Author : Asma Baffa Category : Romance
muku banida carji afuwan
*vote*,
*comments*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady* โ
[16/12, 11:41] โช+234 806 493 3819โฌ: ๐๐๐๐๐๐
TA ME GARI
NA
khadija usman
1โฃ4โฃ
tun sassafe ta shirya ta tafi makaranta a can suka hadu da su rufaida aka shiga hirar yaushe gamo tare da tambayarta yadda tabaro mutanen gida
bayan ta dawo a parlo ta iske mamy zaune ita da wata hajiya saudat qawarta tana duba wasu kaya da sallama ta shigo parlon ta tsugunna ta gaishesu cikin fara'a hajiya saudat ta amsa amma ita ko mamy ciki ciki ta amsa dan har yanzu tana kule da yarinyar tarasa wane mataki yakamata ya dauka akanta amma kawai bari ta turata gidan su naseer tasan acan su zasuci ubanta ba ruwanta koda abu ya biyo baya sunfi kusa
am kinaji na cewar mamy
dije da har ta mike ta fuskanci da ita take dan haka tace eh mamy
maza idan kin shiga ki shirya ki fito kizo habu ya kaiki gidan yayyenki ku gaisa da su kije kiga amare tunda kin gudu bakije kinga gida ba koh ?
ta karasa maganar tana murmushin mugunta
tunda dije taga mamy na murmushi tasan akwai abinda ta shirya mata dan haka cikin ranta tace dena gaigaye mamy nima da shirina zan tafi gudun bacin rana amma a fili saita ce to bari inje in shirya
yauwa to yi sauri kinji
dije dariya ma abin yaso bata a iya shekarin datayi a gidan nan tana iya cewa bata taba samun dariya ko magana irin haka ba a gurin mamy amma yau sai gashi wai ita take yashewa baki dan kawai tasan inma taje ubanta zataci
da sauri ta shirya ta fadawa basira inda zata sannan ta debi guzurinta a 'yar qaramar hand bag dinta ta fito saye da doguwar riga arebian gown cofee colour inda ta sanar da mamy ta fito wasu kaya ta bata tace ta kaiwa yusra zata kirata a waya tarasa dalilin daya sa mamy harda wani farin ciki takeyi dan ta turata gidan a ranta tace wlh kome zai faru sai dai raba biyu kowa yaji jiki
suna tafiya ita da baba habu driver sun zo dai dai wani store tace dan Allah ya tsaya tana zuwa ba musu ya tsaya ta shiga gutin ba jimawa ta fito tace su tafi yaja mota kuwa suna tafe suna hira har suka qaraso gidan
tabbas gida yayi kyau matuka babu makusa inda cikin sanyin jiki ta fito ta nufi bangaren dama dan bata san ya tsarin gidan yake ba
tana zuwa bakin parlourn ta shiga kwankwasawa an dan jima kafin taji ance yes come in
murda handle din kofar tayi ta shiga parlourn tabbas ya hadu iya haduwa ba qarya inda ta shiga da sallama dauke a bakinta ga mamakinta sai gani tayi yusra na washe baki tare da fadin oyoyo sister ta taso da niyyar rungumeta
qamewa tayi a gurin tana kallon ikon Allah murmushi yusrah tayi tare da qarasawa ta rungume dije itama dijen ganin yadda tayin yasata itama yin hakan ta dan jima a haka kafin ta saketa ta kamo hannunta tare da fadin qaraso ki zauna ya gajiyar tafiya ance shekaran jiya kika dawo kinyi gudun hijirar gashi kin dawo kin same mu ya mutan gidan duk lfy suke dai ko?
