Tame Gari 1 Complete Hausa Novel

Author :  Asma Baffa Category :  Romance

Chapter   22 / 33

63K to 66K   out of 96.3K words

kara bawa daddy mamaki da haushi illa tattaro sajida da yusra da mamy tayi kuma babu kunya suka nuna masa suma. sun gajiba zasu iya zama a kauyen ba har kwanakin da sukayi niyya su cika ba.

sawa yayi aka kira masa su Habeeb inda a gabansu yace matan su maimaita abinda suka ce,ai kuwa ba kunya sajida ta zage ta dinga rattaba bayanin cin fuska harda cewa wai mayu sun kamata daga zuwa,ganin da Habeeb yayi ta zake dayawa tana ta cin mutuncin asalinshi yasa ya daka mata tsawa ransa matukar bace.

Daddy ne ya daga masa hannu alamun ya kyaleta,aikuwa taci gaba,har saida takai inda take son tsayawa kafin ta tsaya.

Tana idarwa mamy ta amshe nan itama tayi me isarta bawanda ya tamka,harta gaji tayi shuru.

Itako yusra ta kanta takeyi dan laulayin da takeyi shiyasa tayi shuru bata ce komai ba ta tsaya tan sauraren su itadai kawai ta masu ta ganta a gida.

murmushin takaici Daddy yayi kafin ya kalli mamy yace,

"yanzu Karima duk wannan cin mutuncin da kikeyi saboda kawai kinzo kauye ne?

ai bawai batun nazo kauye bane,ni fa a rayuwata natsani kauye kai ni bama kauye ba duk wani jinin talaka wallahi,saboda shi talaka kullum burinshi yaga mai kudi ya wulakanta saboda tsananin hassada da......

ya isa haka!! daddy ya dakatae da ita

Amma ai kin san ko ni wanene kika aureni kuma kin san asalin inda dangina suke ko?

Ai kai ka daina danganta kanka da wadan nan mutanen dan kai Allah yayi maka sutura,inba ma basu barka haka ba waye zai samu ya kubuta daga wannan masifar ta zaman kauye ta dawo kuma wai ko da sunan ziyara.

Hmmmm!!! hakane naji nakuma gode sosai,amma kisani wallahi ban yadda ki koma gidaba dukanku har sai kwanakin dana dibar mana ya cika.

Gangan ma kenan!! ai wallahi bazan kara yadda na kwana da 'ya'yan mutane ba su macemun anan in shiga uku,tafiya kam kamar da kasa,kai da aka binne cibiyarka anan ka zauna har kwanakin su cika saika dawo,Dan haka ku tashi mu tafi tun kafin rana tayi mana.

Mikewa sukayi duka suka nufi kofar fita Daddy baiko ce musu kala ba.

Har sun kai bakin kofa suka Tsinkayi muryar Habeeb ya kira sunan Sajida yace,

Indai nine mijinki ban yadda kibar garin nan batare da izinina ba kuma sai kwanakin da mukayi niyya sun cika.

shima Naseer haka ya fadawa yusrah.

To ni a matsayina na uwarku na basu izinin su wuce mu tafi in kuma ban isa ba sai inji labari,kafin fa juya ta kalli su sajida tace,

In kuma a cikinku akwai mai zama banyiwa kowa dole ba kuna iya zamanku.

Ai wallahi mamh in kin ganni a lahira kaini akayi cewar Sajida,dan ni da kara zuwa wannan kauyen har abada dan haka muje kawai mamy karsu karasa kasheni.

suna gab da fita daddy yace,kin kyauta Karima amma wannan lokackn zan nuna miki ko ni waye kuje Allah ya kiyaye hanya amma wallahi zan shayar dake mamakin da baki taba tsammani ba........

*vote*
*comments*
*with*
*Alkalamin khady*
[3/15, 11:26 PM] El~hajj: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀

*AWESOME WRITER'S ASSO..*🇳
(palace of excitation n'd pleasant writer's)

*TAME GARI*

NA
khadeeja usman

3⃣9⃣

Zaune yake gaban baba maigari yana yi masa bayani,inda baba malam din ya tattara nutsuwarsa gaba daya ga zancen dan nasa,tare da tunani mai zurfi akan abinda yake shirin aikatawa,dan haka yayi shuru yana saurarensa har saida yakai aya,kafin ya sauke goron numfashi yayi jim kadan yana nazari.

