Tame Gari 1 Complete Hausa Novel

Author :  Asma Baffa Category :  Romance

Chapter   9 / 33

24K to 27K   out of 96.3K words

yima yarinyar wani abu toh sai yaga shi yafi cutuwa qara maimaita tambayar tayi hakan ya katse mishi tunanin dayake yi ko baka jina?

tun yaushe ma ai ba qaramar lallasata nayi ba i hp dai daddy ma baya nan dan ban son ya ganta a wannan yanayin gashi kuma yusra kinsan ta da rigima tace lallai saita koma yau dan wai kada inyi kisan kai ganin yadda na lugwiguita mata jiki

ah to indai haka ne gara ta dawo din dan daddy'n ku yana nan kada kuma ya ganta yace meya sameta ta fada mishi gaskiya kasan shi fa akan yarinyar nan kamar wanda aka sihirce dan haka inaga kawai ku barta ta qara kwana kafin nan ta dan murmure sai ta dawo bayan ya tafi ni kuma in barje nawa haushin


no mamy ai duk hukuncin daya kamata ayi mata zan gama yi mata kedai barni da ita kawai amma dai ki turo a dauketa din kawai


tunda kun matsa dai to ka kawota mana kaga ma saika san abinda zaka fadima daddy'n naku ka fadi wani laifin tayi ka hukuntata

nikam yadda nake din nan ina zan iya fita ki ganni ya fada a zuciyarsa


ya naji kayi shuru


naga ne zaiyi wuya in samu lokaci dan inada meeting karfe 8 din nan na dare gashi zai daukemu lokaci kuma kinga ni inama zan sami time har inkawo ta kawai dai ki turo din inya so kisan me zaki fadawa daddy inya ganta ko kuma kawai ma ki hana haduwar ta so


ok to hakan yayi bani yusra


mika mata wayar yayi suka qara magana ta kashe wayar



******



shi kuwa habeeb ba qaramin fama yasha ba kafin sajida ta fahimceshi saida yasha aikin rarrashi tare da fada mata kalaman da suka kwantar mata da hankali kafin suka koma normal


****


ita ko dije koda ta farka ganin wai hartayi baccin gaske daga na qarya ganin yadda suka kwasa da gudu dazun duk tana kallonsu jin duk jikinta na ciwo ga kuma fatarta data tashi inda naseer ya daketa tunawa da abinda tayi musu kuma yasata sakin dariya tare da fadi a fili ta furta wlh tunda kuka yimin haka sau kun sani wato ni kuka kawo ga jaka kuyita dimata har kwana biyu hhhhhh bakusan dije bane na gwada muku kalata ta fuskar rahma kunki fahimta yanzu aka fara game din let's see who's d winner between us dakin dake pacing dinta ta nufa koda ta shiga hakan ya nuna mata bedroom din yusra ne dan haka kanta tsaye ta nufi toilet din dakin heater ta kunna har ruwan yayi dumi kafin ta fara yin wanka tanayi tana wash tare da matsar kwalla tana kuma ayyana irin fansar da zata dauka akan su


niko nace dije banda kuma kisan kai 🀣


ta jima sosai kafin ta gama ta dauro alwala tana fitowa ta bude wardrope ta shiga neman kaya sai kace dakinta tasan duk kayan yusra sun mata yawa duk da ba wai sosai ba dan haka ta shiga neman ko doguwar riga ce cikin sa'a ta samu kasancewar rigar nada madauri saitayi mata dai dai bayan tayi sallah ta fito farlon inda ta hango mutan gidan nata zuro kai ta qofa suna leqe


duk tana lura dasu ta share su ta zo parlour ta zauna tare da dora kafa daya kan daya ta shiga tunanin meya kamata tayi musu ne ma


ba ta jima ba ta tsinkayi bugub qofar falon tare da sallama kwarai ta dau murya ta baba habu driver ce amsawa tayi tare da fadin ana zuwa


