Kanwar Maza 3&4 Complete Hausa Novel

Author :  Ayshacool Category :  Love

Chapter   66 / 67

195K to 198K   out of 199.9K words

ta ce "Wannan ai kamar shaiWanu ko sihiri"

Tun sanin da Ammi ta yi wa Ade, mace ce mai ibada da yawan addu'a, duk da kasancewar ta ba wata mai ilimi mai zurfi ba.

Ta dafa kan rumaisa tana ta yi mata addu'a, a hankali ruma ta ce "papa"

"Na'am mimi"

"Wata mage ce za ta sha maka jini a wuyanka, ta kasa"

"Babu wata magge fa, tsorata ki ka yi, bacci ki ke yi"

"A'a ta yakushe ni a hannuna, idonta haya?i ma yake yi" ta nuna musu hannunta, in da aka karta mata farata.

Ade ta ce "yarinya na jego kun barta tana yawo ko ina, gashi ba ta son Wan kwali, idonta ne ya buWe take gane-gane ai". Aka samu dai ruma ta farfaWo, sai dai ba ta magana sosai.

A yammacin ranar su Ade har gida suka je, suka gaida mama, dan a washegari suke son komawa.

Mai sunan baba ya tabattar musu da yardar Allah, zai kawo musu iman, ta ga dangin ta.

Har gida suka sake bin mai girma wambai, suka sake yi masa godiya, turaki kuma a lokacin yana Germany.

Hajiya Lubabatu wani irin ciwon kai ta din ga fama da shi, mai tsananin gaske, da har ta kai ba ta gane mutane sosai, kuma ba ta son haske sai duhu, tayi ta surutai na fita hayyaci, haka aka kaita asibiti aka ajiye.

Ranar da su Ade suka koma, ranar mai sunan baba ya koma lagos shi ma, sai dai mahmud ya rasa sukuni, amma bai gayawa kowa abun da yake damunsa ba, iman ta yi wa mahmud godiya, daga shi har mijinta, bisa ga namijin ?o?arin da suka yi mata

Still a yammacin ranar, wani tashin hankalin ya sake afkuwa, Allah ya yi wa galadima rasuwa, wato mahaifin jabir, Senator wakili kuma ya hau jirgi domin zuwa Mexico, sun samu plane crash, da shi da wasu manya-manyan ?usoshi a Nijeriya, wanda galibin su tare suke har?allar smoke duk suka mutu.

Duk mutuwa mutuwa ce, takawa yana jimamin rashin Wan uwan mahaifinsa, gefe guda kuma yana farincikin hukuncin lokaci Waya, da Ubangiji Allah ya haWa azzalumai yayi musu.

Ahalin masarautar kuwa suka shiga taradaddi da damuwar gagarumin rashin da aka yi, turaki ne ya yi clearing komai, ya taho da gawar Kano.
Ga matarsa na can kwance a asibiti, Wan sa kuma aka kawo shi cikin sar?a, sai a lokacin mutane hankalin su ya koma kan cewa matar galadima ba su suka yi jinyarsa ba, baro shi suka yi a can, aka din ga Allah wadai da ita.

Kwanaki uku da rasuwar galadima, ba a ga Mummy ba, mutane suna ta tambayar Ammi, wai ba su ga Mummy ba.

Kwana na huWu mahmud ya je ya samu ammi, ya ro?eta dan Allah ta kira takawa da rumaisa da iman, su haWu a sashin Mummy.

Ammi ta ce masa ba damuwa, dan kuwa yanzu ba ta ?aunar duk wani abu da zai sanya mahmud Win damuwa.

Hankalinsu ba ?aramin tashi yayi ba, da suka ga Mummy, gaba Waya jikinta a ?one, sai ihu take tana kiran sunan rumaisa, ruma kawai ta fashe da kuka ta rirri?e takawa saboda tsoron da Mummy ta bata.

Wambai ya kalli Mummy ya ce "Jamila, ya aka yi ki ka ?one haka?".

Cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali, ta din ga faWar miyagun abubuwan da ta aikata ita da Hajiya Lubabatu, babu wanda yafi Waga musu hankali, irin yadda ta kai Adam wurin boka a ka zu?i jininsa, kuma duk shekara irin bala'in da yake shiga saboda asirin da tayi masa.

