Idan Kaya Ya Gaji Gammo Ma Ya Gaji Book 3 Complete Hausa Novel

Author :  Maman Fareesa Category :  Love

Chapter   3 / 25

6K to 9K   out of 72.9K words

Baba Malam yayi tare da girgiza kai.
"Toh shikenan zata zauna Win har zuwa dare zuwa lokacin Babangida ya dawo, kuma kun dawo in aka ?ar?are magana sai ku tafi da'ita babu wani dalilin da zaisa ta zauna damu a nan ina mai tabbatar muku wannan yarinyar bata san ?ana ba. Sannan in zaku dawo shi wannan mai kallabin yayi ha?uri kada yazo dashi"
Mi?ewa su Maigogul suka yi Cicib yace.
"Kar ka shiga inda zaka kasa fita Malam"
suka ficewarsu suna sambatu.
Baba Malam ya dubeni ya maya idanuna a tsaitsaye a cikin nashi.
"A ina kuke haWuwa da shi Babangida yarinta ki gayan gaskiya?"
Cikin halin ko in kula nace.
Ranar farko dai a Club muka haWu dashi.
Daga lokacin mukan haWu a Hotel, ko a shagon abokinshi dai"
Idanu Malam Baba ya lumshe yace.
"Menene Club Win da kuka soma haWuwa shima Hotel Win fa? "
Ina taunar cingam nace.
Gidan rawar dare wanda ake cakuWuwa maza da mata ayi rawa ayi shaye_shaye dai haka. Shi kuma hotel zango ba?i"
Kai ya girgiza yana jinjina lamarina. Ni kuma a irin rashin tarbiyyar mu bansan cewar yin wannan bayanin kaWai ba ?aramar fitsara bane.
"Kin tabbatar cikin dake jikinki na Babangida ne?"
Ah sosai ma. Ko shima ya sani. Daga ranar dana sanar dashi ina da cikin. Tun lokacin har zuwa yanzu wayarshi ma a kashe take."
"Babangidan shima yana shaye_shayenne ko ko dai bayayi?"
Yana shan taba. Baya ga wannan baya shan ko wanne nau'in kayan maye ?arya da ciwo"
Kai kawai Malam Baba yaita girgizawa har wani bawan Allah mai kama dashi ya shigo ya gurfana a gabanshi. Rauni linkib ya nuna a idanunshi harda muryarshi, izuwa motsinshi.
"Manga yarinyarnan ka tafi da'ita gidanka ta zauna. Zan nemi ka kawo mun ita zuwa bayan isha. Sabuwa ko? Tashi ki bishi. A bata hijabi ta saka in zata dawo"
"Amman Yaya meke faruwa ban taSa ganinka a cikin irin wannan yanayin ba. Meke faruwa dan ALLAH ka barni a duhu. Ita wannan musulunta tazo yi ne?"
Hannu Malam Baba ya Waga ma Manga cikin dakiya da dauriyar da ya aro ya yafa yace.
"Babu wata damuwa Khairan in sha ALLAH. Ku je kawai"
Haka Kawu Manga ya tusani a gaba har zuwa gidanshi. Ya dan?ani a hannun uwargidanshi a matsayin wacce tazo zata musulunta.
?aki ta shigar dani, ta kawo mun ruwa da abinci.
"Ga abinci kici baiwar Allah. Allah sarki na taya ki murna sosai gaki kyakkyawar gaske. Allah ya haWaki da miji na gari wanda zai koyar dake addini da kyau"
Uhm bance mata ba. Ina zaune na faWa zurfin tunani.

Baba Malam:.

