Jeeddahtulkhair Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Khaleesat Haidar Category :  Romance

Chapter   92 / 117

273K to 276K   out of 348.6K words

shi nayi farkon auranmu... To ina xan yarda naga abinda ya fi karfina??" Jiddah ta sunkuyar da kanta, Aneesah tace "Ranan kuwa da na amince kwanan mu uku a asibiti, sai kuma na fara ganin canji daga garesa, kin san su maxa bayan sun samu abinda suke so shkkn... Har yau kuma ina danasanin amince masa" Jiddah ta kalleta da sauri, Aneesah tace "Wllh wllh na ci ubana a wajensa..." dariya Aneesah tayi tace "Ae ranan na ji ke kin samu daman ihun ma, ni ina na samu wnn daman, kuma da xa ku tafi Abuja naga kina tafiyar ki ras, nace ahh lallai ke naki da sauki" Jiddah taki ce mata komai, Aneesah tace "Ko ba haka ba?" Jiddah tace "Me fa?" Aneesah tace "Au wai duk xancen nan baki gane ba" Jiddah tace "Aa ban gane ba" Bude kofar dakin aka yi, Abuturrab ya kalli Aneesah sannan ya kalli Jiddah, Aneesah ta washe baki tace "A waje ka bar motar Captain? ko xaka fita ne?" Bai ce komai ba ya karaso ya ajiye takeaways din hannunsa, Aneesah ta mike tace "Toh Jiddah na gaisheki, bari in je banyi la'asar ba wllh, nagode da tuwo" Daga haka ta nufi kofa da plate din tuwonta ta fita, Jiddah ta bi ta da kallo, Bayan ta fita Abuturrab ya kalli Jiddah yace "Me ta shigo yi?" Jiddah ta girgixa masa kai kawai, daukan takeaway daya yayi cikin guda biyun da ya siyo, ya nufi kofa ya fita Jiddah ta bi sa da kallo, sai kuma ta mike da sauri ta jingina da kofarta bayan few seconds ta bude kofar a hankali tana kallon kofar dakin Aneesah, a kulle taga kofar, ta sauko downstairs sai ta gansa xaune parlor, da sauri ta juya ta koma sama. Da daddare Jiddah ta d'an ci abincin da Abuturrab ya bar mata, ta fita da sauran downstairs xata kai kitchen, Aneesah dake xaune parlor tana kallon wani series ta bi ta da kallo, bayan jidda ta fito kitchen din ta dauke kanta da sauri, ganin Jiddah xata wuce sama Aneesah tace "Ga lemon kankana da abarba nayi Jiddah" Jiddah ta d'an kalleta tace "Aa nagode" Aneesah ta hade rai tace "Naga har yanxu kamar kin ki sakewa da ni Jiddah, yanxun nan fa nayi sa a kitchen, shine na debi nawa na bar maki sauran a jug, captain din ma idan xai sha sai ki basa" Jiddah tace "Yanxu na gama cin abinci" Aneesah tace "Toh ai wannan ba abinci bane lemo ne" Jiddah ta d'an yi shiru, sai kuma ta karasa cikin parlon, Ta dau jug din tace "Xan kai sama, nagode" Aneesah tace "Toh shkkn, sai ki tafi da cup" Daukan cup din tayi ta wuce sama Aneesah ta bi ta da kallo, Jiddah na shiga dakinta ta ajiye Jug din da cup a kasa kusa da mirror dinta, sannan ta cire hijab dinta ta shiga wanka. Tana xaune gaban mirror tana shafe shafenta Abuturrab ya shigo ta kallesa sau daya ta dauke kai, lumshe ido yayi don kamshin turaren da ta sa na karshe ya daki xuciyarsa, ya nufi bayanta ya tsaya ya dafa shoulders dinta a hankali yace "Have u eaten?" Ta gyada masa kai da sauri xuciyarta na bugawa, ya kalli Jug dake ajiye yace "Wannan fa?" Tace "Naka ne tace a ajiye maka" wani kallo yyi ma jug din sai kuma ya nufi kofa ya fice daga dakin, ita dai ta sauke ajiyar xuciya gama abinda xata yi ta saka kayan baccinta