan sune tabbayo yin ka ?

Ehh Abba

Cikin sanyi yace toh Ahmad zan amsa makasu kamar yadda ka buqata



Da forko dai Aysha yatace amman ba ta cikina ba cikin gsky da gsky ya nuna Dr Umar Ardo yace wannan shine mahaifin Aysha ma haifiyarta Kuma itace qanwata khadeeja wacce ta rasu

Da sauri Adam yace Abba me kake cewa?

Eh abinda dai kaji Na fada

ya bashi amsa

Cikin dimuwa yace kenan Aysha qanwa tace uwa daya uba daya

Ehh sosai ma kuwa

Nan ya fara basu amsoshin tabba yartasu

Kamar yadda kuka Sani khadeeja qanwa tace uwa daya uba daya dama a cikin mu mu 6 ne maza 4 mata 2 a gurin maHaifi yarmu mu 3 ne bello Sai ni Aliyu Sai Khadija

Itama inna yayan ta

3 Maza 2mace 1Ahmadu takwaran Ahmad kenan Sai hamisu Sai Aysha

Khadija qanwata ita aka fara aurawa abokina Dr Umar Ardo bayan sunyi Aure Allah ya azur tasu da namiji shine Adam Sai hydar kamar yadda kuka Sani ana tare kuka girma da Adam

Daga kan hydar bata Kuma aihuwa ba kamar yadda kuka Sani khadeeja Na matuqar qaunar Yusuf a ranta shiyasa tayi alqawari duk ran da ta haifi ya mace to matar Yusuf CE ta bashi duniya da lahira

Ku

Kuma bayan kunngama primary school dinki Sai aka sama muku makaran ta a bauchi

Inda kukaje kun Sani sai hutu ke dawo daku hutun ma Sai shekara shekara

Kuna js 1 khadeeja ta samu Cikin Aysha

Cikin ikon rabbi ta goya cikinta lfy ta aihu lfy

Tana aihuwa ta kira mahaifinmu tace ta aihu Kuma ta samu ya mace tace Kuma yarinyar yar nan matar Yusuf CE Na bashi duniya da lahira

Bayan awa daya da ahuwar jini ya yanke mata a take kafin minti 30 tace ga garinku

A haka mukayi kuka muka haqura bayan wata biyu aka aurawa Dr Umar Ardo goggonku Aysha tana zuwa da shekara data ta haifi Maryam

Inda itama Kuma tace ta bawa Ahmad ita amatsa yin mata

Dama a lkcin Kuma da aka haifi Aysha Nenne Ku ta aihu yaro ba rai tsaka ninsu sati 3

Shiyasa Sai ta karbi Aysha ta shayar da ita kaji dalilin da Aure ya haramta tsaka Ninka da Aysha kunsha nono daya mahaifiyar kace ta Sha yar da ita har tsawon shekara daya da woya

6 kafin ta yayeta

Batun daura Auren Aysha da Yusuf Kuma a lkcin kuna India a inda kuke hada digri dinki Na forko

A lkcin Aysha Nada shekara 13

Bappa Yaya yayi woni irin ciwon da ya firgita mu

Gaba data muka karaya to a nanne yake cemana batun daurin Auren Aysha da Yusuf a lkcin yasa aka daura Auren a tunanin Sa kar ya mutum bai hada Auren ba mu zo muqi cikawa khadeeja wasiyar da ta bashi

Tarin da ya sarqafe Ahmad ne ya tsaida Abba daga lbrin da yake basu

Da sauri Yusuf ya talla boshi Cikin azaba ga aman jini da yaketa kwarawa

Murya Na rawa yace

Yusuf kaji ko kaji abin da nake gaya maka Na tabbata

Su Abba bazasu hada haram taccen aureba

Cikin sanyi da daukewar numfashi ga wani zufa da yake ta keti mai

Yadamqo hannu Aysha ya kamo Na Yusuf ya hada su wuri daya ya tura hannu Aysha Cikin Na Yusuf din da qer Cikin wahala da fixgar numfashi yace... ..

Gaisuwata gareki

Hajiya Ramatu Allah ya jiqan mahaifinku da rahamaπŸ‘πŸ»

By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] β€ͺ+234 909 785 3276‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

NAYI NADAMA

πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»

MI,WASMITI page 6⃣6⃣to7⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

Cikin carkewar murya yace

Biyaye

Ga amanar da zan bar maka.

Sai kuma tari ya Dan carkeshi

Hannushi Yusuf ya riqe da qarfi ya kai kan qirjinshi ..