su kuwa mutan gidan sunaji aka fara takaddama nasir yace yusra ta fita ita tace shi ya fita kowa yaqi fitowa cikin hasala yace wlh dai kinji kunya wai wannan 'yar mitsitsiyar yarinyar tasa ki kasa fita dan tsoro


mun dai ji kunya ni da kai idan kai ka kirani babba akanta amma akanmu fa nida ita ai kaine kai kuma yakamata ka fita ka sallameta tunda kaine me gidan ni kam bazan je ba dan ko yanzu ban gama jin zafin ciwon jikina ba haka kawai yarinya ta zo ta qaramin wani ciwon kana gani ma dan raini harda samin kaya ni inka fita ma kaja mata kunne ta ciremin kaya wlh ko inzo inci mata uwa


bude qofar gayi tare da fadin zo ki je da kanki ki fada mata zuwa da kai ai yafi sako maza zo ya fada yana me nuna mata hanya


wlh ba inda zani dan ba sunana saratu ba zan iya zuciya in shake yarinya har saita mutu kaga ko maganin kada ayi kar a fara wuce ka sallameta tabar min gida


yaso ya qara magana amma ya qyale yasan halin yusra akwai rai ni gara ya koma mata nasir din kada taga damar sa


cikin hade rai ya fito tare da nufo inda dije ke zaune


ko kallonta beyi ba ya wuceta ya nufi qofar falon bayan ya bude suka gaisa da baba habu kafin yace bari ya kira dijen ta fito su tafi


yana shirin shiga sukayi kacibis da ita


ke maza inda abinda zaki dauka dauko ki wuce gida


to tace tare da rabashi ta wuce


a ranshi yace wannan duk wanda ya aureki ya aurarwa kansa masifa da kudinsa


bakin mota ta nufa shi kuma yana ganin haka ya koma ciki


tana qarasawa bakin motar ta dubi baba habu tace



baba dan Allah inda hali aromin wayarka in kira daddy


mika mata yayi yana washe baki bayan ya matso number Alhajin


flashing tayi inda daddy na zaune yana cin abinci yaga shigowar kiran habu driver kuma yasan ya tafi dauko khadija hajiya ta fada masa dan haka yssan ba mamaki akwai magana shiyasa ya yi dialling number


muryar dije yaji dan haka cikin sauri yace lfy diyata?


lfy qalau daddy dama naga baba ne yazo daukata kuma ni gaskiya daman um....dama...kinga fadi kawai kanki tsaye khadija me kk bukata


dama cewa zanyi munyi magana ne da Aunty yusra da ita matar yaya habeeb shine suka ce in dawo nan da zama toh shine nace su fada maka wai bazasu iya ba shine nace ni bari na fada maka



dadi daddy yaji dan haka cikin sakin fuska yace kaji su to ai wannan ba matsala bane duk dayane ai naji dadi kwarai


to nagode daddy gobe abawa baba habu yakawomin unifoam dina zan wuce school in mun taso sai in biyo in dauki kayana


toh badamuwa Allah yayi muku albarka


ameen daddy ta kashe wayar tare da miqawa baba habu tace ya tafi kawai


ita ko ta juya ta koma cikin gidan


tana shiga falon ta tarar da su zaune jin bude kofar suka jiyo suna ganin dije kusan a tare suka furta lfy?me kika dawo yi kuma

bata tamka musu ba saita fara kokarin zama saida ta zauna kafin tace naji kunce kuna son nayi muku kwana biyu ne shine nace bari in zauna din yafi kada in tafi kuga rashin kyautawata ko mamy tayi fada


mun shiga ukuπŸ™†β€β™€



🀣🀣


*vote*
*comments*
*with 08066364077*



*Alqalamin khady✍*
πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€

*TA ME GARI*

1⃣6⃣

*ina neman afuwan mutane pls dan Allah ku dinga min adalci nasan masoya basa yawa kuma daukaka daga Allah take ina iyakar kokarina wajen ganin na faranta ran kowacce a cikin masoya na idan kun tambayeni littafin daga farko ko wani page din ban tura muku ba kuyi min uzuri kun san jiki da jini kuma inada abin yi amma nake sadaukar da lokacina dan nishadin ku duk wadda take son littafin tayi magana group nasan zata samu pls afuwan dan Allah na kuma gode da soyayyarku gareni Allah ya bar kauna ya qara zumunci*