Kasancewar sa da runaisa ne, ya sau?a?a masa wasu abubuwan, kuma a wannan karon ma, aljanar ce ta zo shan jini da take duk shekara, ta kasa ta sanya ruma na?udar dole ta kashe Wan, still ta cigaba da bin adam ta sha jinin da ta saba, saboda ba zata iya cigaba da aikin da aka bata ba, sai da jininsa, shi ne take ta dambe da rumaisa, ta fito a suffar mage, rumaisa ta jefata a murhu. Shi ne ta shiga jikin Mummy, ta ce sai dai tayi jinyar a jikinta, idan mutuwa ce su mutu tare tun da tsayin shekaru ita take yi wa aiki.
Wannan matar da rumaisa take gani, da haya?in da idonsa ke yi, aljanar take gani. LA ILA HA ILLA ANTA SUBHANAKA INNI KUNTU MINA ZALIMIN, da rumaisa ta ri?a, tun da lokacin da ta san falalarta, take ganin fa'idarta a rayuwar ta.

Wambai ya ce "Anya ba surutan ciwo ne ya sanya take maganganun nan ba".

Mahmud ya girgiza kai ya ce "Ba zafin ciwo bane, muna bibiyar duk wayar da Mummy take yi, kuma tun asali na san wasu abubuwan, ba abun da zan iya yi a kai ne"

Kuka ammi take kamar ta fita a hayyacinta ta ce "Jamila me nayi miki haka a rayuwa ne? Haba Jamila shikenan bawa ba zai Wau ?addara ba, duk saboda marigayi ya fara aure na?"

Mahmud ya zube a gaban Ammi ya ce "Ammi, dan girman Allah ki yafewa Mummy, na sam ta cutar da mu, amma ta ri?e ni kamar ita ta haifeni, dan Allah ki yafe mata"

Ruma ta ce "Wallahi ba zata yafe ba, nima ban yafe ba, dukkanin mu bamu yafe mata ba, dare na din ga bi, ina kai ?arar ku wurin Allah, sunayenku na din ga gaya wa Allah, kuma yayi mana maganinku, yau na cika al?awarin da na Wauka".

Su Fauziyya sai kuka suke yi, wambai ya ce "Jamila baku yi wa kanku adalci ba, ki ka saka na din ga ganin baiken Binta, ina goyon bayanki, kanki ki ka yi wa. Binta ki Wauki yaranki ki tafi da su, Allah ya haWa miki kansu, mun yi magana da mai martaba da ?an majalisar sarki ma, Adam ne zai gaji kujerar galadima.
Binta ki yafe mini abubuwan da suka din ga faruwa, ke kuma wannan yarinya rumaisa Allah ya ?ara haskaka rayuwarki, kin kawo sauye-sauye da tarin alkhairi a wannan gida".

Ammi ta rungume Mahmud tana rarrashinsa, sosai yake kuka yana Ammi ta yafe musu baki Waya.

Su Fauziyya sai kuka suke yi, ru?ayya na gefe ba ta iya magana, dan tun da Mummy ta fara rashin lafiya abun ya shafeta, take abu kamar taSaSSiya.

Kwanaki uku aka yi bikin naWin sarautar takawa zuwa galadima, shi kuma ya yi wa rumaisa sarautar garkuwar galadiman kano.

Kwananta arba'in da haihuwa, ya biya musu umara, shi da ita da ammi da mama, suka tafi domin nuna Godiyar su ga Allah.

Kamar yadda mai sunan baba yayi al?awari, Iman ta je ta ga danginta, mutane masu karamci da tarin dukiya.

Kamar yadda ammi ta yi al?awari, sabir na isa shiga makaranta, ta basu Wan su, lokacin ruma ta kammala secondary school, sai dai da laulayin wani cikin ta shiga makaranta, take karantar criminology. Kamar yadda suka yanke shawarar hakan ita da takawa.

Cike da tausayawa mai sunan baba yake kallon iman, ta shirya ranar graduation Win su, cikin ta kamar yayi magana saboda girma, scaninc ya nuna tagwaye ne a cikinta.

Mai sunan baba in dai yazo baya bari ta yi aikin komai, manyan mutane sun halarci bikin kammala karatun su iman.

Hajiya Lubabatu brain cancer ta samu, kanta ya din ga Wurar ruwa, aka fita da ita ?asashen ?etare, sai dai duk da an saki Jabir, bai iya zuwa yayi jinyarta ba, sai ?an uwanta.

Mahmud ya koma aiki, idan ya zo kuwa, kullum sai ya je duba Mummy, sai dai abun nata babu cigaba, kullum ciwo ?ara jagwalewa yake yi, an kai ta asibiti dressing ake yi, amma ?una sake jagwalgwalewa take yi, tana wani irin wari.