ita dai dije yake kawai takeyi dan tasan wlh wannan faran faran din da dalili hmmm koma meye ai zan gani bari na biki yadda kk so sakin jiki tayi suka shiga hira tamkar ba yusran data sani ba amma dije ta tabbatar da dalilin yin hakan aikuwa suna tsaka da hira taga wayar yusra tayi qara dauka tayi tare da barin falon ta shige bedroom dinta takai wajen minti 30 kafin ta fito ta sake neman guri ta zauna tare da fadin me za'a kawo miki sister ban dai yi girki ba nasan ze biyo da take away so something with drinks duk akwai su ba matsala
um um ba abinda zan sha ga sakonki inji mamy ta miqa mata ledar hannunta karba tayi tare da fadin tnx
yusrah ce ta kara kallon dije kafin tace naga kinki sakin jikinki ki manta da komai kawai kinji
no ba haka bane tashi ma zanyi in tafi naga yamma tayi
kije ina? cewar yusrah a dan hade rai
gida mana kinga bamuyi da baba habu ya zo ya daukeni ba gara in tashi da wuri dan taxi zan shiga
ah ah wlh bazai ma yiyu ba kizo gidan nan baki hadu da yayanki ba ai bazai ma sabu ba nasan ya kusa dawowa kawai ki jirashi ta karasa maganar tana murmushin da ita kadai tasan dalilin yinshi
tsaf dije ta karanceta a ranta tace hmm kin girmeni amma baki fini wayo ba tabbas in kuka min abinda ban gamsu dashi ba toh naku salon muguntar da zanyi muku saiya ci uwar wannan a fili kuwa cewa tayi ok to bari in leka bangaren ya habeeb ko
ok ba matsala muje in rakaki miqewa tayi ta suka fita
part din sajida zaune suka sameta sanye cikin riga da wando three quater sai wata 'yar mitsitsiyar riga wadda da kadan ta rufe cibiyarta kanta yasha qananan kitso jikin nan sai kamshi ke tashi sajida bata da kyau kwarai amma akwai wanka domin irin matan nan ne masu son komai suga sune a farko shiyasa komai nata yake kan gaba ko cikin friends dinta
da fara'arta ta tarbesu amma ta rasa dalili tun ranar da ta tambayi habeeb meye alaqar su da dije ya fada mata da ganinta da tayi gurin dinner taji sam bata ra'ayinta ko da ta ganta yanzu gabanta saida ya fadi amma sbd halinta na 'yan duniya kuma goggiyar 'yan boko yasata sakin fuska nan ta karbi dije hannu bibbiyu abinci me rai da motsi takawowa dije inda ta bude ciki taci t koshi dan dama yunwa takeji tunda dawowarta kenan daga skull mami ta tunkudota nan ba laifi amaryar habeeb ta iya girki amma dai gaskiya basu dace ba cewar dije dan wannan ai kusan sa'arsa ce
sun dan taba hira kafin suka tashi suka koma part din yusrah inda suna shiga yusra ta shige ciki tace ma dije tana zuwa miqewa tayi itama ta shiga toilet din dake parlour ta dauro alwala tazo tayi sallar la'asar
bayan ta idar ne ta koma kan kujera ta kama kallon wani film da ake haskawa a bollywood film din yatafi da hankalinta hakan yasa sam bataji tsayuwar mota a gidan ba illa jin sallamarshi kawai da taji yayi
amsawa tayi ga mamakinta shima din cikin sakin fuska ya shiga fadin ah ah mutanen kauye yaushe aka dawo?
kallon mamaki tayi masa tare da fadin shekaran jiya
to an dawo lfy?
lfy qalau suna gaisheku
hmmm muna amsawa
ok bari na shiga ciki in dan watsa ruwa
shiru tayu bata bashi amsa ba a ranta tace kinga dije anya kuwa bazaki tashi ki gudu ba ba mamaki mutanen nan shirya yankaki suka yi dan kin san dai ko giyar wake kika sha bamai yimiki dariya irin wannan amma da ganin yadda suka miki kin san da mugunta a zuciyarsu dan haka tunda qafafunki ki tashi ki fece kafin a karya miki su miqewa tayi ta nufi qofa harta daga labulen ta tsinkayi muryar yusra na fadin ina kuma zaki?