Tarin yayi sosai kafin ya da lfa gaba daya jikin shi ya sake idansa duk sun fiffito kan goshinshi Sai zufa ke tsatsafo a take fuskarsa ta dauki sheqi da qelli

A wahalce yaci

Gba da cewa

Ban saniba Yusuf ko zaka iya karbar amanata ?ban saniba ko zaka iya riqemin amanar tawa ?

Ban saniba ko zaka iya Sa farin ciki a rayuwar Aysha ?

Yusuf kam tamkar icce ya zama a wurin ya kasa koda qifta idan shi Sai zuciyarshi dake bugawa

Da qollah😭 da ke bin fuskarsa

A hankali ya daqo hannushi ya shere hawayen dake bin fuskar Yusuf din ya kamo hannu Aysha ya jawota

kanta ya daura dai2 kan qahon zuciyarshi

Cikin rawan murya yace

Aysha kiji bugun zuciyata da zanyi Na qarshe a duniya

Ki ji lkcin da sonki a matsayin matar Aure zai bar jikina kiji lkcin da numfashi zai rabu da gangar jikina

A yau zaki gsknta cewar kece bugun zuciyata

Kanta ta daura kan qirjinshi ta Saki kuka mai ban tausayi

Tana ya Ahmad bazaka mutuba numfashi ka bazai bar gaggar jikin ka ba

Toh ya zanyi dole zan tafi Na barku

Hannushi ya daqo ya kalli inda Maryam ke

Durkushe Sai

Kuka take jikinta duk bari yakeyi

Cikin qarfin hali da kawaici da haquri da jarumta irin Na Ahmad

Ya miqa mata hannu Cikin sautin qarfamata zuciya yace

Maryama zo Maryama zo Maryama zo masoyi yata

cikin kuka ta tsura mai ido tana kallon yadda yake fizgo numfashi Amman wai a hakan yake qoqarin sata farinciki

Hannu ta Sa ta kamo nasa

Cikin sakin wani irin numfashi ya jawota ya daura kanta kan daya gefen qirjinshi

A hankali yace

Maryama tawa kin zamani Na zamake

Komai zanyi in babuke bazan ji dadiba

Maryama kontar da kanki a jikina inji dumin jikinki Na qarshe Maryama matso gareni ki ga fitar raina a take Sai ga wani irin tari mai qarfin ya turkeshi numfashin ya fara fizqa in ya shaqa baya fitarwa da qarfin yasa hannu daya ya qara damqe hannu Yusuf da Aysha da ya hada wuri daya

Ya Sa daya hannu Kuma ya damqi hannu Adam Wanda tuni yake kuka kamar mace

Kuka 😭😭😭😭😱sosai Maryam da Aysha keyi Nenne ko miqewa tayi Cikin dimuwa kamar wacce hankali ya bar jikinta zata fita

Da qarfin Cikin tarin yace Nenne kiyi haquri zaki rabu dani Nenne ki kalli Rabi,u a madadina

Baba bello ne ya matsoshi Cikin qarfin hali da jarumta irin ta maza Sai kai yake juyawa yana cije lebe

Yace Ahmad Na yafema duniya da lahira ubangiji ya maka raya Allah ya sadaka da Mala ikun rahama

Ahmadu Cikin cijewar voice ya rinqa maimaita mai LA ila haillah muhammadura sulillah s a w

Cikin sanyi ya karbi Kalmar shahadar da maifinshi ke mai

Abba da yake ruqqume dashi kanshi a kan cinyarsa

Da qarfin ya ruqqumeshi gami da rumtse idanshi

Yana fadin innalillahi wa ibailaihi raji um

A hankali Yusuf yaji hannun Ahmad ya saki nashi

Cikin zaro ido ya kalli fuskar

Ido Cikin ido

Sukayi

Murmushi Ahmad din yayi Cikin sanyi yace

Biyaye ga amanar Aysha

Sai kuma ya daura da Kalmar Shahada

Idanshi suka koma suka kafe murmushin da yayi yana kan fuskarsa

Dr Umar ardo ne ya rinqa mai mata kullu nafsin za ikatul maut

Nenne dake gefe cikin gigita tace shike nan Ahmad kaima kabi yan uwanka Ahmad Na rabu da kai Sai kuma ta saki wani irin kuka mai ban tausayi

Gaba daya dakin ya rude

Hatta Abba kuka yake sosai ringume da gawar Ahmad din

Adam kam

Tuni ya fada kan Yusuf Cikin riqe hannushi

Yana

Shike nan Yusuf Ahmad ya tafi ya barmu Yusuf mun rasa Ahmad

Sh kenan yanxu dagani Sai kai Yusuf Ahmad ya tafi ya barmu

Maryam kam da Aysha qaqqame qawar sukayi Cikin firgici da rudani

Suke kuka kamar ransu zai fita

Baba bello ne da Dr Umar ardo sune suka samu Dan qarfin jikin miqewa baba bello kam Nenne ya kamo ya ruggume Cikin rawar murya yace haba ruqayyatu kar kibi Ahmad da kuka mana shin baki ga Rahamar da Allah ya mishi ba cikawafa yayi da kalmar shahada