Turaki ya tattara iyalin sa yayi watsi da su, duk wani abu na kyautatawa tsakanin su, ya daina yi musu, Jamil aka din ga i?rarin ya mutu a hannun DSS saboda babu wanda ya san a in da yake.

Mai sunan baba kan Iman ta haihu, ya canza musu gida, gida mai kyau sosai da sosai, daga Lagos yake sayo kaya yana aiko wa da Usman da Aliyu kayan takalma, computer da yadiddika da lesuna da ga Aba yana aiko musu da shi, iman da ruma da nusaiba suka haWa kuWi, suke tura masa suma suna karSar takalma da laces.

Yaya Abubakar da yayi aure, jigawa ya koma, saboda a can yayi karatu ya saba da mutane, kuma cikin ikon Allah ya samu aiki a can.

Alhaji Aminu ya din ga jan mai sunan baba a jiki, yana koya masa yadda ake importing kaya daga ?asashen ?etare, mai sunan baba ya ce a koyawa su Aliyu, sune suka fi ga harkar kasuwanci, kar son rai ya shiga lamarin tun da yana aiki da hukumar hana fasa ?wauri.

Tagwayen mata aka yi wa Iman aka ciro mata, masha Allah kyawawa tamka su suka yi kansu, lokacin mimi ma ta yi nauyi sosai, aka sha shagalin suna, an yi wada?a da shanu da nono a haihuwar nan, mai sunan baba ya sanya sunan Ammi da mama.

Abdallah ma a DSS ya samu aiki, yana abuja tare da Bashir, cikin ikon Allah babu wanda Allah bai Waukaka a ?a?an mama ba, kuma galibi duk a sanadin rumaisa ne.

Kasuwanci ya buWewa su Yaya Aliyu, suka tattaga aure, mama ta ce duk su yi Allah ya taimaka.

Mahmud ma yayi aure, Yasir kuwa sai ?arshen shekara yake samu yazo ya koma, zaman canada ya yi masa daWi yana ta karatunsa, ga wata irin sha?uwa tsakaninsa da ?ar anty laila.
Mijin anty laila yana ta jaddada mata, shifa idan Yasir ya kammala karatun sa, a nan zai samu aiki su cigaba da zamansu, sannan kuma da ya kammala karatun ya bashi anam.

?an mazan mama, gidaje uku suka saya, a jikin nasu, suka faWaWawa mama shi, dan cewa tayi dan Allah yayi musu arziki ba zata bar unguwar nan ba, tana fatan suma su ci albarkacin ruma da ?an uwanta.

Hakan ya sa suka gyara layin, aka yi masa kwalta da kwalbati, aka sassaka sola, wannan ya shiga da abun alkhairinsa wannan ya fita.

Mummy ta koma tamkar mushe da rai, saboda wari, kuma tana ji tana gani, gida ya koma hannun ammi, ta malleke komai da take ta ?o?arin hana faruwar hakan.
Ba tare da ?yashi ba, ammi ta din ga nemawa ru?ayya magani, ta ce in dai tana raye ba zata bari Wan marigayi galadima ya wulakanta ba.

Adam ya sauyawa ruma gida, manyan motocin take ja, da ?ananun shekarunta sai ta birgeka, saboda har a lokacin ba ta haWa shekara ashirin ba, ta saka ya Waukko mata Wan mai unguwa mai hanata shiga lambu sata, yake kai Sabir makaranta ana biyansa kuWi mai yawa.

Adam ya Wauke mata komai, dan haka kuWin kasuwancin ta a sama suke, sai dai tayi ta kyauta kasancewar ta mai kyauta ce.
Ba ?aramin girmama rumaisa suke yi ba, saboda rawar ganin da taka a rayuwar Adam, dan shi kansa duk wani abu da zai taSa mutuncinta, ko tayar mata da hankali fito na fito yake da shi.

?an unguwarsu ruma har murna suke su ga dan?areriyar mota a ?ofar gida, sun san akwai kaSakin alkhairi ranar.

Hajiya Lubabatu ce ta fara mutuwa, ba tayi arba'in ma Mummy ta bita, ammi ta ji mutuwar nan ba kaWan ba, hakan ya sa ta ce duk ta yafe musu, kuma ta rungumi Fauziyya da ru?ayya ta cigaba da ri?o, baba uwani a can garin su mahaifinta aka ganota, Cancer ya kama mata ?afafuwa ita ma, babu kuWin da za ayi mata aiki, ammi ba ta yi shawara da wani ba ma, ta tura sidi aka biya kuWi, aka cire mata ?afafuwan ta saya mata keken guragu tare da bata jarin sana'a.