Da idanu yabi bayan Sabuwa. Sai da yaga fitarsu ya mi?e tsaye tare da sauke numfashi.
Le?awa yayi wajan almajiran ya yafito babban Almajirinshi wanda almajirai ?an uwanshi sukai mishi ?alani da magajin Malam.
Da sauri ya iso hannunshi ri?e da bulala.
"Magajin Malam ka kula da almajiran ni zan shiga gida akwai abinda zanyi"
Cike da girmamawa magajin Malam ya amsa.
Baba malam ya shige cikin gida izuwa turakarshi. Zama yayi a bakin gado yayi shiru yana nazarin maganganun su Maigogul. Tare da tunanin irin tarbiyar da ya bama yaranshi da irin gwadaben da ya Waurasu a kai.
Babangida shine Wa tilo mafi soyuwa a zuchiyar Baba Malam wanda har ya kasa Soye son da yake yi mishi tun yana yaro balle daya girma asalin kamanninsu ta sake bayyana.
Ko Magana Babangidan yake yi yana mamakin tsantsar kamannin muryarsu. Haka inya hango Babangida daga nesa yana tawowa kamar harta Saci.
A ranshi yasan shi ba kuWi ba, ba Wan siyasa ba, babu wani dalili da zaisa su Maigogul su zo da nufin sharri. Wani Sarayi na zuchiyarshi na faWa mishi kuskure suka yi ba gidan suke nufi ba, ba kuma Babangidan gidan ake nufi ba.
Wata zuchiyar tana sanar dashi cewar.
Girman lamarin da suka zo dashi yafi ?arfin ace wai Satan kai suka yi.
Amman tambayar anan meye haWin Babangida da wannan ?ar barikin. Meye haWinshi da Hotel, meye haWinshi da Club, meye hadinshi da karar sigari?
WaWannan tambayoyin su suka hana wannan Dattijo sukuni. Ya shafe tsawon awannin da suka haura uku yana karanta wasi?ar jaki. Har Malama Babba taima kanta masauki a kusa dashi baida wata masaniya har saida ta ambaci sunanshi kana ya Wago idanuwanshi da babu wasa cikinsu ya sauke a kanta.
"Yaya akayi har makaranta ta tashi kenan?"
Ya faWa cikin magidanciyar kamilalliyar muryarshi mara wasa.
"E Malam amman abunda ya bani mamaki shine a karon farko tunda ka kafa wannan tsangayar ban taSa ganinka a zaune a Waki alhalin makaranta nayi ba.
In ba'a ganka a makaranta ba to kana wajen karSan Waurin aure, ko raWin suna, ko jana'iza, ko kuma al?alanci. Amman yau abun mamaki kaine kayi zaune tunaninka ya tafi wani wajen. Na tabbatar hakan baya rasa nasaba da waWannan mutane marasa tarbiyyar islama da suka zo wajenka ko?"
Murmushi yayi kawai tare da cewa.
"Babba kenan. Hakane damuwar dana shiga tana da hala?a da zuwan nasu. Amman wannan damuwar ba komai bace akan damuwar da zamu shiga dukkanmu in abinda suka zo dashi gaskiya ne"
Shiru tayi tana son tambayarshi abinda ke tafe dasu, amman tasan halin mijin nata da ace yaso faWa mata da kai tsaye zai soma maganar. Tasan bai shirya faWa mata ba.
Kawai dai tunda taji harda Babangida a cikin maganar ta kasa samun nutsuwa.
Haka ta tafi ta bama malam Baba waje domin a ?a'idar gidan da rana haka basa shiga turaka sabida kunya da sakayawa kasancewar almajirai ko da yaushe cikin shige da fice suke a gidan, yaransu ma dake gidajen mazajensu kullum suna gida kasancewar sune malaman makarantar Malam Baba dasu akeyin abincin rana tamkar yadda da gidan yake cike da yara.
Da Baba Malam da Malama Babba haka suka wuni a cikin damuwa. Ko da akayi abinci da rana Sa'a ta kai mishi abincin. A tsaye ta sameshi ya kai mari ya kai gwauro
"Sa'a ki mayar da abincin. Ko wacce cikinku da kunci abinci ku koma gidajenku. Sannan ki sanar ma iyayenku mata kada wanda aka bari ya shigo Wakinnan har su kaWaici kawai nake so. Babangida ne kaWai in ya shigo za'a yi mun Magana. Ku hanzarta kuci abinci ku tafi"
MRS BUKHARI