am dama zan tafi ne tunda ya dawo
cikin hade rai tace mamy bata fada miki cewar sai kinyi kwana biyu zaki koma ba
zaro ido tayi tare da fadin kwana biyu fa a nan gidan?
eh ko bazaki zauna ba?
to amma ai ban taho da kaya ba kuma ma skull dina fa?
iyeeeh lallai yarinya wato skull dinki da yaushe kika fara bokon yau she ma ministry tasan da zamanki shine zaki fadamun makaranta to bari ma kiji da ke kin dauka abinda kikamin kisha a banza wlh duk duniya bawanda ya isa ya hana inci ubanki ba duka ba zagi amma zaman prison zakiyi a gidan nan na tsawon kwana biyu cikin awa biyu kika barar min da burin danaci a bikina toh ke cikin kwana biyu sai duk wanda ya ganki ya tausaya miki dan haka kada ki kuskura ki fita a gidan nan dan dama an sanar da me gadi kada yabari ki fita
kirjin dije fa ya shiga lugude inda takeji kamar ta arta bata san tanadin da sukai mata ba tasan ma makaman yakin su sunfi nata dan haka ta yunkura da niyyar artawa taji ya riketa haba classic lady ina zaki kuma ai kinzo gida kuma sai jibi ya fada tare da hade rai mutsu mutsun kwacewa takeyi inda ya riqe hannun da karfi riqo bana wasa ba hakan yasata sakin qara don jinda tayi yana barazanar ballata wurgi yayi da ita gefen kujera inda saida kanta ya dan bugu kafin ya dauketa da wani wawan marin dayasa ta ganin star wata qarar ta saki yayi saurin aza hannunshi a saman bakin shi alamar tayi mishi shuru
kasa shirun tayi inda nan ya shiga fyadarta yusra na gefe tana dariyar mugunta saida ya gama canzawa dije hallitar fata abinka da fari duk jikin sai yayi ja yayi rudu rudu kafin ya kyaleta ya zauna yana maida numfashi
cikin daurewar fuska yace dan uwarki ubanwa yasa kiyi min abinda kikaimin
shiru tayi in banda shasshekekar kuka ba abinda takeyi da alama dije akwai zuciya
yusar ce ta taso cikin daga murya dan uwarki ba magana akeyi miki ba ta karasa maganar cikin daka tsawa
uwarki ce๐
sukaji ta ce ๐
cikin zaro ido kusan a tare suka fadi
me kikace
cikin jan kuka da majina tace cewa nayu uwarki ce kuma wlh tunda kuka taba mana godiyarmu duk sai kunci ubanku
kallon kallo aka shiga yi shi naseer yana nazari da tunanin rainin hankalin yarinya itako yusra ta tuna da yadda suka kwashe kwanakin baya amma kuma kai ai da gani wannan ba irin wadan can bace dan haka a hasale tayo kan dije da niyyar dukanta wata irin zabura dije tayi kayo cikin yusra ganin da yusra tayi dije tayo kanta yasata sakin ihu tayi bayan naseer
ke ni zaki yiwa iskanci cewar naseer wlh zan babbala ki
itako dije ko'a jikknta ta nufosu tana qara barw baki miqa hannu yayi da niyyar riqota aikuwa tayi caraf da hannun a bakinta ta dankara masa cizo kuma gam ta rike hannun qara ya saki wadda tasa yusra saurin barin gurin ta ruga da gudu tayi bayan kujera duk yadda yaso ta saki hannun ki tayi saida taga jini yana bin yatsansa besan sadda yakai mata mangari ba aikuwa zafin da taji ne yasata tashi ta dane bayansa ta shiga yakushinsa tako ina baji ba gani cizo duk ta dabaibayeshi ga azabar da hannunsa keyi ga jini nabin yatsan dan ta dauke mai fatar koma cinyewa tayi oho waya sani
