Mis Wasmiti 1 Complete Hausa Novel

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Romance

Chapter   15 / 38

42K to 45K   out of 112.1K words

tausayi

Tana kuka tana fadin Yusuf ya zamuyi Allah shi yabamu Ahmad Kuma shi ya dauke shi

Dama kullum haka Ahmad ke gayamin ai Wanda ya Baku ni yaga fiku sona Anuty Sadiya ki dena damuwa da halin da nake ciki ase Ahmad duk maganganu da yakejin wasiyace

A hankali ya daura nashi kan kan kafadarta

Yasa hannushi ya riqe nata Sai ya kuma kura mata ido

Yana jujjuya kai

A hankali tace Yusuf kayi min mgn ma ko zanji sanyi a raina dama kullum Ahmad cemin yake ko ya mutum kar Na damu gaka ga Adam da Abubakar duk abin da nake so zaku min

Kai ta juya cikin kuka tace Ummi INA Abba Ummi a wane hali Abba yake ?

Cikin duseshewar murya tace Sadiya

Abba tun a Daren jiya ya tafi Abuja shida Hydar Kuma yau dinnan zasu wuce India

A Dan tsorace tace Ummi Abba ne ba lfy ko ehh Sadiya abbanku baya Cikin hayya cin sa

Hawan jinisa ne ya tashi

Sai hawayen ke bin fuskar ta

Adam ne ya kalleta Cikin sanyi yace anty sadiya ko zakizo kije dakin Ummi ki zauna da su Maryam da Aysha da Amira suna can Sai kuka sukayi ba mai lallashin wani

Cikin sanyin jiki ta nufi dakin Ummin

Ayyah Maryam da aysha suna zaune tun jiya da Aysha ta farfado suke ta kuka abin tausayi Aysha abin ya hadu mata jiya tasan ba ummi

bace mahaifiyar ta kuma a jiya ta rasa ya Ahmad dinta Kuma a jiya tasan mahaifiyata ta rasu a lkcin aihuwarta

Ganin Sadiya yasa ta fada jikinta tai ta wani sabon kuka

Ta ruggumi meta nan sukayi ta kukansu

Da dyar dai suka samu suka tsagaita

Da kukan

Rayuwar gidan ya canja musu gidan ya koma tamkar ba kowa Sai masu zuwa gaisu da zaran bakin suntafi kuma to shike nan gidan yayi shiru

Rayuwar Yusuf ta sauya ta koma abin tausayi baya mgn da kowa komai za acemai da kai ko ido yake bada amasa duk masifar Na ta Yusuf da bala,I da mishkilanci yanxu babu su

Ya koma abin tausayi Baya iya mgn 5 lafiyeyyu

Komai ya rigada ya gama sauyawa

Aysha kam ko yaushe Sai ta shiga toilet tayi ta kukanta Sai fuska ta kumbura Maryam Kuma yanxu bata iya kukan ya rigada zuciyata ta bushe

Yau ne akayi sadakan 7 gaba daya baqi sun waste su Bappa Yaya ne kadai suka rege basu tafi ba

Yau kwana 10 da rasuwar Kuma yaune su Bappa Yaya ya zasu koma

Shiyasa da safe ya Tara zuriyar tasa

Bayan ya gama musu nasiha

Ya kalli Yusuf da Adam yace

Dudabe

Na,am ya amsa cikin

sanyi

Ido ya zuba mai cikin tausayawa yace

Yanxu me kakeyi a qasarnan ?

Kai ya sunkuyar gami da cije lips enshi yace me zanyi Kuma a qasarnan bani da abin da zanyi

Toh ka shirya kaida matarka Ku koma kaje kaci gaba da kara tunka

Aysha dake takure a jikin Nenne Cikin kuka tace Dan Allah Bappa Yaya Ku barni ni bana son komawa can

To me zaki zauna kiyi a nandin ?