Rumaisa kafin ta gama makaranta sai da ta haifi ?an maza biyu, ta din ga Addu'a "Allah kar ka sa na yi irin ta mama na haifi ?anwar maza, ba zan iya ba" takawa ya din ga yi mata dariya ya ce ashe kina sane ki ke tsiyata ku.

Idan ta tuna wasu rashin hankalin da tayi a baya, ta ji kamar ta yi wa kanta duka, babban abun da ya bata mamaki, bai wuce duk shekarun nan takawa yana ajiye da wasi?ar da ta rubuta masa, na cewar ya taSa mata nono, yayi ta tsokanarta yana dariya.

Samha kuwa rayuwa ta juya mata baya, dan abun da Jamil ya aikata, da wanda tayi ita ma, ya zame mata ba?in fenti, aka rasa mai aurenta, duk gayu da ?walisar samarin duk suka watse.

Runaisa ba ta bar harkarta ta zane-zane ba, dan har rubuce-rubuce take yi, kamar wasa ta zama popular manyan mutane suke sayen zane-zanenta.

Cikin ikon Allah rumaisa ta zama criminal lawyer, sunanta ya shahara sosai, ga ta lawyer, ?wararriya wurin zane-zane da rubuce-rubuce, kuma ?ar kasuwa.
A duk lokacin da aka yi hira da ita, ta kan ja hankalin mutane a kan cewa a duk lokacin da aka samu Wa mara ji kamarta a cikin al'umma, kar a tsangwame shi, a ja shi a jiki a duba wace irin baiwa Allah ya yi masa a dafa masa a kanta, saboda Allah baya halittar abun da ba shi da amfani. Kamar dai ita da tun a tasowarta ko makaranta ba ta so saboda rashin jin ta, amma cikin ikon Allah a yanzu, ilimi na addini da na zamani sai dai ta koyar da wani bisa jagoranci da jajircewar mahaifiyarta yayyenta da kuma mijinta ta zama abun da ta zama a yanzu.




TAMMAT BI HAMDILLAH!!!


GODIYA TA TABBATA GA UBANGIJIN TAIKAI MAI KOWA MAI KOMAI, DA YA BANI IKON FARA RUBUTUN NAN YA BANI ARON RAI DA LAFIYA NA KAMMALA SHI. ALL???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?AH YA SANYA A AMFANA DA DARUSSAN DA KE CIKI, AKASIN HAKA KUMA ALLAH YA YAFE MANA.

SA?ON GAISUWA TA MUSSAMAN, UWAR KIRKI UWAR ALJANNA UWA TA TA KAINA, MALAMA NAFISU ADAMU, DA MUKA FARA TARE HAR NA KALLAMA ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MIKI HAR GADON BACCINKI.


GODIYA TA MUSAMMAN GA ?AN UWANA.
ZEE KUMURYA NIMCY LUV, TARE DA SAURAN MARUBUTA MAIMOON, MARYAM MAI ?OSAI ANTY ZEETY, KUNA DA YAWA GASKIYA DUK INA JI DA KU DAI.

BAN MANTA DA KU BA, MUTANEN DA SUKA BANI TALLACE TALLACENKU
MAMAN MEENAT COLLECTION
MAMAN KHADIJAH MAI SABAYAR ?AN GAYU TARE DA MAMAN ILHAM KUN GA DAI YADDA SUKA KANKARO RUMA A GIDAN AURENTA, KAR A GAJI DA CIGABA DA PATRONIZING KAYANSU, TESTED AND TRUSTED RUMA TA YI AMFANI DA SU KUN GANI.

WA?ANDA SUKA YI SUPPORTING ?INA, WURIN SAYEN LITTAFINA, ?AN NORMAL GROUP, SPECIAL DA AKE TURAWA TA PC, ?AN AREWABOOKS DUK INA GODIYA, DA SUPPORTING ?INA ALLAH YA ?ARO MUKU ARZIKI DA BU?I MARA YANKEWA.

WA?ANDA SUKA DIN GA FITAR MINI TARE DA KARANTAWA, BA TARE DA KUN SAYA BA, DA WANDA SUKA YI MINI AMFANI DA SHI WATA SIGAR BA TARE DA IZININA BA, INA YI MUKU TUNI DA ALLAH BAYA YAFE HAKKIN WANI A KAN WANI, IDAN KUN SHIRYA BIYANA HAKKINA.
0009450228
AISHA ADAM JAIZ BANK.