***

kut......in kin isa Allah ya tsinen ai wlh bazan zauna da 'yar jagaliya a gidana ba cewar yusra ta fada tana huci

shima nasir cikin hade rai yace ke ina wasa dake ne ?wlh tun muna mu kadai ki tashi ki tafi gida waye zai yadda ibola ta zauna masa a gida har kwana biyu ko ki tashi wlh ko in babbala ki a kwasheki a kaiki

gani sukayi ta miqe yusra da dama tun tuni ta miqe tsaye ta riqe kugu ganin dije tayo kanta yasata kwasa da gudu tayi bayan naseer wanda shima ganin dijen ta miqe ya danji wani abu a zuciyarsa amma fa gara ya nuna mata shima namiji ne dan haka saiya dake ya tsaya yana fadin ke yusra meye haka ban son iskanci

saida ta qaraso gabansa kafin ta kalleshi ido cikin ido shiko kawar da kai yayi domin shi in yana kallon idonta sai yaga kamar idon mage bare yanzu daya qara tabbatarwa kansa yarinyar nan ruwa biyu ce wato mutum aljanπŸ˜‚dan haka be son hada ido da ita kada yaje ko maguzawan ne akanta arnan farko su nuna masa basu san hasken addini ba

tsinkayar muryarta yayi tana fadin

haba yayana yanzu kawai dan nace zan kwana biyu gidan ka kk korata bayan kuma tun farko ku kuka nemi da in zo inyi kwana biyu a wajenku ai ko ba komai nayi muku haka dan zumunci amma tunda bakwaso shikenan

jin kalaman datayi yasashi sauke a jiyar zuciya domin yasan yanzu zata ce zata tafi amma me ?

sai ji yayi tace tunda na fuskanci baka son in zauna gidanku hakan na nufin tun yanzu zumuncinmu zai samu rauni kuma nasan megari bazaiji dadi ba bare iyayenmu dan haka na yanke shawarar zamana a gidan nan har sai ranar da nayi aure

😳

me?

la'ilahaillah anta subahanaka inni kuntu minazalimin

a'uzubillahi minasshaidanir rajim

ka manta baka hada da ayatul kursiyyu ba

cewar yusra dake bayan naseer wanda keta kwarara addu'o'i kawai dan dije tace zata zauna a gidansu

itako dije dariya ma abin yabata cikin zuciyarta tace ikon Allah sai kallo

ganin yaki yin shuru banda ruwan dala'ilai ba abinda yakeyi hakan yasa dije fadin haba ya naseer meye naga kanata addu'a ko wani abun ne yafaru ?

kinga khadija dan girman Allah da ma'aikinsa na rokeki ki taimaka ki koma gida kinji

to wai sbd me?

ta tamvaya

yasan sha'anin jinni be zama lallai yarinyar tasan meta aikata musu ba kuma baya son tasani dindan haka saiya waske yace kawai kinga mamy nada hawan jini ga shi ma yau mura take fama da ita matsananciya ina ma zargin limoniya gareta kinga gara kije ki zauna kusa da ita nasan zaki taimaka mata da wasu abubuwan

hakane kam yakamata in koma

yauwa qanwata ya fada a dan raunane

yusrah ma harda gyada kai tare da fadin wlh kam gara kije dan tayi kewarki

toh shikenan ta fada tare da fadin

ni zan wuce toh saida safe

Allah ya tsare ya kiyaye a sauka lfy

qofar falon ta nufa har ta isa sai kuma ta tsaya ta juyo yake sukayi mata tare da wiving din hannu ita wlh dariya ma suka bata dan haka saida ta dara tare da fadin

lah ya naseer meya sameku ne a fuska kaida aunty yusra naga duk kunji ciwo

saurin kallon juna sukayi kafin daga baya suka hada baki wajen fadin Accident

subahanallah accident kuma?da kura ko kuma da kare dan wannan ai naga ciwon kamar bada mota ko wani qarfe akayi shi ba ko

da biri mukayi fada naseer ya fada yana yashe baki

.biri kuma a ina?