tayi kwanciyarta ta rufa da duvet ta rufe idonta. Aneesah dake xaune parlor sae bin Abuturrab that is wearing just short and singlet take yi da kallo, sosai take missing dinsa, rabonta da shi kusan wata daya da sati biyu kenan, Safara'u kuma na gidan a duk lkcn balle ta sama ma kanta mafita, kallon agogo dake nuna karfe goma da minti arba'in tayi ganin ya haura sama rike da cup din plane water ta san bangarensa xai je ya hada coffee don tuni ya dauke coffee powder dinsa a kitchen sbda karewan da yake a kwana biyu kuma Safara'u ce ke sha sau biyar sau shidda a rana, Aneesah ta kashe kayan kallon parlon da fitila sannan ta haura saman ita ma, dakinta ta shiga cikin mintuna kadan ta fito ta nufi bangarensa tana baxa kamshi, xaune ta samesa a parlornsa yana kallon wrestling hannunsa rike da cup din coffee, sau daya ya kalleta ya ci gaba da kallon da yake, ta xauna gefensa tana kallonsa a hankali cike da kissa tace "It seems u are still angry at me Captain, naga sai wani hade min rai kake kaki sakewa da ni, snn i notice dakin Jiddah da na shiga daxu kamar u are not happy about it, ni kuma ba da wata manufa na shiga ba ina son mu xauna lafiya da yarinyar ne don naga bata da matsala ko a wancan lkcn ma ni kadai nake haukana ita kam babu ruwanta" Abuturrab yace "Kilan u misperceived me, but i am not against ku xauna lafiya ai..." Kwanciya tayi a kirjinsa ta lumshe ido tayi kasa da murya tace "Toh fushin da kake da ni har yanxu fa?" Ya ajiye cup din hannunsa don saura kadan ya sake yace "Idan kika canxa halin ki xan daina fushi da ke" Tashi yake son yi ta ki sakesa ta marairaice tace "Muna magana kuma ina xa ka Captain?" Yace "I want to get my laptop" Abinda tasan tana masa xai yi turning dinsa on ta shiga yi masa, ya koma ya jingina da kujera trying to control himself yace "Stop that Aneesah, i need to go get my Desktop" Ko sauraronsa bata yi ba, Bata sake kuma basa daman magana ba, sai da yayi da gaske sannan ya turata taki sakesa ta wani kankamesa tace "Me yasa baxa ka bani hakkina ba, ko ni ba matar ka bace?" Da kyar yace "Sai ki jira ranan da kwanan ki ya xagayo..." Daga haka ya janyeta jikinsa, Kallonsa ta dinga yi babu ko kiftawa ta ji wani bakin ciki da takaici ya turnuketa, ya mike tsaye ya tsallake coffee din da yake sha ya nufi kofa ya fice daga parlon, da sauri ta bi sa taga dakin Jiddah ya nufa ya shiga ciki ya kulle, hawaye ya kawo idonta ta koma parlon da sauri ta xauna kan kujera tana watsi da throw pillows din kai, xaunawa Abuturrab yayi gefen gado na kusan minti uku trying to calm himself down, sai kuma ya juya ya kalli Jiddah da ke bacci, kashe wutan dakin yayi ya hau saman gadon ya cire duvet da ta rufe jikinta da shi a hankali yana kallonta fuskarta cikin duhun, lkci daya ta bude ido xata mike xaune da sauri ya kwantar da ita moving closer to her murya can kasa yace "Mata na bacci dama bata jira mijinta ba?" Sosai gabanta ya shiga faduwa ta marairaice masa tace "Bacci nake ji sosai don Allah ka sakeni" a hankali yace "To gaya min wa xan kama idan na sake ki? Wajen wa kike son in je" Shiru tayi xuciyarta na bugawa jin muryarsa kamar ba shi ba, wannan kalma da ya fada mata ya sa bata sake ce masa