Tabb wannan lamari da girma yake
[8/14, 7:22 AM] +234 802 205 9556: https://chat.whatsapp.com/IUKFTeul76p2VaAvQ5nk0U?mode=ac_t



IDAN KAYA YA GAJI...
GAMMO MA YA GAJI
BADIAT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ?AMSHI
LITTAFI NA UKU
SHAFI NA UKU 3



Cikin dakewa da rashin wasa yayi maganar. Dama wannan Wabi'ace ta Malam ba Mutum bane mai sakewa a cikin gidanshi ba. Hakan yasa ko kara ya gindaya babu Wanda ya isa tsallakewa yaranshi ashirin da uku da Allah ya bashi kowanne cikinsu yana kiyaye Sacin ran Baba Malam Kuma umarni sau Waya rak yake bayarwa babu wanda ya isa tsallake wannan umarnin. Har iyayensu mata babu wanda ya'isa yaji dalili madamar bashi yaso sanar dasu dalilin ba.
Da haka Sa'a ta koma a sanyaye ta mayar ma Malama Babba abincin tare da zayyana mata a yadda ta shiga ta sameshi da kuma sa?on daya bata.
"Kudidi ni kam tafiya gida zanyi tsoro ya kamani sabida bamu san Abinda zai biyo baya ba. Ko meye haWin Babangida da waWannan mutanen sai Allah"
Cewar Sa'a data zura dogon hijabinta tana tsaye tana Waura ni?abi. Malama Babba tace.
"Ni kaina jin sunan Babangida a cikin Maganar yafi komai tayar mun da hankali. Gashi wayarshi sam bata shiga sam ko ina yau ya shige oho. Allah yasa ba wani babban abun bane. To ma me Babangida zai yi?"
Sa'a tace.
"Ai da ganin yanayin Baba Malam lamarin fa da girma. Ke dai kiyi ta adda'a kawai. Yarinyar da ta zaro wu?arnan tana gidan Kawu Manga fa Baba Malam yace a ajjiyeta acan har zuwa Babangida ya dawo. Ni dai zan tafi koma menene gobe da safe in nazo naji. Bana so Baba Malam ya fito ya same ni a gidannan."
Ai duka suka mi?e ko wacce ta kama gabanta.
Bayan Sa'a ta sanar da yaran Wakinsu Alawiyya, suma wasu abinci ma suke ci, amman duk suka suri hijabansu. Suka bar Malama Babba tana tubka da warwara.
Ta jima sosai a zaune har Autanta ya shigo ya zauna bata sani ba.
"Malama Babba lafiya kuwa inata magana amman baki ma jini ba?*
Ajjiyar zuchiya kawai ta sauke ta fuskanci Autanta. Kafin tace wani abun suka jiyo sallamar Malama ?arama a kofar Wakin.
Amsawa tayi tare da bata izinin shigowa.
Labule ta Waga ?afarta Waya a waje Waya a ciki.
"Babba dama batun girkin dare ne tun Wazu Sahura tazo harfa ta gama jajjagen kayan miya amman baki fito ba shine nace bari in zo inga ko lafiya?"
Tsakankanin Malama Babba da malama karama ana gwabza kishi da gasa sosai fiye da tunanin masu karatu.
Sai dai dake ba faWa suke yi a tsakankaninsu ba yasa Baba Malam ya zuba musu idanu kawai amman yana sane da irin zaman da suke yi. Haka in wani abunne na jaje ya samu ?an wasu Wayan Wakin ko?arin Soyema Wayan Wakin akeyi. Abun alkhairi ne dai suke shelar sanarwa a tsakar gida.