Allah sarki Nenne Sai fafawa tayi jikin mijinta ta rinqa kuka mai ban tausayi

Cikin kuka Abubakar ya riqo hannu marya da Aysha da nufin ya jasu su fita

Da qarfin Maryam ta fada qirjin shi Cikin n kuka tace ya Abubakar da gaske ya Ahmad ya rasu Na rasa ya Ahmad

Kai ya rinqa juya mata yana zubda qollah😭ya jata suka fita

Ummi CE ta matso Cikin kuka tasa hannu ta rufe mai idanshi

Su Usman da Rabi,u kam da abdul dama tuni suka koma parlon kuka suke kamar yara

Ummi CE ta miqe gami da kamo hannu Aysha da nufi su fita

Tana janta Sai gani tayi tayi yuu

Sai fadawa kan Yusuf tayi a sume

cikin firgita Ummi ta rinqa kiranta tana jijjiga ta Amman ina

Goggo Aysha CE tayi tunanin debo ruwan ana Dan shafa mata a fuska Amman INA ko matsi bata yiba

😱😫dimuwa. Da firgici da tsoro mai matuqar tsananin su suka sauqa kan rayuwar Yusuf inda ya zama tamkar mai Ciwon mantuwa

Lallai kuka ma Rahama ne

Shi kam Yusuf yau yake buqatar kuka a rayuwarsa Kuma a yau kuka ya mai tsada

Zuciyarshi ta kasa tuno komai qoqol warsa Kuma gaba daya ta tsaya bata aiki kanshi da jikin shi duk jinsu a juye sukeπŸ™ƒ

Ido kawai Yusuf ke binsu dashi Sai hannushi da yasa ya damqi hannu Ahmad din

Su Ummi yake klo Cikin zare idon fuskar Aysha yabi da idonshi Cikin yanayin rashin sanin abin da akeyi

Hydar ne ya zo ya ciccibi Aysha yayi dakin Ummi da ita kamar gawa

Yusuf kam yana zaune a gun riqe da hannun gawar

Dr Umar ya ja Abba ska fita tare

Fuskar Ahmad din ya zubawa ido Sai ya juya ya kalli Adam dake durqushe a gefen shi yana ta kuka

A haka har zuwa tsawon wani lkci

Allahu Akbar

Lbrin rasuwar Ahmad

Ta kasance tam kar sauqan aradune a zuqatan yan uwa da abokan arziqi

Lbrin ya zama tamkar sauqan qanqarane ne a jikin mutane

Kafin wani lkci gida ya cika tab da yan uwa da maqota da abokansu

Baba Ahmadu ne da Dr Umar

Suka shigo

Daukar gawar Dan

Aje ayiwa gawar wonka ayi mata sutura a kaita makoncin ta

Cikin tsoro baba Ahmadu ya daqo yana kallon yadda dr Umar ke ta yin qoqarin cire hannu Ahmad Cikin Na Yusuf Amman .......

Allah sarki rayuwa Dan Adam Dan mutuwa nima kaina Aysha Ali Garkuwa rasuwar Ahmad ta zame min fami a zuciya ta ta famimin rasuwar yan uwana shiyasa wlh bazan iya ci gaba da typing ba har Sai zuwa gobe 😭😭😭

By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] β€ͺ+234 909 785 3276‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

NAYI NADAMA

πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»

MI,WASMITI page 7⃣1⃣to7⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

Amman gsky Baku kyautamin ba masu karatu ya kamata ace tsakaninmu Marubuta da ma karanta a ringa yiwa juna uzuri

Daga jin Ahmad ya rasu Sai wasu suka rinqa qananan maganganu wasu harda kirana a woya Wai meyasa zan kashe Ahmad ai wanna NAYI rashin imani Haba masu karatu kukam kuyi Haquri maNa Ku Biyoni A hankali ai zakuga yadda zan tsara mana abin masu bina ta prvt chart kowa da irin qorafin da yake min

Dan Allah mu rinqa yiwa juna uzuri

Wasu harda cewa ai gwara akashe Yusuf😫

Ina Baku haquri wasu nace Na sasu kuka sosai karku damu zakuyi dry a gaba fiye da yadda kukayi dry a baya zaku Sha nishadi fiye da zatonku