duk yadda yaso yaraba dije da jikknsa abu ya faskara gashj tana kuka tana yakushinsa duk ta damalmale masa jiki ta hada masa jini da majina cikkn daga murya ya kira sunan yusra sakamakon wani dankareren cizon da dije ta mallara masa a kunne hakan yasa shi finci kota da iya qarfinsa ta fada kan kujerar da yusra ta labe a bayanta riqe da waya jikinta na makyarkyata tana son yin kira takasa nemo number ma ido biyu sukayi da dije aikuwa ta kwalla wata qara wadda duk gidan ya amsa kanta dije tayi ta cakumeta aikuwa yusra memakon ta tabuka wani abun sai kawai ta bude baki ta shiga kurma ihu nan ko dije ta fara caskala ta itama harda rabon nata cizon a kumatu
ganin tana shirin kashe masa mata yayo kanta ai kafin ya qaraso ta saki dije ta qara nufarsa ba shiri shima ya juya dan ko kadan bazai so ta qara dane shi ba yarinya kamar mayya sai shan jini takeyi
habeeb na zaune a parlour shida sajida suka tsinkayi ihun yusrah da sauri suka taso suka nufo part din suna zuwa suka shiga kokarin budewa dan lokacin da naseer ya kamo dije da niyyar duka yusrah ce harda rufe kofa dan haka suka shiga bugawa yana fadin nasir nasir lfy bude mana
yusra ce ta nufi kofar danta bude dije tasha gabanta tanata kada kai tana bude baki naseer ko nacan yasa tissue yanata qoqarin goge jinin dake bin hannunsa da bayan kunnansa fuskarsa kuwa tuni duk ta hade tayi burdin burdin dan tasha yakushi
da dabara yasamu ya qaraso ya bude kofar
ya salam meya faru haka naganku a wannan yanayin ?
kafin yabada amsa yaji kukan dije daga cikin parlourn
leqawa yayi aikuwa ya ganta ta fara jifa da duk abinda ke falon tanayi tana kuka
tambayar nasir yayi meke faruwa nan ya sanar masa dalili
gurin dije ya nufa inda take kokarin jefo da wani fishers dishuis ya riqeta gam tare da hadata da jikinsa ya rungume ta tsam ya shiga yi mata addu'o'i a kunne
dije na jinsa tayi luf tare da qara gyara kwanciyar kanta a kirjinsa dukansu sai suka tsinci kansu cikin yanayi me wuyar fassarawa dije kam sai sauke ajiyar zuciya takeyi tare da qara shakar daddadan kamshi turaren dake jikinshi har take taji wani bacci na shirin kwasheta
jin shirun da sukayi ne yasa naseer leqowa dan duk su yusra da sajida gayyar tsorone hakan yasa suka kame a waje
yanayin daya gansu ciki duba da yadda yaga habeeb ya wani rufe ido bakinsa saitin kunnen dije gashi kuma ita ta wani lafe a jikinshi
duk radadin da ilahirin jikinshi keyi mishi sai yaji ya dena ji yayin da yaji zuciyarsa tayi masa wani irin zafi dan me zai rungumeta haka to me hakan ke nufi
jin shirun da matan sukayi ne yasa su dan shirin leqowa dan da alama abun ya lafa tunda sunji shiru aikuwa suna leqowa idon su yasauka akan abinda naseer ya kurewa gani
daram dammmmmm gaban sajida yayi dubs da yadda taga mijinta rungume da wata mace bata san lokacin datayi kansu ba tana zuwa tajanye dije daga jikinsa dije najin an jata tayi saurin qara langabewa ta zube a gurin
shi kuwa bude idonsa yayi a hankali ai kuwa ya saukesu cikin na sajida data kafeshi da ido ckin tuhuma waigawa yayi ya kalli inda dije ta sheme kafin ya maida dubansa ga naseer yace sai ku maidata gida tunda kun rama
yana gama fadar haka ya juya ya fice a dole sajida ta bishi itama............