Tabbas maganar dansa gaskiya ce,gaba ake ji ba baya ba,domin karima tana so matuka ta tarwatsa musu zumunci yaransu masu tasowa,gashi maganganun ta sunyi tsauri,bata jin kunyar nuna kyamar ko waye indai dan kauye ne ko talaka,yayi tunanin abin zai tsaya iya kanta ne sai gashi tasa harda surukanta wanda suma sun dauki wannan mummunar akidar ta kin mutanen kauye da kyamar talaka,tabbas inya barta wannan abin yayi tasiri,"toh fa tabarbarewar zumunci za'a samu a zuriyarsa",wadda baya fatan hakan.

maganar daddy ce ta fargar dashi ga tunanin daya tafi,inda daddy ke cewa,inka amince baba ina son ayi abinda na fada abi shawarata dan wannan lokacin nayi rantsuwa wallahi saina nuna mata kalata da bata taba gani ba.

Ka kara hakuri khamis, dan dukka rayuwar hakuri akeyi musamman sha'anin mata,sai dai ni kaina wannan lokacin abinda tayi ya taba zuciyata,amma hukuncin daka yanke kana ganin baiyi tsauri ba akan su?

Baba ai wannan hukuncin shine dai- dai dasu,shine zai sa su shiga taitayinsu.

To kayi shawara da yaran naka ko?

Banyi ba baba!

Amma nasan babu wanda zaiyi mun musu a cikinsu.

To shikenan!!

mu bari zuwa anjima mu tattauna da sauran 'yan uwanka sai muji yadda za'ayi ko?

Toh baba!! Allah yasaka da alkhairi.

Ameen! Allah yayi muku albarka baki daya.

Ameen

nan yayi masa sallama ya fice dan gaisawa da jama'ar dake jiransa a waje.

su kuwa su mamy,ba wanda suka wa sallama ko kallon arziki haka suka hada kayansu suka tafi bayan sun gama cin mutunci da yadda maganganu wai an kama su za'a cinye su an kawo su garken mayu.
_____*********______

Zaune take gefen gadon Innah suna hira ita da Zainab diyar wajen baba bala kanin mahaifin ta,inda zainab din keta yaba kyan da Dije tayi tare da sanar da ita irin surutun datake sha a kauyen na wai taki aure ta tsaya karatun boko.

Dagowa Dije tayi ta kalleta kafin tace,

"kin san Allah ne yaso mutanen garin nan ban karasa wayo na anan ba", da wallahi duk saina sa su ciwon baki,dan kut.....nafasa,

Ah ah!! da kin karasa ai.

Ai na auna na auno na kuma hango ba amfanin karasawar ne,amma inba gulma da shegen tsegumi irin na mutanen kauye ba,meye laifin karatun boko,kuma ma duka nawa muke da har za'a damu dan bamuyi aure ba,su je su ga inda uwayen mata suke,wadana suke cikin jin dadi ga nera ta zauna,gasu bul-bul dasu kamar kajin gidan gona,amma ba mashin shini,sun gama cika har sun fashe.

kamar dai matar yaya Habeebu kenan ko?

dan ni nayi mamakin da aka ce wai itace amaryar sa.

Dariya Dije tayi kafin tace,

To me kika gani game da wannan,badan kar kice nayi miki karya ba wallahi da sai ince miki akwai iyayenta a kasa.

kinga basai kin karasa ba dan wallahi nasan halinki Dije da karyar masifa,duk uwar data haifi kamar wannan.matar ai ta kusa cizon kasa.

kinga fa abinda ke hadani dake da can kenan shiyasa nake kilarki,dan karyata ni da kikeyi,sai ki bari kije ki ganewa idonki wata rana.

Ah ah ni wallahi bada ni ba,kina kallon cin mutuncin da shegun nan sukayi mana,ai naga kokarin zamanki tare dasu da banga alamun targade ko karaya a tare dake ba,saima wani fresh da kikayi.

hmmmm!! kedai abar kaza cikin gashinta,kin san dai halin Dije kowa yayi mata saita rama,to hakan ce ta dinga faruwa shiyasa nasami sa'ida,amma wallahi da in kun ganni sai kun dauka a jejin sambisa nayi rayuwa.

Shegiya!! kice kinji abar,

hmm kedai kawai mubar maganar,bari intashi mu wuce kawai kar rana tayi.

A tsakar gida suka iske Innah tana gyaran shinkafa,inda sukayi mata sallama suka fice ta bisu da Addu'ar Allah ya tsare a kuma gaishe mata ita.

