Kanwar Maza 3&4 Complete Hausa Novel

Author :  Ayshacool Category :  Love

Chapter   61 / 67

180K to 183K   out of 199.9K words

zo".

Ya ce "Eh, ranar Alhamis zan shigo"

Ta ce "To Allah ya kaimu, idan ka zo sai ayi shawara, ka turawa mama dubu Wari a sai mata abun da take so kan ka zo na neman albarka".

Ya ce "To ?ar mama, za ayi in sha Allah, zan cigaba da waya, zamu yi magana anjima"

Ya ajiye wayar yayi shiru, yana cigaba da fatan Allah ya sa Alhaji Aminu yana da ala?a da Iman.

Har gida Alhaji Aminu ya aika da direba, aka Waukko mai sunan baba, yana da matu?ar karamci da son mutane, kamar ya goya mai sunan baba da ya ganshi a gidansa.
Aljannar duniya, an kashe dukiya an zuba kayan alatu a gidan nan, kamar ba za a mutu ba, karen da yake gadin gidan kuwa bayan mai gadi, shi kansa ba na Nigeria bane ba.
Ga iyayen motoci a parking space.

Ya ce wa mai sunan baba "Mu je ka fara ganin Ade, ka gaya mata ta ha?ura da tafiya ?auye ko Allah ya sa ta yarda".

Tsohuwa ce, a ?alla zata shekara tamanin da biyar, tana zaune a ?asan carfet, tana shan fura, sai mita take da fulatanci ita da jikokinta.

Ta Waga kai ta ?ure mai sunan baba da ido, har ya ?arasa gabanta ya zauna.

"Ade, ga wanda yake ta yi mini ?o?ari a kan kayana, shi ya ce a baki ha?uri, dan Allah kar ki koma ?auye".

"Au jibo gulmata ka ke yi kana yamaWiWi da ni kenan, yaro na bar shanu da dabbobina a ?auye, an zo nan ?wam an ajiyeni, sanyi na neman yi mini illa, ga wannan yaran da suka addabe ni, ai zaman ?auye yafi daWi".

Mai sunan baba ko rantsuwa yayi ba zai yi kaffara ba, wannan matar na da ala?a da matarsa, duk da tsufanta, tsananin kammaninta da iman ba su Suya ba, sai a yanzu ma ya ga Iman ba kama take da Alhaji Aminu ba.

Ade ba ruwanta, ta din ga zuba tana bashi labarin yadda take son shanunta, tun da a cikinsu aka haifeta.
Kayan marmarin da ya zo da su, ya din ga Wauka yana Sarewa yana bata, tana karSa tana ci.

Ta ce "Kaga yadda ka ke yi mini Win nan, shi ba ya yi mini, kullum cikin rubutu yake da lissafin kuWi, Euro ya le?o mun gaisa, sai ya kama hanya ya tafi yawonsa"

Alhaji Aminu ya ce "Sai ka ce a ?auyen hakan suke yi miki"

"Eh amma dai idan na ga nagge, zuciyana na sanyi sosai"

"YallaSai kai baka da ?an uwana ne?"

Alhaji Aminu ya ce "Kowa ya kama gabansa, ka san ainihi daman mu fulanin tashi ne. To ?an uwan nawa galibi wasu suna wasu garuruwan, wasu ma wasu ?asashen. Ni ne Wan autan ta, ?auyen fa a gidan wani ?aninta take, wai an rabata da Wan uwanta, kamar Wan uwanta ya fimu"

"Ya fika mana, shi yana zama mu yi hira, kai sai shegen son kuWin tsiya".

"Ni zaki tozarta a gaban ba?o ko, saboda ya baki ayaba, da lemo, to yasin a daina yin ?osai a gidan nan, tun da ba kya so na"

Alhaji Aminu kamar kakarsa ya Wauki Ade, su yi ta faWa wasu lokutan, saboda shi ne ?aramin Wan ta.

Mai sunan baba ya Wan jima a gidan, sannan baba ya ce zai tafi, Ade ta din ga tambayarsa yaushe zai dawo, idan bai dawo ba, za ta ?ulle takalmanta a zaninta, ko ta katanga ta bi, ta gudu ta koma ?auye.

Mai sunan baba ya ce "Ai ba za ayi haka ba"

"Ka rabu da ita, karen nan zan kawo Wakinta na Waure, na ga ta wurin fita"

Ta galla masa harara ta ce "Tashi ke je Wakina, ka samo masa Wan biskit Win nan"

Alhaji Aminu ya ce "Biskit kuma? Ade kyautar nagge zaki bashi, me zai yi da wani biskit"

Mai sunan baba ya ga ?o?arin ta ma, rikicin taufan na ta ba na zage? bane ba.