Ku dai Ku hira Yusuf ya shigo hannuπŸ˜πŸ˜˜πŸŒπŸ™ˆπŸ˜

Jan hannu Yusuf din yakeyi yana qoqarin rabewa a na Ahmad din shiku ma Yusuf Sai damage hannu da yayi yana mai zuba musu ido

Kamar zaucecce a hankali Dr Umar ya zauna kusa dashi Cikin tausasa zuciyarshi yace

Yusuf saki hannu Ahmad

Kaji sakeshi a yanxu ba wani gata ko

Alfarma da zamuyi mishi sama da mu kaishi Cikin qabarinshi

Baiyi mgn ba bai Kuma sakiba Sai zuciyarsa da ta rinqa bugawa da qarfin qarfi

Hannu nashi ya jawo ya dawowa kan qawar yasa yatsunshi ya rinqa bude tafin hannu da Yusuf do ya damqe

Shi kam Yusuf kallon shi kawai yakeyi

So ya yake yaji shi shima a mace ko zaiji wani a bu a ranshi ji yake dama haukacewa yayi

A hankali zuciyarsa ta fara tuno mai abinda kalaman baba Umar ke nufi a take Kuma Sai jikin shi ya rinqa karkarwa

A haka suka samu suka dauke gawar

Cikin kuka Adam yabi bayansu

Shi kam Yusuf a wurin ya zauna kamar dasashi akayi

Acan Kuma akayiwa gawar duk abin da ya kamata kafin ma gari ya waye anyi komai an gama

Washe gari da safe wannan lbrin ya iski Anuty Sadiya

Duk da mijinta ta ya ji dashi akayi komai Amman ya rasa ta INA zai fara kawo mata wannan zance

Sai da safen yace ta shirya suje gida

Su gaidasu

A mota ta kalli mijinta Cikin sanyi tace Abban Yumin.

Na,am ya amsa mata Cikin sanyi

Sai kuma tayi shiru gamida dafe qirjinta

Hannushi yasa ya kamo nata yace

Kin kirani kin Kuma yi shiru

Kai ta daqo ta kalleshi Cikin rawar murya da alamar kuka zatayi

Tace Abban Yumin

Zuciyata Na tsinkewa tsoro nakeji ban San meyasa ba tun jiya nakejin faduwar gaba

A hankali ya jawota ya manna ta a jikin shi cikin fargaba yace ki rinqa addu,a ki Kuma kasance mai yarda da gaddara

Dai dai nan yayi parking a farfajiyar gidan nasu

A hankali ta zame jikinta ta fito

Cikin tsoro da firgita ta bude idanta da kyau ganin gaba daya harabar gidan a cike yake da mutane a take qafarta ta fara rawa Cikin tsoro ta juyo gareshi tana Abban Yumin me ya faru me kake boye min

Hannushi ta riqe tana jijji gawa da qarfi tana ka fada min INA Abba ban ganshi anan ba

Allah sarki

ita Sam bata kai tunanin ta kan qaninta ta rasa ba

Rabi,u dake gefe ne yayi saurin isowa gareta durqushe wa yayi a gaban ta Cikin kuka yace Anuty Sadiya ya Ahmad ya tafi ya Ahmad ya tafi ya barmu

Ido ta zaro Cikin tsoro Sai kuma tayi Cikin gida kai tsaye dakin Nenne ta nufa

Can ta hango Ummi da sauri taje gaban ta ta fada Cikin kuka tace Ummi

Me nakeji Ummi meya samu Dan uwana wayyo Allah wayyo Dan uwana wayyo Nenne Na wayyo cikina Ummi shike nan Na rasa Dan uwa

Adam ne ya kamo hannuta Cikin kuka yace Anuty Sadiya mun rasa Ahmad Anuty Sadiya Ahmad ya tafi ya barmu

Gaba daya suka ruda parlon kakace ta tashi itama Cikin kuka ta kamo hannu Sadiya

Da Adam tayi Cikin daki dasu



Suna shiga Sadiya ta hango Yusuf Wanda tun jiyan bai tashi a wurin ba sai sallan asuba da ya tashi yayi da taimakon hydar

Tana hoggo shi ga Nenne a gefenshi

Tana riqe da hannushi tana fadin

Haba Yusuf kayi mgn mana Yusuf katashi kaje qun baqin da sukazo yi maka gaisuwa

Haba Yusuf fushi kakeyi da yin ubangiji ne

Shin ase bazaka rungumi qaddara ba

Yusufa mufa musul Maine

Shi kam Yusuf ido ya zubawa Anuty Sadiya

Ita Kuma gabanshi tazo ta durqusa ta kamo hannushi ta kifa kanta kan cinyarsa ta saki wani kuka mai ban

14 / 38