Baba Malam ya haWe kan yaranshi ne tun suna ?ananu ta hanyar zaunar dasu duk asubar duniya yayi musu nasiha tare da jaddada musu mahimmancin zumunci da haWin kai. Har yanzu yana irin wannan zaman dasu duk Sallah sakamakon abubbuwa da suka sha kanshi da yawa.
Malama Babba ta taSe bakinta ta mi?e.
"Kin ganni yanzu zan fito sai ga Auta ya shigo shine kuma na zauna. Kice mata ganinan"
Da "Toh" Malama ?arama ta amsa tare da sake labulen ta fita.
"Auta kaga Babangida yau dinnan?"
"E na ganshi Wazu a can majalisarsu da abokanshi su Mustapha. Amman lokacin ma mota suke shiga naganshi da ?ananun kaya..."
Da sauri Malama Babba ta rufe bakin Auta.
"Kul naji wannan maganar a bakin kowa Auta duk wanda ma ya tambayeka yayan naka kace baka ganshi ba fa?at"
Mi?ewa tayi ta fice daga Wakin zuchiyarta cike da tsoro.
A babban kitchen Win tsakar gidan ta tadda Sahura.
"Sahura ga kabewa can ki fereta baki Waya miyar kabewa zamu yi. Akwai tanta?washi a rufe a kwano ki zuba a tukunya. Zanyi Sallah yanzu zan dawo mu kwaSa alkubus"
Tana faWin haka ta fito a kitchen Win ta nufi bakin rijiya ta Wauki buta cike da ruwa tayi Alwala ta koma Wakinta tayi Sallah tare da ro?on Allah yasa Babangida ya dawo kadayayi dare asirinshi na yawo ya tonu tasan in wannan asirin ya tonu kashinta ya bushe ma?iya zasu yi dariya sosai, za'aga Babangida da Baba Malam a rana.
Tana shafawa ta fice suka shiga aikin girki ita da Sahura har zuwa magriba kafin suka kammala yau aikin yayi musu dare kasancewar Malama Babba bata fito da wuri ba.
Gidauniyar abincin Baba Malam ta Wakko ta soma zuba mishi, kafin ta zuba na ?an Wakinta, dana ?an Wakin Malama ?arama, sai na Sahura, da almajiran Baba Malam
Saida ta kammala wannan rabon ta samu tayo wanka tare da alwala ta shigewarta Waki.
Tana idar da Sallah ta nutsu taita adda'a a zaune a inda tayi Sallah tasan Baba Malam inya fita tun yamma sai bayan isha yake shigowa. Ita tsoron haWuwa dashi ma take yi.
A sanyaye ta tashi tayo sallar isha ta Wakko zaninta na super ta saka harda sabon Wankunnen zinaren data siya ta saka tana shafa turarenta na mai da ?ar ba?ar humrarta mai ?amshin asali ta jiyo sallama a ?ofar Wakinta. Izinin shigowa ta bayar.
Sumayya ?alibarta ce ta shigo da goyo a bayanta yarinyar sai kuka take yi.
"Ah Malama Babba kinyi kyau sosai"
Dariyar dole tayi tace.
"Toh mu mata duk tsufanmu sai da gyara musamman in kaine da kwana. Kune yara_ yaran mata baku Wauki gyaran jikinku a bakin komai ba"
Sumayya tayi dariya tare da cewa.