Mai sunan baba har ya koma gidan da yake, yana al'ajabi, kuma ya yanke shawarar zai yi wa Mahmud zancen, koma ya zo lagos Win, ya je su ganewa idonsu, su san ta in da za a Sullowa lamarin.

Dan baya son yayi gaggawa, a zo a gane cewar ba su da wata ala?a.

***
Ammi ta kasa mantawa da matsananciyar cin amanar da babu uwani ta yi mata, har ta kai ba ta iya sakin jiki tayi magana a gaban kowa yanzu, saboda tsoro da tunanin kowa ma ba son ta yake yi tsakani da Allah ba.

Ranar da mai sunan baba zai koma, Iman gyara kala-kala, aka ?al?ale ko ina, ta shirya girke? ta sha kwalliya.

Dama har kirari yake yi mata da Wawisu sarkin ado, Iman akwai ado da kwalliya.

Sosai suka yi missing Win juna ita da shi, sai dai da ya kalleta, Alhaji Aminu yake tunawa da mahaifiyar sa.

Ya din ga jin tamkar yayi mata zancen, amma ya kasa.

Washegarin dawowarsa, da yamma ya shirya su ka yi wa mama siyayya, suka je gida gaisheta.

Mama tayi ta yi masa faWa a kan yanzu yana da iyali, yakamata ya mayar da hankali a kan gidansa, ?an samarinta sun Wauke mata komai, kuma dubu Warin ma da ya turo tayi yawa, jiransa take yi ya dawo dama.

Ya ce "Ni fa ba ruwana, ?ar ki ce ta ce ayi haka"

Mama ta ce "Kuma sai ka biye mata?"

Iman ta ce "Mama idan bamu yi muku ba, wa muke da shi? Ayi ta saka mana albarka kawai".

Mama ta ce "Albarka da addu'a kullum cikin su muke, amma dan mun haifeku ba ya nufin, mu takura rayuwarku, ina fatan dai kun je wurin hajiyar?"

Iman ta ce "Gobe in Allah ya kaimu za mu je ammi, a can zan wuni, shekaranjiya na koma gida, idan na kuma zuwa faWa za ta yi mini".

Mama ta ce "Ai faWan na gyara ne, mun kai ku Waki amma kullum ku ba kwa gajiya da zuwa gida"

Iman ta yi dariya ta ce "Mama kenan".

Kasancewar umar akwai kyauta, haka ya din ga bayar da kuWi, ga bikin Abubakar saura wata Waya kacal ya rage.

Mai sunan baba suka yi waya da Mahmud, ya tabbatar masa da shima zai shigo kano, dan haka umar ya ce idan ya shigo yana son su haWu za su yi magana.

Nusaiba har ta shirya tafiya makaranta, sun yi sallama da ammi, ammi tana ta fama Sabir, ya isheta da fitina, tana ta mita ta ce makaranta za a kai mata shi, ta huta.

Barira tana mata dariya ta ce "Anya ranki ya daWe, kin hana mamansa shi ma balle kai shi makaranta, idan aka kai shi, sai kin fi kowa damuwa"

"A'a ba wata damuwa gara a kai shi, tun da yayi baki"

"Ammi, ammi" Nusaiba ta shigo tana ?walawa ammi kira.

"Lafiya baki tafi makarantar ba?"

"Ammi wai yaya Mahmud ne ya dawo shekranjiya, wai ya je har gida ya yi wa Jabir dukan tsiya, ta ?arfin tsiya ya saka shi a mota a fita da shi, ya kai shi ofishin ?an sanda an rufe shi. Yau shi kuma ya wayi gari da ciwon ciki, a asibiti ma ya kwana bai san waye a kansa ba".



Ayshercool
08081012143
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR? DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ?URAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHE?I KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

=?I? *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1.? Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2.?? Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3.? Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4.? Supplements na karawa fata kyau da sheki? glowing skin*

*5.?? Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6.?? Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7.?? Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8.? Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9.? Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10.? Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11.? Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12.? Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13.? Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14.? Supplement na whitening/glowing skin*

*15.? Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

Paid book ne, ? 500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, ga masu bu?atar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book Win. Kar ku manta da subscribing YouTube channel Winmu na Cool hausa novels, domin samun daWaWan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ?anwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel Win*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please =?O?