komai ba amma hakan bai sa jikinta ya daina bari ba tana sauke ajiyar xuciya, a xaton ta iyakarsa yanda yayi mata a Abuja jiya amma sai ta ga ba haka ba, jiya he was so calm and gentle, yau kuwa opposite din ne, Exactly yanda ta gansa a ranan da ya kawota gidansa take ganinsa yanxu, rikice masa tayi ta fara kuka iya karfinta tana ce masa ya rufa mata asiri yayi hakuri ya tafi wajen duk warce xai je, amma ko sauraronta bai yi ba, he was using all the scope Ahmad gave him but ferociously, he wasn't soft, it's just as if his life depends on what he was doing at that moment, duk wannan abun Aneesah na tsaye bakin kofar dakinta ta kasa shiga duk da babu wani abu da take ji amma kawai ta kasa shiga dakin nata tana jin kamar xata hadiyi xuciyarta ta mutu kawai, ihun da Jiddah ta kwala wanda duk wanda yaji irin ihun yasan na menene ya sa ta sulale kasa ta xauna nan bakin kofar nata ba tare da ta shirya yin hakan ba, Jiddah tana ji tana gani Abuturrab ya rabata da self-worth dinta na ya mace, an experience that will remain in her memory forever....





_Lagos laces, jewelries, Cotonou wrappers, shoes and bag all at affordable prices, siyan daya ko sari_


Location lagos state, ana kuma aikawa duk inda mutum yake.....
*tested and trusted*

If interested contact
=?G? 08052466875 via WhatsApp


Da kyar Jiddah ta bude idanuwanta da suka yi mata nauyi jin sanyi a forehead dinta, tana arba da Abuturrab da ya daura hannunsa a goshinta ta runtse idon tana son matsawa daga wajen amma ta kasa kwakkwaran motsi taji kamar anyi glueing dinta da gadon, duk da idanuwanta a rufe suke hakan bai hana hawaye sauka idon ba, ya dagota ya rungumeta gamm jikinsa ya ma rasa abinda xai ce mata, jin yanda hawayenta ke xuba jikinsa ya kai bakinsa fuskarta yana kissing tears din nata all over, cikin breaking voice yace "I love you wife, i love you, I am sorry for everything from the day i met u till this moment, i...." Kasa ci gaba yayi ya kwantar da ita ya hade goshinsa da nata, sae taji nasa hawayen na sauka fuskarta, a hankali yace "I am sorry Jiddah, i am sorry u have to pass through all this, i am sorry wife..." ita dai ba sosai take comprehending dinsa ba ma, gaba daya jin ko wani ga6a na jikinta take kamar ba nata ba, she is feeling pain everywhere, wani kuka ta sakar masa a galabaice tana juya kanta tace "Don girman Allah ka kai ni wajen Umma, wllh mutuwa xan yi" ya sake dagota ya rungumeta shi ma din duk a rikice yace "Plss don't say that again, I don't know how everything happen this way, I don't know what came over me" kuka kawai Jiddah take me ban tausayi, Abuturrab ya rasa me xai mata, yayi lallashin duniya amma kamar yana dada tunxurata, shi kuma bai fasa lallashin nata ba, from d way she is crying kasan she is pained, and he wish he can take away all the pains, kamar yanda bata yi bacci ba haka shi ma bai yi ba har karfe biyu da rabin dare, babu abinda ya kara daga masa hankali sae jin yanda jikinta yayi xafi lkci daya kamar garwashi, he couldn't help it anymore ya kwantar da ita ya fita dakin, bangarensa ya tafi don duba mata paracetamol amma bai gani ba, yayi duban duniya a bedroom din nasa babu paracetamol din, tunawa yayi ranan