Ni dai banson komawa canne

Ta bashi amsa Cikin kuka

Shi dai Yusuf shiru yayi Dan yanxu qoqolwarsa bata fiye gane me ake yiba

Haka kuwa akayi randa akayi kwana 15 da rasuwar a ranar baba bello ya kamma lawa su Yusuf shirin tafiyar su

A Kuma ranar ✈ jirginsu zai tashi

A hankali suke fitowa daga parlon suna zuwa harabar gidan

Bayan su Rabi,u sun gama Sa musu kayansu a but

Cikin sanyi Yusuf yaje ya durqusa gaban baba bello murya Na rawa yace baba zan tafi

Kanshi ya dafe Cikin qarfafa mai guiwa yace Allah ya kaiku lfy Yusuf

amin yace

Gami da miqewa yaje gaban Nenne itama ta mai addu,a

A hankali ya qarisa gaban umminshi

Ya durqusa guiwa bibbiyu yace Ummi zan tafi Amman bazan sake zuwa qasarnan da wuriba

Cikin

ajiyar hrt

Ta kamo shi ta tsaida shi

A hankali taja hannu Aysha ta samai Cikin nasa tace to ga amanar da Dan uwanka ya baka

Yana Cikin qabarinshi

mu kuwa mune masu ganin irin yadda zaka riqe amanar da ya baka a dai dai lkcin da ransa yake fita a jikin shi

Hannu yasa ya kamo Na Ayshan ya juya Cikin Rashin sanin me zaiyi

Ya jata

Suka qarisa gaban Adam ya ruggume juna sukayi musabaha

Ya kalleshi Cikin sanyi yace biyaye Allah ta sadamu kan alkhairi

Amin yace dai 2 lkcin da suka shiga mota

Usmanne da Rabi,u suka kaisu airport

3:37 pm jirginsu ya tashi

By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] β€ͺ+234 909 785 3276‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

NAYI NADAMA

πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»

MI,WASMITI page 7⃣4⃣to7⃣5⃣ Na Aysha s Garkuwa

πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

Allah sarki rayuwa mai juyawa

A

cikin jirgi

Yusuf ya zauna kan kuje rarsa ta number 24 yayinda Aysha Kuma nata number 23 ne

Nata kujerar itace kusa da window jirgin

A hankali Yusuf yake takawa har ya isa wurin zaman nasu

Jiki a sanyaye ya zauna

Gamida yin taqumi da hannushi daya ya Sada kanshi qasa

Bai tuno komai Sai ran da suka dawo India a lokcin da suka kamma la kara tunsu

A wannan jirgin suka dawo a wadannan kujerun suka zauna inda ya ke zaune anan ya zauna a wancan lkcin Na gefenshi Kuma biyayenshi ne

A hankali ya zubawa sit din ido

Zuciyarsa Na suya

Sai cije lebenshi yakeyi sabida kuka yake son yi Amman kuma ya kasa samun kukan

Yana Cikin wannan halin

Yaji abi Na diga kan wuyanshi

Hannushi yasa ya shafo wurin kamar ruwa yaji

Kai ya dago ya zubawa Aysha dake tsaye a gefenshi dafe da kan kuje ranshi

Hawaye wannan Na koran wancan

Kallonta yayi Cikin shawa,a

A ranshi yake cewa

Kinji dadi da kika samu kina kuka kina zubda qollah😭 nasan koba komai zakiji sauqi a ranki

Sanarwan da akeyi Na koma ya koma gun zamansa jirgi zai tashi shine ya dawo dashi daga tunanin da yakeyi

Ido ya sake zuba mata

A hankali ya daqo

Hannushi ya kamo nata

Ya jawota

Gami da Dan Jan qafafunshi

Dan ta samu gun wucewa

Kan sit din gefenshi ya yaja hannuta ya zaunar da ita

Ita kam Aysha ido cike da qollah😭 ta bi fuskar shi da kallo

Lkci guda Kuma ta tuno

Lkcin da zasu tafi wancan karon

Da ta tsaya a kanshi haka tana kuka

Cikin masifa ya rinqa surface mata bala,I harda yarfa mata mari yana mayya kawai kin wani tasa mutane a gaba kina kuka toh kanki zakici ai tunda kikayi kuskuren yadda kika biyoni toh wlh baqin jaki Sai ya fiki jin dadi