****

wannan karon ma kamar wancan lokacin yara baibaye su sukayi har suka sallami mai mashin suka nufi kofar gidan,

da sallama suka shiga inda suka iske Hansai jingim zaune tana bakacen geron da daalama surfawa tayi.

har wani murgudewa tayi garin amsa sallamar da kuma ido biyu da tayi da jami'ar tsaronsu wato Dije.

cikin sauri bakinta har yana hardewa ta shiga kwadawa Inna Haule kira,aikuwa sai gata nan itama a sukwane jin kiran da Hansai ke mata,tana zazzaga masifa da ya zuwa yanzu ita ke mulkin dan haka ta taho tana fadin,"ke wai lafiya kike ta kwalamin kira kamar naci bashi",

Turus tayi ganin jami'ar tsaron su tsaye ta harde hannuwa.

washe baki ta shiga yi inda ta fara fadin,

marhaban lale! yau kice kun kewayo sannunku da zuwa,ai ko yaushe munata tsimayi da sa idon yaushe zaku bullo ashe zuwan bazata kukeyi,kai amma munji dadin ziyarar nan wallahi,ke Hansai maza tashi ki dauko musu tabarma mana da ruwan sha,

Ganin yadda ta yunkura da kyar dan ta mike,Dije a ranta ta furta Astagafirullah!!! Allah mai halittar bawa yanda ya so yanzu kalli ko hannun ta kawai yayi ni gaba daya,ganin kafin ta mike din ma wani sabon jidalin ne yasa Dije fadin,

Ina ita Dayar abokiya zaman tata take?

Allah sarki!! Ai sun tafi neman kudi ita da mijinta yanzu haka suna legas,tun bayan haihuwarta,

Allah sarki!

ashe harta haihu kenan?

eh tasamu diyarta mace ansa mata suna Hadiza.

washe baki Dije tayi cikin nuna farin ciki tace kai amma Allah ya raya,yaushe zasu dawo?

ai basu jima da tafiya ba dan dama da Hansai ya fara tafiya daga baya ya dawo da ita data cika kwanakin ta saiya dauki Hafsy din.

nan Dije ta kara sabin sharhi da sabbin dokoki kafin tayi musu sallama suka ce zasu koma

har kaji madu rai Inna haule tasa aka kama guda biyu d sauran tsarabun kauye ta bawa su Dije a cewarta da ta fada komar 'yan sanda gara tayi kyautar shiga daka kayi kuka.

**************

Yau jumma'a dan haka tun safe maigari ya tattara iyalinsa gaba daya manyan yaransa ya kira ya sanar dasu abinda ke faruwa,tare da kuma bukatar da dan uwansu yazo da ita,dukan su sun amince sun bada goyon baya,

Amma baba Inusa ya dan jimanta abun a ransa amma daya tuna zumunci abu ne mai girma sai kawai yayi addu'a.

Ana idar da sllar juma'a daruruwan mutane suka shaida daurin Auren zuriyar gidan mai gari.

KHADIJA INUSA
DA
HABEEB KHAMIS

ZAINAB KABIRU
DA
NASEER KHAMIS

Tare da mai gayya mai aiki madugu uban tafiya.

ALHAJI KHAMIS (Daddy)

da

Zarkwadediyar amaryarsa,tsohuwar budurwarsa wadda yaso aure tun farko Allah baiyi ba wato

MARYAMA diya ga kanwar maigari amma ita yanxu da sanin ta da amincewar ta dan tun zuwan su Daddy daya ganta tazo gidan mai gari aka sanar masa mijinta ya rasu gashi dama bata taba haihuwa ba,to fa sai tsohuwar soyayya ta motsa nan aka shiga tuna baya sai kuma lamari yazo akan gaba.

*tabbbbbb......Alkur'an ba ruwana dan akwai bom*

*vote*
*comments*
*with*
*Alqalamin khady*
[3/15, 11:27 PM] El~hajj: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀

*AWESOME WRITER'S ASSO...🇳
(palace of excitation n'd pleasant writer's)

*TAME GARI*

NA
Khadeeja usman

4⃣0⃣

Tuni labari ya iso gari cewar,an daura auren Daddy da kuma yaranshi,abinka da kauye,nan da nan magana ta bazu,masu sa albarka nayi,masu tsegumi nayi.

kasancewar ana idar da sallah kuma cikin masallaci aka daura auren, yasa su Habeeb dake nesa daga waje suke jin kamar kunnensu gizo yayi musu jin kamar an ambaci sunayen su wajen daura auren.

Suna nan tsaye suka hango fitowar su Daddy da maigari anata mika musu hannu tare da yi musu Allah ya sanya alkhairi inda sukaita washe baki,da alamun farkn ciki a fuskar su,suka nhfo inda su Habeeb din suke,wadanda suma ya zuwa yanzu sauran 'yan uwa nata zuwa suna basu hannu,tare da ce musu Allah yasanya alkhairi,lamarin daya kara daure musu kai kenan har su Daddy suka iso inda suna zuwa suka tasa su gaba batare da dogon bayani ba zuwa gida,dukan su ji sukayi jikinsu yayi sanyi toh me yake faruwa? yanzu haka inka bibbiya aure aka daura a gidan Daddy zaisa suyi alheri shine ya kirasu.Da wannan tunanin suka karasa gidan.