"Gaskiya ne Malama Babba. Amman ai ku na musamman ne dama ku kuke koyar damu dabarun da zamu ri?e miji. Littafin ahalari nazo siya dama na bar yara su kaWai, yanzu sai kiga kafin ka koma sun yi ma ba daidai ba."
Littafin ta Wakko ta mi?a mata, ta bata kuWin suka fito tare. Ita ta nufi waje, ita kuma ta nufi kitchen ta Wauki gidauniyar abincin malam Baba ta nufi Sarayin nashi gabanta na ta faWuwa. Gashi taga Malama ?arama ta kafa ta tsare tana son gani da jin gulma. Wannan a faWar malama Babba ne.
Da sallama Malama Babba ta tura ?ofar ta shiga.
A hankali Baba Malam ya amsa sallamar yana zaune a bakin gado ya cire hularshi.
"Sa'a bata faWa miki sa?ona bane, ko kuwa mantawa kikayi ne?"
Ya jefo mata wannan tambayar tare da ?are mata kallo.
Jikinta a sanyaye ta nemi waje ta zauna.
"Ta faWa mun asalima shi yasa ban shigo na gyara maka Waki ba. Naga baka ci abincin rana ba, ya kamata kaci abincin dare kaima Allah kayi ha?uri"
Hannu ya Waga mata halamun tayi mai shiru.
Kafin ma yayi Magana suka jiyo sallamar Malama ?arama a dokin ?ofar.
Malama Babba bata so ya bata uzinin shigowa ba. Amman dake macece mai kissa da son mulki sai tayi sauri ta koma kan gado kusa da Malam. A haka Malama ?arama ta shigo ta taddasu.
Tsugunnawa tayi a gefen ?afar Malam Baba tare da cewa.
"Ba?ine da kai amman magajin Malam ya shimfiWa musu tabarma a zaure na uku kamar yadda yace. Shine nace bari inzo in sanar maka afito lafiya"
Tana dasa Aya ta fice abunta.
Hular daya cire a kanshi ya saka ya fice yabar Malama Babba a zaune cikin bugun zuchiya.
Yana fitowa tsakar gidan yaci karo da Wawo yana gaisawa da Malama ?arama.
"Kai me kake yi a cikin gida? Maza wuce makaranta ka bar Walibai na jiranka"
Da sauri Wawo ya juyo ya fice harda Wan haWawa da gudu.
A hankali Baba Malam ya shiga ratsa zaurukan gidan nashi, yana jiyo yanda su Maigogul ke Waga muryoyinsu har ya iso cikin zauren da sallama Wauke a bakinshi.
"Sannunku da zuwa. Ina zuwa bari a kawo muku abinci"
"A_a ba abinda ya kawo mu kenan ba. Kawai munzo ne muji ba'asin Magana."
Cewar Maigogul kenan. Kallonshi Baba Malam yayi yace.
"Toh shikenan ina zuwa bari in sa yara su dubo Babangidan"
Yana kaiwa nan ya fice ya kirawo magajin Malam.
"Ka kirawo mun Babangida yana makaranta. In baya makaranta ka duba shagon kwanansu kace yazo" shi kuma Talle kace mishi nace yaje gidan Manga ya kirawo Manga da ba?uwa haka kawai zaka ce mishi. In kuma ka haWu dashi Mangan a makaranta sai ka faWa mishi kuyi maza. Ku same ni a zaure na uku."
Umarnin daya bayar kenan ya dawo ya zauna suna jiran ?an aike."