Cikin tsawa ya jawota ya tura a wancan lkcin

Tana Cikin tunanin taji jishi

Cikin wani irin voice yace

Kija bel dinnan ki saka

Kai ta sunkuyar Cikin zubar qollah😭

A hankali

Jirgin ya rinqa

Qugi da Dan diri

Cikin tafiya a hankali ya rinqa Dan tashi sama

A hankali Yusuf ya maida kanshi jikin sit din ya lumshe idansa jikin jin wani irin azaba a karo Na forko da yaji yana qaunar barin qasarsa ta aihuwa

A karo Na forko da yaji ya qagu ya daina shaqar iskar qasar

A ranshi yakeji to me y rege masa a qasar nan

Babu ya fada a bayyane

Gami da bude idanshi da jin zafi a ransa

Ita kam Aysha ta window take yiwa qasar ta wani irin kallo da jirgin ya gama tashi sama

Ta kifa kanta jikin window ta saki kuka mai ban tausayi

Ido ya zuba mata gami da jinjina kai

A ranshi Kuma cewa yayi kuka ma Rahama ne bazan hanaki ba

A haka Cikin kukan bacci ya debeta

Yayinda shi Kuma Sai ajiyar hrt da yake tayi

9:00 Am agogon Nigeria

Dai2 da 11:00Am saudiya

Jirginsu ✈yayi landing Cikin birnin Madina

A hankali fasinjoji suka rinqa fita

Ido Yusuf ya rufe a sannu Kuma ya budesu

Kan fuskar amanar Ahmad dinshi

Cikin sanyin murya yace

Ke

Ke tashi mun iso

Kamar a mafarki taji muryar shi

Sai kuma taji tsoro Dan tuna wancan Zuwan nasu inda ya rinqa zuba mata mari Cikin fushi yace ko ki taso ko Na tafi Na barki

Bira alaqaqai kawai

Banza mayya..a wancan lkcin



A hankali ya katse mata tunani da takeyi

Muryar shi ta kumaji

Cikin Dan kauri yace

Ke INA mgn kinyi shiru

A hankali ta miqe

Tabi bayan shi

Har inda aka ta naji motici Dan ma tafiya wani ma aikaci Na biye dasu riqe da jakarsu

Har zuwa gun motar

Suka shiga suka tafi

A dai dai harabar wani qaton gida mai kama da ma aikata part part sun kusa 7

Abakin qofar su direban ya tsaya dai2 bakin qofar shiga

Suna fita

Yaja motarsa ya tafi

Jakar ta ya zubawa ido Cikin ranshi yasan bazata iya dagawa ba Amman kuma shima ga nashi

Sai kuma ya kalli inda take ta tsaya Sai rawan sanyi take Dan daga dukkan alamu anyi ruwan samane ya dauke Sai walqiya akeyi da iska mai sanyi da take kadawa

Hannu yasa ya dauki jakar tata yasa qafa ya tura mata nasa

Ya juya yayi gaba a hankali tabi bayan shi

A parlo ya ajiye mata nata ya karbi tasa ya juya yabi Cikin Dan koridon da zai Sa dashi da parlon shi

Yana shiga ya fada kan 3 str Cikin

Yanayin shi da yafi kama da maraya

Ido ya lumshe ba tare da yayi bacci ba zafi yakeji sasoi a rayuwarsa

A hankali ya daqo phone dinshi Nenne ya kira

Tana dagawa tace Yusuf kun isako ? ehh yace mata

Gamida cewa ki gaida baba Sai da safe

Toh Allah ya bamu alkhairi tace dashi gamida katse woyar

Shi kuwa a nashi gefen kashe phone din nashi yayi gaba daya

Ita kuwa Aysha da qyer taja jikinta ta tafi bedroom dinta

Kan gado ta fada Cikin kuka a haka a ranan ta kwana kuka

Shi kuwa Yusuf kukan ya nema ya rasa shiya sa ya tashi Cikin rawan jiki yaje yayi alwala yazo ya rinqa nafilfili