*TALLA! TALLA!! TALLA!!!
*?AN?ANO DAGA LITTAFIN NAZEEFA SABO NASHE, MAI SUNA ?UDURAR ALLAH*

Ta Yaya zai zama jinina alhali ni na san bayan matana ban tab a kusantar wata mace ba? Ya furta kai tsaye yana kallon likitan da sakamakon gwajin yake hannunsa. Likitan yana jinjina kai ya sake furta  Tabbas Jaheed jininka don gwajin k wayar halittarku da komai ya tabbatar kai ne mahaifinsa kafin a kai ga haka ma ko Kamanninku da suka zamo kwabo da kwabo sun tabbatar da Hakan koda Ba a yi gwajin ba.

Shiru na tsawon lokaci d akin ya d auka kowa da irin tunanin da yake a ransa ya kasa yarjewa zuciyarsa shine Mahaifin Jaheed duk da k wararan shaidu. Abinda ya sani ko da wasa bayan matansa na aure na Sunna bai tab a rik ewa wata mace hannu ba, idan kuwa ya tabbata Jaheed d ansa ne ta yaya ya samar da cikin nasa a jikin wacce aka kira mahaifiyarsa da ko a mafarki bai tab a ganin mai kama da ita ba TABBAS AKWAI LAUJE CIKIN NAD i. Mahaifiyar Jaheed ma Zata iya zama abar tuhuma da zargi.? Kai tsaye zai iya cewa hakan zai iya zama K UDIRAR ALLAH& .

(*Ina ma'abota karance-karancen litatafan hausa, na san kun santa, Nazeefa sabo nashe, tsohuwar marubuciya, da ta saba nishaWantar da ku, da WaWan litatafan hausa masu ma'ana da ilimantarwa, ya kuke tunanin wannan turka-turka, DNA Win sa ya kasance daidai da na yaron da bai taSa ganin mahaifiyarsa ba, haka zalika a iya saninsa tun daga ?uruciya har girmansa, bai taSa aikata zina ba? Ku kasance da Nazeefa sabo nashe, dan jin yadda zata warware wannan turka-turka a cikin littafin ?udurar Allah. Masu bu?ata kai tsaye za su iya tuntuSar ta a kan lambar wayarta 08033748387*)

*Littafin kuWi ne, ? 500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*



Mi?ewa Ammi ta yi cikin sauri ta ce "A ina ki ka ji?"

Nusaiba ta ce "Yanzu su musa suke faWa, wai a asibiti ya kwana ma, tun cikin dare aka kai shi"

Rikicewa ammi tayi, ta nufi Wakinta, Nusaiba ta bita ta na cewa "Ammi me zaki yi?"

"Nusaiba asibitin zan tafi, ni babu wanda ya gaya mini ai"

Nusaiba ta ce "A'a Ammi, kar ki je su yi miki wani rashin mutuncin, ki fara kiran takawa ki gaya masa"

"Yaron ya kwana a asibiti, ki ce sai na kira takawa na gaya masa?"

"Dan Allah ammi ki bari ya zo tukuna, sai ku tafi tare ma, kar su cutar da ke" da ?yar Nusaiba ta shawo kanta, ta amince a kira takawan tukuna".

Juma'a ce, dan haka rumaisa ta ce ba zata makaranta ba, dan jikinta babu daWi ko ina ciwo yake yi mata.

Takawa sai lallaSata yake yi, yana son ya fita aiki, sai sangarta take yi masa, da shagwaSa kala-kala.

Wayar Ammi ya gani, dan haka ya Waga tare da yin sallama.

Cikin ruWewa ba tare da ta iya amsa sallamar ba ta ce "Takawa, kana ina ne? Mahmud aka kwantar a asibiti, wai ya kwana yana ciwon ciki jiya, so nake na je"

Takawa ya ce "Dan Allah ammi ki kwantar da hankalinki, ki bari na je wurin aiki, idan aka saukko daga masallacin juma'a zan zo na kai ki ki duba shi".