*vote*
*comment*
*with 08066364077*
*Alqalamin khady*โ
[16/12, 11:41] โช+234 806 493 3819โฌ: ๐๐๐๐๐๐
TA ME GARI
1โฃ5โฃ
team dijeee kuna qarawa wutar nan fetur sai dai fa kuma hmmm a dai yi shuru yanzu muci gaba da gashi
ga masu tambayar littafin daga farko masu kirana da masu yimin mgn ta pc pls ku taimaka ku dinga tambaya a group dina in baki ciki kiyi min magana zan tura link kiyi join nasan mutan gidana akwai karrama bako da kin tambaya zasu hau tururuwar tura miki dan akwai su da karamci ๐
ina mugu mugun ji daku member's na khadeeja fans novels๐
******
ita kam yusra ko ta kan dije dake kwance bata qara biba ta lallaba ta shige daki shima naseer din binta yayi inda ba shiri dole ya dauki emergency care box suka nufi part din habeeb yayi musu dressing kafin suka dawo ind take kwance har yanzu tana nan yadda suka barta itako dije bacci ne ma yadauketa a gurin sai sauke ajiyar zuciya takeyi cikin baccin
koda suka shigo suka risketa a hakan naseer ya kalli yusra yace ke jeki tasheta ta tafi gida
wani kallo tayi masa kafin tace kai ka tasheta mana
ah ah naga dai ai ke yafi cancanta daki tasheta tunda ke kika sa aka kawo miki ita
hmm lallai to ai sai kayi duba cikin ni dakai wayafi wani shan jiki kaga kenan wanda yafi wahala shine yafi matsuwa da a barshi ya huta ni zaka danawa tarko inje in tabata tayimin yadda ta yi maka ka ganka kuwa?ta fada tare da sakin dariya
kulewa naseer yayi kafin yace ban ganni ba amma na ganki ki duba gefen bakinki da kuma kumatunki ga dankwalelen cycle nan an zana miki na musamman dan haka ki wuce kije ki tasheta ta bar gidan nan ina zaman zamana ke da mamy kunja an rudamin jiki yanzu ta ina zan doshi zuba ruwa duk yarinya tabi ta yage mutane sai kace kura nk ina zargin ma a garin nan akwai damusoshi alamu sun nuna cikinsu ta girma ga kuma 'ya'yan aljanu nidai wannan yarinyar ba qaramar jaraba baba malam ya jefo mana ba
kaga ni wlh duk ba wannan ba yanzu dai ka samo min maganin da zansha wlh ji nakeyi fuskata duk ta daure
hararar ta yayi kafin yace toh duk azabar da kk ji bata kai ya wadda nake ji ba
suna tsaka da maganar dije tayi juyi tare da yin miqa alamar zata tashi
da gudu suka kwasa suna rige rigen shiga daki wajen shiga dakin ma yusra ta riga shiga inda tana shiga dai dai naseer ya kawo kai danya kutsa ai kuwa ji kk yi bamm tare da wani sauti qummmm goshinsa ya daki qofar ko zafin daya ji baibi ta kai ba ya danna qofar ya qarasa sa key din kafin ya jingina bayansa da kofar suka shiga maida numfashi kamar wadanda suka yi gudu ko wani aikin wahala
jin goshinsa yayi kololo ne yasashi sa hannu ya taba yaji zafi kuwa kallon yusra yayi dake zaune gefen gado tana mayar da numfashi kafin yace kinga maza ki kira mamy ta turo a kwashi yarinyar nan
da sauri ko ta dauki wayarsa ta shiga kiran layin mamy
tana dagawa yusra tace yauwa mamy pls ki turo a dauki yarinyar nsn pls
jin hakan da mamy tayi yasata fadin baku kuka ce a barta tayi kwana biyu ba meye kuma na cewa ta dawo yau ko har kun gama huce fushin naku ne?
ai gara kawai ta tafi din inba haka ba...fizge wayar naseer yayi tare da fadin hello mamy
au kana kusa ashe ya akayi ne naji kunce a turo a dauketa yau ince ko kaci ubanta dai ko
yasan halin mamy inya fada mata abinda ya faru zata iya sasu daukar wani matakin shi kuma a nashi tunanin ya lura duk lokacin da ya