Idan yayi sujjada ba abin da yakeyi Sai nemawa Dan uwan shi gafara

Washe gari da safe

Abokan Yusuf laraba suka rinqa zuwa mai taziya da dama daga cikinsa sun San Ahmad

Wasu sunsu Kuma insun zo kuka sukayi kamar zasu suma

Akwai wasu abo kansu su 2 Sulaiman da Bashir Wanda tare sukayi karatu a inda

Kuma suma yanxu suna Jami,atul madinan ne suna kara ilimi

Bashir Dan Katsina ne Kuma tare da matarsa sukazo

Mai suna Zakiya

Tunda sukazo

Sulaiman yake kuka kamar mace dan shi ya shaqu da Ahmad sosai kusan halin su iri daya

Bashirne ya rinqa Dan bashi baki yayinda dashi ma yake ta sharar qollah😭

Shi kam Yusuf Sai cije lebe da yakeyi

Cikin daburcewar murya yace Zakiya ki isa gun qaunar Ahmad tana ciki

Ku gaisa

Toh tace mai gami da miqewa

Tayi candin

A hankali tayi SLM Cikin parlon ba kowa

Ido ta Dan bude Cikin zubar hawaye tana kallon parlon a shirya yake tsafta ba datti ko kadan komai Na parlon farine da jaa gashi labulayen suna sasake shiyasa Sai parlon yayi dubu kamar dare

SLM ta kumayi gamida zuwa jikin gini ta kunna wutan tsakiyar parlon

Ba kowa har ta juya zata fita Sai kuma taji sautin kukan a cin bedroom din

Juyawa tayi ta shiga dakin

Kan gado ta hangota tayi rufa da ciki Sai kuka takeyi tana

Ayyah ya Ahmad yanxu mun rabu kenan bazan Kuma ganin ka ba

Zuwa tayi ta zauna gefen ta Cikin sanyin murya

Da qoqarin danne nata kukan tace

Kiyi haquri Aysha ki daina bin Dan uwanka da kuka kiyi ta masa addu ,a shi yafi buqata a gareku ba hawayen ki ba

Dagowa tayi tana kallonta Cikin rashin Sani

Fahimtar hakan da Zakiya tayi shiyasa ta kamo hannuta

Tace

Ni suna Zakiya ni matar abokin Yusuf ne sunan mijinta Bashir

Muma muna qasar nan Kuma tare muke da mijina yana can gun Yusuf dinne .

Allah sarki Aysha rashin Dan uwa shiyasa a take taji zaki tamkar Maryam da Amira

Cikin hawayen tace kinsan ya Ahmad dinako ?

Eh Na sanshi Aysha

!

Ayyah to shinefa ya rasu.

ehh Na Sani Aysha

Kibar kukan Dan Allah

Wlh nima zaki Sani kuka

Kai ta jinji na gami da share hawayen ta tace

Ni ma banson yi mishi kukan kasawa nake in banyi kukan ba ji nake kamar zan mutu

Cikin tausa yawa tace ki rinqa addu,a kinji ko Aysha

Toh tace Cikin goge qollah😭

Haka dai Zakiya tayi ta lallashinta

Har ta samu ta jawota suka shiga kitchen

Suka danti girki mai Dan sauki

Dan dama ba abin da babu a cikin kitchen din

Ita ta dauka ta kaiwa su Yusuf

T juya zata tafi Bashir yace in kin gama kizo mu tafi

Toh tace Cikin sanyi Dan tanajin tausayin yadda Yusuf da Aysha zasu kasance su kadai

A

Parlon ta zuba abinci ta matso ayshi cin lallashi tace

Ayyah Aysha ki matso kici abinci kinji ko

Kai ta girgiza tace bazan iyaba bakina daci nakeji

Ta Dan sunkuyar d kai tace Aysha bakya son nazo gobe ko ?