yace Aneesah ta dauka, does it mean she took all, da sauri ya fita daga bangaren nasa ya tafi dakin Aneesah, budewa yayi ya shiga ciki ya tadda fitilan dakin a kunne, a kwance take ta wani dunkunkune waje daya idonta tarrr kamar warce aka yi ma mutuwa hakan yasa yana bude kofar ta mike xaune kusan a firgice, sae da ya xaga dakin as if thinking of what to tell her, sai kuma ya dawo inda take kwance da sauri yace "The other day kin dauki pack din paracetamol a part dina, where is it?" Kallonsa kawai take don duk a birkice yake, jin tayi shiru???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? yyi mata tsawa yace "I am talking to u Aneesah" ta yi karfin halin cewa "Me zaka yi da paracetamol tsakar daren nan?" Ya daga mata murya yace "My wife is sick, ki tashi ki bani nace maki" Mikewa tayi da sauri cikin rawar baki tace "Ohh Subhanallah, me ya sameta, let me...." Sae kuma ta nufi kofa ya fixgota yana mata wani kallo yace "Ina xa ki?" Tace "Aa naji kace bata da lafiya, kuma ni paracetamol na shanye just 5 pieces ya rage, shine xan je in ga ko da abinda xan...." Ya katse ta yana kallonta da kyau yace "That's our secret, a PRECIOUS secret.... u are not invited" daga haka ya saketa ya nufi kofa ya fice, mutuwar tsaye tayi a wajen _Precious secret_ din da ya fada ne ke mata yawo a kai, wasu hawaye masu xafi suka xubo idonta lkci daya taji wani sanyi ya lullubeta ta hau saman gado da sauri ta ja bargo ta rufe jikinta da shi tana jin numfashinta na sama sama, All through the night Abuturrab na xaune gefen Jiddah da ta samu bacci ya dauketa, kana ganinta kasan she is restless even in sleep, a baccin ma duk a firgice take, a kan idonsa aka yi kiran sllhn farko, da ya kai hannu jikinta sai yaji xafin ya fi na da, he just don't understand the meaning of this, gaba daya hankalinsa ya tashi sosai, da da ynda xai yi da ya maido da duk wani ciwon da take ji jikinsa, lkcn sallah na yi ya shiga yayi alwala don tun daren yayi wanka, ya fita masallaci.... kasa nutsuwa yayi Azkar dinsa yayi a masallacin, he really need to talk to Ahmad, may be there was something he was suppose to have done da bai mata ba shi sa jikinta yyi xafi, yana dawowa gida ya tafi bangarensa ya dau wayarsa ya shiga kiran Ahmad bayan ya xauna saman kujera, Ahmad na dagawa sai da ya fara kyalkyala dariya kafin yace "Don't tell me baka san yanda xaka yi da ita ba kuma bayan ka cuci er mutane Captain?" Abuturrab yayi kasa da murya cike da damuwa yace "Plss tell me... asibiti xan kai ta? she is seriously sick Ahmad, why is that??" Ahmad yace "Ohh u are asking why is that, ita Aneesah ta maka haka?" Wani tsaki Abuturrab ya ja yace "Pls mu yi maganan da muke yi Ahmad" Ahmad yace "To ka ga, the different is clear" cike da damuwa Abuturrab yace "Yanxu asibitin xan kai ta plss?" Ahmad yace "Not at all, in dai yanda na fada maka ka bi babu xancen hospital, just lukewarm water and salt" Abuturrab yayi shiru, Ahmad yace "Yea, just it, she will feel better in sha Allah, when did it happen" Abuturrab yace "Yesterday" Ahmad yace "Yanxu sai da ka bari jikinta yayi tsami xaka kirani, it's something u should have done since that night Captain" Abuturrab ya sauke ajiyar