Nan ma suna shiga gida yadau guda da fadin ga angwaye nan,inda sauran mata da abokan wasa suka shiga tsokanar su,lamarin daya kara sasu yin yake dan badai murmushi ba.

Jan su baba malam yayi zuwa bangaren shi,inda suna zuwa suka samu guri suka zube yarab dan ba wani mai kwari cikinsu,duk da basu tabbatar da abinda suke zargi ba.

Bayan baba malam gayi gyaran murya nan ya shig rattabo musu bayanin komai game da abinda suka ji kuma suka gani yanzu,inda ya dinga musu sharhin da sam bama sa fahimtar shi har ya kare batunsa Daddy ya shigo ya karbe,nan din shima ya fada musu dalilinsa nayin hakan,ganin kowannensu baice komai ba yasa Daddy yakalle su yace,

"Naji kunyi shuru", ko baku karbi hukuncin danayi yanke muku ba? ko baku yadda da zabin nawa ba?

Nan ma shurun sukayi har saida ya kara magana.

Mun Amince Daddy Allah yasa haka shine mafi alkhairi!

Ameen!! Allah yayi muku albarka ya albarkaci zuriyarku baki daya,yasa kuyi alfahari da wannan auren ko bayan ba mu.

kai kayi alfahari da Auren Khadija,kai ma kayi da taka matar zainabu!

Ameen suka amsa

nan maigari da Daddy suka fice suka barsu zaune an rasa ma me cewa kanzil kowanne zuciyarsa cike da tunani barkatai.

wani abu suka tuna lokaci daya ksmar kowa yasan abinda ke zuciyar kowa kawai sai suka saki dariya inda suka kalli juna suka kuma hade rai.

Wallahi ni dai an cuce ni,dan ni a tsarin rayuwata ban shirya qara aure yanzu ba,cewar Naseer.

Wai kai aka cuta ko ni? ni da a tsarina ba auren mace fiye da daya,ai gara kai kana da niyyar karawa wata rana ni kuwa fa?kai ni duk bama wannan ba a ma rasa wadda za'a hadani da ita sai Khadija kawai dan tsabar ci baya,yarin yar da bata cikakken bacci kullum Aljanu na bisa kanta,so akeyi nima tazo gidana ta haifamin irinta masu fitinar tsiya,to wa ma zan nunawa wannan tatsitsiyar yarinyar ince wai mata ta ce! ni wannan ma ba shine abin ji ba shiyas kaga nayi dariya dazu,yadda gidanmu zai kama da wuta,idan su mamy suka sami labarin abinda ya faru,ni wallahi da za'aimun gata da sakin yarinyar nan zanyi salin alin batare da ankai ruwa rana ba.

Kana sakinta ni kuma sai ince a bani ita a bar Zainab din,dan wallahi gara khadija sau dubu akan Zainab,kai ba fa kaga kafafunta ba wallahi sunyi nawa,gata baka,kai ni wallahi ni aka fi cuta,khadija kuwa nasanta nasan halinta sai in lallaba ta muyi zamanmu hankali kwance wallahi magani ma zan nemar mata.

Ji yayi ransa ya baci da kalaman Naseer,dan haka cikin dan zafi yace,

kai wane irin mahaukaci ne? matar tawa kake fadin wadan nan maganganun akanta?

ah to ya kake son ince?

kai tunda baka so ba sai ayi furfure ba,Wallahi ni da gudu zan amshe ta,kai ni fa da ni aka bawa ita bazanyi wani bakin ciki sosai ba duk da ban shirya ba,amma ya zanyi ance kaddara ta riga fata,ya karasa maganar kamar zai fashe da kuka.

Hmmm!!!! lallai Naseer kayi nisa ya fada yana me mikewa ya cire rigarshi ya fada saman gadon yayi rufda ciki,tare da lumshe idonsa,ya rasa dalili sam baya jin bakin cikin yin auren da akayi mishi,amma kuma baya farin ciki,tunanin khadija ya fara yi zamansu da duk wata dramar da aka dinga kwasa a zuciyarsa ya furta,ashe ba'ayi komai ba tukun dramar na nan gaba.

Shiko Naseer tunanin kafafun Zajnab kawai yakeyi,wai ya zaiyi inya tashi sai mata takalmi.?