ai da yake akwai shi a nan gidan toh shine ina masa wasa ya yakusheni yusra ma haka

.wow gaskiya wlh har kunsa nafasa tafiya sbd wlh ina son biri dama

.wayyyoooo 🀣

dan girman Allah ki tafi kawai gobe zan kawo miki shi

ah ah nidai ina son ganinshi wlh

ai nasa an kasheshi

what ?

kisa fa?

akan me?

.sabd yaji mana ciwo har haka saina lura gaba gaba zai iya daukar rai ma

amma ko wannan biri sai kace ba dan nigeria ba

ah ah dan boko haram ne

au dama dabbobi ma suna zama 'yan ta'adda

ai.....kaga dan Allah ka barta ta tafi dare yanayi kuma gashi taxi zata shiga Allah ya kaiki lfy sister cewar yusrah dake tahowa danta dan tura dije

au ni kinga ma fa na manta wlh aunty ashe fa baba habu ya tafi ko yanzu ya zanyi to ni dije ta fada tare da rike haba

.akwai abinyi kawai kinga bari nadauko miki kudi kishiga taxi tunda baki da su ko

ah ah barsu kawai inaga inada su a jakata zasu isheni zuwa gida

to a gaida su daddy zasu ji tace tana qoqarin fita

tana ficewa kuwa yusra ta rufe qofar tare da sauke ajiyar zuciya haka shima naseer din

bakin gate ta nufa gurin me gadin gidan inda ta samu guri tazauna suka shiga hira kamar sun san juna tun da can gumi fa ta hadu da anka nan kayan zance ya hadu sukaita zubawa kuwa kafin daga baya taji qarar mota a waje koda suka leqa baba habu ta gani da kayanta a akwati kin kim kim musa me gadi ne ya karbi kayan tace ya tafi kawai nan ya juya ya musu saida safe

ganin dare nayi ne yasata miqewa tare da fadin toh baba musa zan shiga ciki saida safe ko

toh hajiya mu kwana lfy

Allah yasa ta fada tare da jan trolly dinta

harta nufi part din su yusrah kuma saita fasa ta tsaya ta danyi jimm kafin ta juya akalarta zuwa part din su habeeb tana zuwa ta shiga knoking a hankali a daidai wannan lokacin suna zaune suna hira tare da dan taba kallo jin ana buga kofar yasa shi fadin waye a hankali

shiru tayi sai da ya qara maimaitawa kafin tace nice

jin muryar mace yasa sajida saurin miqewa ta nufi kofar tana fadin kece wa?

khadija!!

bude qofar tayi sukayi ido hudu da dije inda gaban sajida ya yanke yafadi ganinta da tayi da jaka dirkekiya

lfy ?

ta tambayeta cikin dan hade rai

kallonta dije tayi ganin yadda tayi mata tambayar yasata itama hade nata ran kafin tace lfy lau mana ta karasa maganar tana me kutsa kai palon

sai yanzu ya dago ya dubesu shima ganin dije da jaka yasashi mamaki tare da fadin ke lfy naganki da jaka haka kamar me shirin barin gari

guri ta samu ta zauna tare da fadin lfy lau wlh nadauka daddy ya kiraka yayi maka bayani ai shine yace in zauna inyi kwana biyu anan nama shirya zan tafi sai gashi yasa an aikomin da kaya na toh da zanje part din ya naseer sai naga kaine babba kada kaga ban kyauta ba gara in zauna anan ko

hmmm haka

tunda yace haka be qara fadin komai ba illa juyawa da yayi ya kalli sajida dake tsaye kikam ta zuba musu ido maida kallonsa yayi ga tv din itama sajida ganin haka yasata samun guri tazauna dan nesa dashi

sun jima a haka banda karar tv babu abinda kk ji a falon itako dije duk jikinta ciwo yake mata gashi tana jin yunwa ga bacci data fara ji

gyaran murya tayi kafin tace am yaya nace ba

kallonta ya juyi yayi jin yadda take son yin magana dashi lallai ma yarinyar nan yafada a ranshi

itako ko'a jikinta tace wai azumi kukeyi ne a gidan nan?