SABUWA:.
Haka na wuni a Waki cur ga azabar ciwo na cina, ga ba?in cikin Babangida na cina shima.
Azahar nayi wannan matar tazo ta tasheni na Wan samu bacci kenan
"Baiwar Allah muje in koyar dake yadda zaki yi alwala sai ki bini muyi Sallah tare"
Ina mi?ewa na cabke kuguna na dubeta da kyau.
Kin ganni nan? Da musulunci aka haifeni. Ni musulmace gabana da bayana, sabida haka kada ki sake mun kallon arniya"
Ina faWan haka na koma na kwanta.
"Ikon Allah. Toh Allah ya kyauta"
Iyakar abinda tace kenan ta fice. Bata daWe ba ta kawo mun abinci. Shinkafa da miya harda kaza da fanta.
Zagewa nayi na cinye tas na kakkarya ?asusuwa yadda ya dace.
Sai da akayi sallar la'asar yamma sakaliya na haWa azahar da la'asar. Tunda dama tazo ta ajjiyemun hijabi a gefena.
Inata waye_waye da ?ar Shuwa ina sanar mata halin da ake ciki"
"Wai ko in zo ne ?awata?"
"A_a kiyi zamanki ai ni warki ce daidai ?ugun kowa kema kin sani. Ni da Babangida shege ka fasa"
A haka muka gama wayarmu ta karshe. Tafe_tafe nice har wajajen taran dare kafinnan aka aiko wai inzo.
Ajjiyar zuchiya na sauke na fito na tadda wannan mutumin daya kawoni a tsaye.
"A_a ki koma ki saka hijabi. Ba mutunci bane mace ta dinga tawo tsirara ba"
Ai ba da hijabin nazo ba. Babangida kuma ya kamata ku tusa gaba kuna ma wa'azi ba wai ni ba"
Ina gama fitsarata na yi waje ai zan iya gane gidan tunda hanyace fetal babu wani kwana.
Ina jiyo takunshi a bayana har muka isa zaure na uku a inda su Maigogul suke da zama.
Waje na samu na zauna bance komai ba.
Wani almajirine ya ?araso da sallama.
"Malam duk inda ya kamata a samu Babangida ba'a sameshi ba"
Kai Baba Malam ya girgiza tare da cewa.
"Magajin Malam dama Babangidan yana kaiwa haka a waje ne kaine Wakinku yake kusa, ka faWa mun gaskiya"
?asa magajin Malam yayi da kanshi halamun babu amsa. A raina nace . Ashe Babangida ?aramin Wan balaja'u ne ma a gidama ba'asan waye shi ba. Baki na taSe.
Ana kan mayar da zance sai ga Babangida ya shigo saye da dogayen kayan farar shadda harda zanna bukar a kanshi.
Idanu muka haWa dashi ya kalleni cike da maWaukakin mamaki, ni ko gajeren tsaki na saki kawai na juya kaina.
Baba malam yayi tsam yana kallonmu tare da nazari. Shigowar Mazan gidanne wajen yasa Baba Malam yace.
"Kai Babangida nemi waje ka zauna. Wawo kaima haka. Ashiru shiga gida ka kiraqo iyayenka mata su zo su samemu ka biyo su. Ku kuma Ramadan kuna iya shigewa ciki"
Duk wannan jawabin da yayi kanshi na ?asa jikinshi yayi wani irin mugun naushi.
Jiki a mace Babangida ya nemi waje ya zauna a Warare.
Cikin mintunan da basu wuce biyar ba Malama Babba da malama karama da Wan aike suka dawo. Daga gefe can su Malama suka rakuSe a tsugunne.
"To ga mai gayya mai aikin ya iso. SABUWA zan baki dama ki mana bayanin ala?arki da Babangida. Ke muke saurare. Ku kuma ku buWe kunnuwanku ku zama shaidu. Dukkannin abinda Babangida ko Sabuwa zasu faWe ku yi nazari akai"
Cike da rashin sanin girman manya nace.
Saurayinane da muka haWu a gidan rawa dashi. A takaice ina Wauke da cikinshi na wata kusan huWu. Na kirashi na sanar dashi yau kwana biyu kenan wayarshi a kashe. Shine Babanmu ya rakoni muzo gidansu domin asan da zaman cikin, wannan shine dalilin eh zuwan namu"
Ina magana ina ciccije leSe ina karkace bakina, irinna yaran da basa ganin uban kowa da gashi "
Salati kafatanin ?an wajen suka saka banda ni da su Maigogul da suke zaune Cicib na yatsina
"Sannan yaronnan kwararo_ kwararo babu inda baya Waukar ?ata su tafi, hotel _hotel babu wanda baya kaita suje su kwana. Ya Wirka mata cikin kuma ace kada mu kwato mata ?ancinta. Yaro a gidan malamai amman gashi ?wallon shege"
Cewar Maigogul kenan.
Malama Babba dai kuka take yi sautin kukan na fita a hankali. Wawo yace
"Amman Baba

3 / 25