Da sauri tace a a wlh inaso

To kici abinci

Ayyah Zakiya nima ina son ci bazan iya bane shi yasa

Miqewa tayi gamida yin Cikin kitchen din furts ta dauko ta kawo mata

tace gashi ki daure kici koda inabinnan da Dan dabino ga Apple

Karba tayi ta danci

Sannan sukayi sallan insha

A parlon Yusuf Kuma shi da sulamai sun kasa cinnkomai shima Bashir sai dan tea ya Dan Sha

Bashir dinne ya miqe gami da kallon Yusuf

Cikin sanyi yace

Yusuf zamu tafi Sai gobe in Allah ya kaimu insha Allah zamuzo

Amman dan Allah Yusuf ka rinqa Sa dauriya a ranka Yusuf ka rege tunani Dan Allah kar ya maka illa

Kasan kana da matsalan zuciya

Kai ya sunkuyar Cikin ceje lips dinshi da gaba daya yanxu sun kubbura sunyi jazur sabida rashin kukan da bai samu yayinba

Sai yayi ta cizon lips din nashi

Haka dai Bashir ya rinqa bashi baki

Sannan suka wuce parlon Aysha

Sulaiman kam yana ganin ta Sai hawaye Dan shi yasan irin son da Ahmad yake mata

Kuma itama tasan Sulaimanu

Durqusawa tayi a gabanshi tana zubda qollah😭 Cikin rawan murya yace

Sannu Aysha sannu da rashi Allah ya jiqanshi da Rahama

Amin ya rabbi ta fada Cikin kuka shima Bashir ya gaida ta sannan suka fita suka tafi

Shi kam Yusuf parlon shi ya koma Cikin kuncin zuciya

Yadda ya kwana jiya hakama ya kwana yau

Washe gari da safe Bashir da Sulaiman sukazo Zakiya kuwa sai da ta tsaya tayi musu girki sannan ta taho

Daga ranan haka sukayi tayi Sai randa suka cika kwana 7 da dawowa sannan suka daina zuwa

Su wuni Sai dai duk da haka kullum zakiya ke musu girki ta bawa Bashir ya kawo musu duk da baci sukayi ba yadda Bashir ke kawo shi haka yake zuwa ya

dau keshi

Sannu a hankali yau watansu daya da dawowa

Rayuwa ta juya ta canxa

Yusuf Dan qolisan nan gaba daya ya zama abin tausayi banda wonka ba abinda yakeyi ko mai bai shafawa

A hankali Dan sirinrin sajenshi Na ya rinqa qaruwa yana yawa yana bajewa ga wani irin rama da yayi duk ya canxa sai dai kyau kam kamar qara mai akeyi

kullum da safe yana dawowa masallaci Sai ya leqa gun Aysha a cewarsa amanarsa CE ita

Duk da ita kam bata ganin shi

Wata ranar jummah da daddare misalin qarfe 2

Na dare Aysha dake parlo Wanda a yanxu parlon ya zama dakin kwananta Dan

Da zaran tayi bacci a bedroom sai mafarkin ya Ahmad dinta ke bibiyarta

Shiyasa ta dawo parlon

Inda zata kwana kuka yayinda zata kwana jin sautin karatun Yusuf Kuma a parlon shi

Sai dai abin tsoro da firgici jin a yau ba sautin karatun Yusuf din take jiba Cikin firgita ta tashi da sauri ta nufi parlon bashi..... Tsoron ta ya qaru ganin abinda Yusuf din keyi

ta kidime ta rude ta kidime da sauri tayi kanshi..........

I love you all my frns😘😍😘

Allah ya barmu tare

By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] β€ͺ+234 909 785 3276‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

NAYI NADAMA

πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»

MI,WASMITI page 7⃣6⃣to7⃣7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

Kina raina Asma,u Adam admin din zauren guzurin gobe alqiyama😘😍

I love you all my frns😘😍

Kuka yakeyi cikin fitar hankali kuka mai ban tausayi gaba daya ya fita hayyacinsa

Jikinsa kab zuface ke tsatsafo mai tako ina

Ya zaune kan sallayah runqqume da qur,ani mai girma a jikinsa ga qaton photo su su 4 Shi da Ahmad din da Adam da Abubakar

Hannushi yasa ya dafe kanshi da hannu bibbiyu

Cikin kuka

15 / 38