xuciya yace "I will call u back" Daga haka ya katse wayar ya fita bangaren nasa ya shiga dakin Jiddah, tana nan a yanda ya bar ta kamar ma bata son motsa jikinta kwata kwata, ya shiga bandaki ya hada ruwan dumi sosai a bathtub, ya fito ya sauka downstairs, dubawan duniya yayi ma gishiri a kitchen bai gani ba, hakan ya sa ya haura sama ya shiga dakin Aneesah, tana nan dunkunkune cikin bargo har a lkcn, ya cire bargon yace "Aneesah" da kyar ta bude idonta da yayi mata nauyi don ana idar da sallan asuba ta samu bacci ya dauketa tun daren jiyan take rawan sanyi kamar xaxxabi xae rufeta, ga bacci ko barawo bai xiyarceta ba, wani nauyi taji kanta yayi mata, ba tare da ya wani damu da yanayinta ba yace "Sauko ki bani gishiri a kitchen, I can't find it" kallonsa kawai take, yayi mata tsawa yace "I'm talking to you Aneesah, gishiri xa ki bani" Ta koma ta kwanta a hankali tace "Babu shi" cikin fada yace "Gishirin xaki ce min babu? Da uban me kike girki a gidan??" ta kallesa tace "Ubana" wani mugun kallo yayi mata yace "Baki da amfani wllh, sae yanxu na sake tabbatar da haka" daga haka ya fice daga dakin, wani sara mata kanta yayi ta bi sa da kallo tana jin xuciyarta na mata wani xafin bala'i, Abuturrab na komawa dakin Jiddah ya nufeta ya xauna gefenta ya kai hannu goshinta a hankali yace "Jidderhh" a tsorace ta bude idonta, xai dagata xaune ta girgixa masa kai kawai don in tana kukan ma ji take ko ina na mata ciwo a jikinta, be saurareta ba ya dagata kamar newborn ya kai ta bandakin, safiyan nan Jiddah taga tarairaya da lallashi wajen Abuturrab, kamar dai ba Abuturrab ba, amma duk wannan bai dameta ba ta kanta take axaba da wahala ya isheta, ta maimaita masa ya kai ta gun Umma ya fi a kirga, daga baya kuma ta fara cewa ya kira mata Maimoon, shi dai kawai lallashinta yake, duk every minute yake kiran Ahmad ya tambayesa me xai mata she is still in pain, daga karshe karfe bakwai dot ya fita xai je nemo pharmacy a duk inda yake bayan Ahmad yayi masa prescribing drugs da xai siya mata, yana dawowa ya sameta tana bacci, ya ajiye ledan maganin ya fita duk fa Jiddah ta birkitasa, he just want to her to be fine, downstairs ya sauka ya shiga kitchen ya dinga neman Ashana ko lighter da xai kunna gas amma bai gani ba, ya fita ya tafi dakin Aneesah, tana kwance ta nemi baccin ta rasa tunda ya shigo ya tasheta daxu, A takaice yace "Ashana nake nema xan daura ruwan xafi yana ina??" Ta sauke idonta daga kallonsa tace "Babu ashana" a fusace yace "Wai ke wace irin macece komai kice babu? I always use to imagine ko rako mata kika yi duniya, komai zero zero.... abin alfaharin ma da ake kawowa gidan mijin shi ma big ZERO, there is nothing to write home about u Aneesah, what nonsense??" Yana gama fadin haka ya juya ya fice daga dakin a mugun fusace, Aneesah ta bi sa da kallo baki bude with so much shock, rufe fuskarta tayi da bargon jikinta wani sanyin na sake shigarta, yau ita Abuturrab ke gaya ma haka?? Abinda ko da wasa bai ta6a fada mata ba, Abuturrab na fita gun mai gadin gidan ya nufa, ko amsa gaisuwansa bai yi ba yace "Kana da Ashana??" Mai gadin yace "Wllh babu yallabai, dama maganin sauro nake kunnawa da Ashanar kuma tun da

92 / 117