"Baka da hankali ne? Ka san ciwon ciki kuwa? Yaron ya kwana a asibiti amma ka ce sai an idar sa sallar juma'a awa nawa? Idan zaka kaini ka zo yanzu, idan ba zaka zo ba zan yi tafiyata ko me za su yi zan jure tun da ni na kai kaina"

"Kiyi ha?uri gani nan" rumaisa ta zuba masa ido, bayan ya kashe wayar ya ce "Duk ta rikice a kan Wan da bai san darajarta ba, nan zai yi ciwo ta je duba shi, ta hanata ganinsa ta ce bacci yake, ko baya son hayaniya amma za? taje duba shi, ammi ba ta gudun abun da zai Sata mata rai sam"

Ruma ta ce "Dan Allah zuciyar mutum ce a jikinka? Ka san me ake nufi da uwa da Wa kuwa? Kai banda dalilin sihiri da nake da tabbacin shi ya raba ammi da daddy, kai kana zaton akwai dalilin da zai sanya ta zuba ido ta barwa wata mata Wan ta.
To ai ko ni da abun da ke cikina bai zo duniya ba, da shi da Sabir, ban ga wanda ya isa rabani da su ba, kai idan aka ce za ayi asirin ma, sai na haWa asirin da bokan na ci ubansu wallahi.
Dan Allah papa kaima ka sassauta wannan ?iyayyar, yanzu bari in saka kaya in bika".

Ya ce "No, ki zauna a gida, zan je kawai"

Ruma ta ce "Hankalina ba zai kwanta ba, ka tafi da ni dan Allah, idan ba haka ba zan biyoka idan ka fita".

"Mimi kina da matsala, cikin nan ne bana son a gani".

Ta kalleshi ta ce "Saboda me?"

"Kin fi kowa sani ai, ba na son wani abu ya samu cikin nan naki, kullum cikin Addu'a nake yi Allah ya sa ki haihu lafiya, kin san komai ai"

"Babu abun da zai faru sai ikon Allah, ka tafi da ni saboda zatin Allah, hijjabi zan saka, ba wanda zai gan shi ai" kasancewar rumaisa ta ?ware a iya magiya, tamkar ?ar maro?a, haka ya sanyata a gaba suka tafi.

Da shi da Nusaiba, da Ammi, haka suka rankaya asibitin da aka ce Mahmud yana can.

Gaba Waya Ammi ba ta cikin nutsuwarta, takawa ya ce "Ammi dan Allah ki kwantar da hankalinki, kin San ki na da high bp".

A rikicen dai Ammi ta ce "Kai ka san sani high bp, ka tambayar mini Wakin da yake dan Allah "

Ruma ta din ga kallon ammi cikin tausayawa, haka ta shafe shekaru da soyayyar nan da tausayi suna nu?ur?usa zuciyarta, ruma ta jinjinawa mugunta irin ta mummy.

Ba ?aramin razana ammi tayi ba, ganin Mahmud a kwance ba ya motsi, ga ruwa an saka masa, ga kuma oxygen da take taimaka masa yana numfashi, gefensa kuma mummy ce a zaune.

"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Mahmud meya sameka haka?" Ammi ta yi maganar cikin rawar baki.

Jin muryarta ya sanya shi ya motsa, ya fara yi wa ammi nuni da hannunsa ta zo.

Cikin hanzari ammi ta ?arasa, idonta na ta zubar da hawaye.

Ya mi?a hannunsa ya ri?e nata, sai dai ba baki, sai hawaye da yake zuba ta gefen idonsa.

Ammi ta ri?e hannunsa tana jejjera masa sannu.

Ya Wora hannun a kan cikinsa.

Ruma ma ta ?arasa gaban sa cikin kuka ta ce "Daddy meyafaru? Meya sameka?"

Wata irin mi?a yayi bakin sa yana zubar da kumfa, cikin sar?ewar numfashi ya ce "Daughter mutuwa zan yi. Ammi. Amm....Ammi na faWa yau rumaisa, Ammi ki yi mini Addu'a cikina" yayi maganar tamkar numfashin sa zai bar gangar jikinsa.

Daga rumaisa har Ammi kuka kawai suke, Nusaiba ma kuka take.

Cikin kiWimewa Mummy ta tashi cikin azama, ta ce "Mahmud ciwo ba mutuwa bane ba, kar ka sake cewa zaka mutu, haba Mahmud kar ka yi mini haka dan Allah " tayi maganar tana fashewa da kuka.

Ya buWe ido a galabaice ya kalli Mummy, ya zare hannunsa daga na ammi, ya ri?o nata "Mummy na gode, na gode Mummy"

Ya sake zare hannunsa daga na Mummy, ya mi?awa adam, sannan ya cewa ruma "Ki ce masa ko sau Waya ya ri?e hannuna Daughter" ya yi maganar yana sake mimmi?e wa.

Cikin matsanancin kuka da tashin hankali rumaisa ta kalli Adam ta ce "Papa dan Allah"

Adam da tuni ya karaya, kuma

61 / 67