DOMIN GYARA SHARHI, KO SHAWARA ?OFATA A BU?E TAKE.
SAI MUN SA
08081012143

Rumaisa ta ja numfashi, sannan ta fito da wata waya, duk ta sha jiki, screen Win ma duk ya tsage, ta ce "Wannan wayar, ita ta fara haWani da takawa, kafin ?addara ta sake haWa mu a karo na biyu.
Silar haWuwarmu na farko wannan abu ne da ya shafi rayuwarmu ni da shi, bai shafi abubuwan da suke faruwa a yanzu ba"

Ta Wan yi shiru sannan ta cigaba da cewa, "Kamar yadda wasu suka sani, yayyena maza ne, nice ?arama da duk wanda ya sanni, aka yi mini shaidar rashin ji.
Wannan wayar na Wauke da wasu abubuwa da ka iya taimakawa jami'an tsaro, saboda a rashin ji na, bani da tsoro, kuma cikin ikon Allah ranar da mu ka tafi kai ziyara dangin mahaifina, muka haWa mota da ?an bindiga. A cikin wayar akwai hotunan wurare da abubuwa da na yi ta Wauka, ciki har da jakar bullet mai Wauke da wasu lambobi, da sunan SMOKE.
A rashin ji na, na tattauna da ?an bindigar, har shugaban su yake ce mini, ?asa ta san da zaman su, dan kuwa akwai kason su, a kasafin kuWi da ake duk shekara.
Kasancewar a lokacin bakomai nake ganewa ba, amma na fuskanci wasu abubuwan.

Zuwana garin su babana, wanda ?an bindiga kusan suke mulkar garin, nan ma nayi wata tattaunawar da wani dattijo da aka ?ona rigar su, sai shi kaWai, wanda shima yana da ala?a da ?an ta'adda.

Daga nan har zuwa lokacin da aka yi garkuwa da ni, abubuwan dai tamkar a mafarki, duk yadda za a bawa mutum labarin yadda abun yake, sai ya je ya gani. Na sha ba?ar wahala saboda ina da taurin kai da rashin jin magana, na daku kamar ba mutum ba, saboda ban daina rashin kunya ba.

Kwatsam! Aka kawo matar da silarta abubuwa da dama suka faru, mace da tsohon ciki, ta din ga magiyar a bari ta tafi, ko dan cikin jikinta, aka ce a kula wannan ajiyar wakili ce".

?iff Wakin yayi, Wambai ya ce "waye wakili, wane waikilin tukuna".

Turaki ya ce "A daina katse ta, mu bari ta kammala tukuna".

Rumaisa ta Wora da cewa "Lokacin da ta zo ina tsaka da rashin lafiya, halin da take ciki bai dameta ba kamar ni, ta kula da ni sosai da sosai, sai dai wasu lokutan sai tayi ta kuka, idan na bata ha?uri sai ta ce; ba sace ta da aka yi ne dameta ba, mijinta, ba yadda bai yi da ita ta fasa tafiya ba amma ta?i, sai kuma sanya hannun Wan uwanta a wurin saceta.

Ta bani labarin mijinta, iyayensa, yadda suke rayuwarsu, da kuma irin rayuwar da tayi a nasu gidan.

Ta gaya mini mahaifinta ya saka sunanta a kadararsa, kuma wasu kuWinsa na shiga account Win ta, saboda ita bai taSa mallaka mata wata kadara ba, saSanin ?an uwanta, da kowa yana da wani muhimmin abu da ya bashi.

Ta gaya mini matar mahaifin ta da yayyenta, sun uzzura mata sosai a kan hakan, kuma babu wanda ya san da zuwanta Nigeria, sai yayanta da ta gayawa, ta sanar masa ga ranar da zata je dubiya....

"?arya ne, me ki ke nufi, Jamil ne ya sanya aka yi garkuwa da aisha, wallahi ?arya ki ke yi, ni za a yi wa sharri, a cuci Wa na a Sata mana suna"

Wambai ya Wagawa babar su Jamil hannu, ya dubi ruma ya ce "Wani tabbaci zaki bamu a kan haka, ta yaya zamu yarda da ke?".

"Na yi wa anty aisha al?warurruka, bayan ta ce mini ta bani amanar mijinta da Wan

66 / 67