cikin rashin fahimtar magsnarta yace kamar ya ban gane ba kina nufin na nafila ko me?

ah ah na dare nake nufi naga ne ko ruwa ba'a bani ba ga yunwa da nakeji kamar hanjina zai tsinke toh naga kada inyi nauyin baki tunda ni bana azumin gara a in magantu kada in cuci kaina

binta yayi da kallo wanda tarasa na meye shi kanshi ya kasa tantancewa ko kala be ceba taga ya miqe tare da daukar wayarsa ya nufi dakinsa

ganin hakan datayi yasata fadin to ko masauki a tausaya a bani ai ko tunda abincin bazai samu ba nazo gidan economic masu auna ci da ciyar da wani

rasa me zai ce yayi kaji yarinya sai kace irin kurege shi sam be son yawan magana bare wasa dan haka cikin dan hade rai yace ki tambayi matar gidan mana ai itace da gidan yana gama fadar hakan ya shige daki

sajida data tsaya kallon ikon Allah tare da nazari inda daga karshe taji dadin yadda habeeb din yai sannan tasaki ranta tare da fadin oh khadija baki abin magana ga gajen haquri tashi muje in nuna miki inda zaki sauka

ok ta fada tare da mikewa dakinta dayan takaita inda tace ta zauna a kawo mata abinci

ah ah ni ai a gidan nan nafi qarfin a kawomin kice dai in tashi in dibarwa kaina kawai in hidimtawa kaina kada kizo inga laifinki kin san hausawa sunce mu dangin miji ba'a iya mana

kallonta sajida tayi tare da nazarin yarinyar wannan yarinyar fitinanniya ce ta qarshe amma zanyi maganinki ta fada a ranta........

naso inyi muku yafiv haka amma kaina ciwo yakeyi bacci😚

*vote*
*comments*[3/14, 9:18 PM] El~hajj: πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€πŸŒ€

TA ME GARI

1⃣7⃣

nayi adungure na wulwula na heqo na mazgo gaisuwa ta tare da jinjina ga dukkan masoya ta me gari tare da jinjinar ban girma ga members na khadija. fans novels 1 da khadija fans novels 2 ina ganin comments dinku gaskiya kuna yin dije da yawa 😘

miqewa tayi ta tabi bayan sajida wadda ke ganin ikon Allah ganin da gaske take bin nata zatayi yasata juyowa tare da fadin

haba qanwarmu ai kya tsaya inyi dawainiya dake ko iya na yau ne ko a matsayinki na bakuwa kamar yadda kk fada

dakatawa dije tayi tare da fadin ah ah matar yaya bawai fa wani dalili yasa nace ki bari in nemawa kaina d'a'amin ba kawai sai dan kin san iyawa mutum sai Allah kuma gashi naga bakisan da zuwana ba kada in saki wahala kije kawai ki kula da mijinki dan naga alamar ke yake jira bakin ciki ya cika masa zuciya kije ki rarrasheshi

kallonta sajida tayi tare da fadin wane irin bakin ciki kuma ?

ah bakin cikin zuwana mana shin wai be baki labarin abinda ke tsakaninmu ba?

dammmm gaban sajida ya fadi cikin karfin hali tace meye tsakanin kun ?

ah lallai da sauran ku tunda har yanzu be fada miki ainihin sahihin abinda ya hadani dashi ba

zuciyar sajida fa tafara cunkushewa jin yarinyar na ambatar wai alaqa tsakaninta da habeeb shin me hakan ke nufi?wace alaqa ce kuma?to ko dai ya so yarinyar ne ?kai no habeeb

9 / 33