🤔

*Ni ko nake lallai kowa da abinda ya dame shi*

*ga wannan ku dan taba dan naji dadin comments dinku akan page din jiya,ku dai tanaji ruwan kashe wuta dan har yanzu fa Dije bata da labari ,bare kuma uwayen gayya 'yan birni,masu brush da kwandala*

*vote*
*comments*
*with*
*Alqalamin khady* ✍[3/18, 8:02 AM] El~hajj: 🌀🌀🌀🌀🌀🌀

*AWESOME WRITER'S ASS..* 🇳
(palace of excitation n'd pleasant writer's)

*TAME GARI*

4⃣1⃣

Da gudunta ta shigo dakin,inda ta iske Dije kwance rashe-rashe saman gadon Innah,tana waya da Ishaq.

Ganin yadda ta shigo din yasa Dijen dagowa ta kalleta,batare data kashe wayar ba tace,

ke kuma lfy malam kika shigowa mutane a haukace haka ? ina tsaka da soyayya ta zaki katsemun jin dadinta!!!

Au kice zani ce ta tadda muje bari kawai inyi shuru da bakina tunda abin nema ne duka ya samu,kin san da jikon da akayi tun da can kenan!

ban fahimci abunda kike magana akai ba? wata ce ta zageni ko tayi gulmata inje in kaddamar mata maxa fadamun da sauri kar hawan ruwana ya tashi",

Sha kuruminki ni nadauka ma kin samu labari amma naga alamar baki san da zancen ba,to albishirinki!!

Goro fari kal!

meye tukwicin?

"nabaki dan mutum da uwarsa"

masha Allah

to karkarde kunnuwanki kisha labari.

ke ni in zaki fadamun abu ki fadamun in bazaki fadamun ba ki kara gaba ki barni insha luv dina da rabin raina.

gyara zama tayi,kafin tace,

.Allah yayiwa maigari albarka Allah ya ja da kwana.

Ameen Dije ta amsa dan ta matsu taji meya ke faruwa.

kin san tun ranar dana fara ganin su yaya Naseer naji duk duniya ba namijin danake so saishi,amma saboda nasan ya wuce ajina dan ba abinda zaiyi da 'yar kauye da kuma hango halin mamansa da nayi yasa na cirewa raina wannan banzan tunanin,ban san ma ina sonsa ba har yanzu saida naji yayi aure kuma naga matarsa yanzu ,har ga Allah naji kishinta matuka,amma ganin wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa yasa nacire abun a raina.

to cikin ikon Allah da kuma yardar sa yau gashi Allah ya amshi rokona ya cika min burina,tsoho mai ran karfe yayi abinda zan ta yimasa addu'a har karshen rayuwata.

Ke ni fadamin meya faru ne nagaji dajin soki burutsun ki.

kafin ta bata amsa suka tsinkayi muryar Inna tana magana cikin kuka tana fadin,

Wallahi bazai yiyu ba malam,sai dai ince kayi hakuri wannan lokacin,nasan ban taba sabawa umarninka ba amma wannan lokacin dole inyi magana,ta yaya ma hakan zai yiyu! duk da yarinyar nan bata fito ta fada mana irin zaman datayi a birni ba,amma ai munada hankali,kuma zuwan su ya nuna ya kuma tabbatar da batayi zaman wani jin dadi a can ba,nasan halin Dije da shegen kafiya da taurin kai,shiyasa ta zauna,duk a bar majjjjjjjjjj ta wannan ta yaya kake tunanin Dije zata iya zaman kishi da wannan matar wadda ko ni uwar ta ban isa ba,yakamata a dinga mun adalci,Dije ita kadai Allah ya bani duk wani hukunci da kuke yankewa a kanta ban taba magana akai ba,amma wannan lokacin ina ganin anyi abinda bai dace ba gaskiya,dan dalilinku bai kai dalilin da zaku hada su aure ba alhalin kun san ba son junansu sukeyijjjj ba,kai yau ko Dije tacemun tana son yaron nan wallahi bazan bari ta aure shi ba dan bata isa yin kishi da wannan guzumar matar ba,indai ba so kuke a kawomin gawar ta ba wata rana..ta karasa magabar tana me sharbejjj majina.

tunda ta fara maganar ya kafeta da ido yana saurararta har takai aya,shuru yayi yana nazarin maganar ta tabbas yasan saude mace ce mai hakuri da kawaici ga dukkan lamuranta,yasan malam na yanke hukunci akan kowa kuma ya zauna babu mai muds masa dan haka akanshi baza'a fara ba,shi kanshi yasan wannan hadin

22 / 33