Matar So 1 Complete Hausa Novel

Author :  M Shakur Category :  Romance

Chapter   63 / 64

186K to 189K   out of 190.6K words

Inda yayi kokarin barin kasar.

         ........

"Eh nine nasakawa Yunus Marafa, shi kuma kaninshine ya bani aikin."

         Basu kyale shi ba suka mishi lagalaga.
             Koda suka isa Abuja, kallon sunboy Minister yayi yace.
"Ku karya min ɗan iska, dan yasani kusan mutuwa da taimakon suwaye kake wannan aikin a filin jirgi."

        "Da taimakon ma'aikatan gurin wanda nake sayansu"

    "Ku karya min ɗan banza. Yau zamun kaishi kasar saudiya na dawo da ita, sai kuma Maganar Yunus marafa shima yanzun zamu je ofishin jakadancin china mu nime diyyar kashe shi da akayi ba tare da hakkinshi ba."
         ****
Shekara ɗaya baya........@lalaci ya kamani, 😹
[4/3, 7:56 PM] Addah Ramlah: Page.....11
       Shekara ɗaya baya, da alkali ya yanke hukuncinsu Yunus. Za'a kaisu inda ake gabatar da hukuncin. Toh a lokacin kungiyar siyasan da take gudanar da mulki tana fuskarta barazana daga wata kungiya wanda har take zargin party mai mulki tana kashe mutanen da basuji basu gani ba, dan haka suna kira da alummar china su juyawa wancar party mai mulki baya, a zaɓe su.

       Abin da ya kawo ruɗani kenan a ɓangaren siyasar kasar sai aka dakatar da duk wani hukuncin kisaa, aka ajiyesu.
               Toh a cikin haka aka manta da case ɗin Yunus aka kaishi wani mugun gidan Yari, wanda akayi ta axabtar dasu.
   Yafice hayacinshi, ya lalace
Idan ka ganshi matukar baka yi dagske ba toh xaka shiga ruɗani.
        Dan yayi baki ya jeme.
          Kullum kasame shi yana istigifari, dan yasan hakkinmu ke binshi. Matsalar gurin shi baya jin yarensu su basa jin English sai ya ajiye haka A matsayin k'addarar shi. Koda mutuwa yayi yana fata Allah ya yafe mishi hakkinmu.

               *****
    A zaria kuwa Mama kilishi ce ta yanki jiki ta zuɓe sakamakon jin abinda Sulaiman ya aikata, koda ta farka. Zatayi magana hajiya ta rufe mata baki.
    "Haba Rukayya sai kace baki san k'addara ba, wannan aikin shaiɗane, kuma nayi imani da Allah Makahon sone da tausayi yasa Sulaiman ya aikata haka, tunda kowa yasan Yanda Babangida ya zalunci maryam, wallahi bani da haufi akan shi dan nasan duk inda yake nadama yana tare da shi, ki mishi addu'ar niman shirya karki yarda zuciya takaiki ta baroki."

     Mai da kai Mama tayi tare da zubda kwalla sabida bakin cikin abinda ɗanta ya aikata.

                 ****
   A lokacin guda aka kafa kwamintin lura da abinda ya sami Yunus inda suke tattaunawa da jakadar china, kwamitin yar minister aka kafa zuwa saudiya,
        Na Yunus kuwa har da Alhajinshi wanda aka mishi kiran gaggawa. Da zai tafi bai tafi shi ɗaya ba sai da ya ɗauki Aman da Ahmad.

         Sosai maza suka murza gashin baki da tattaunawa mai zafi inda aka koma har kaduna aka duba cameransu,  aka koma samo vedion. Ba'a ɓata lokaci ba aka wucce china.
   
           ****
Ina can hankalina a tashe, bana ko iya magana. Yaran kuwa suma sai abin ya taɓasu basu da kuzari. Suma sai suka koma gefe guda, suna kallona. Sabida rashin walwalana, na kasa basu farin cikinda nake basu kullum. Toh yanzun bana iya basu. 
      "Wai kina nufin haka zaki shiga hakkin Yaran da basu da laifi, miye laifinsu da baza'a basu abincinsu ba, karfi da yaji zaki maida yara marayun dole, idan kuma kin yayesu ne toh ki faɗa mana." tana gama faɗar haka tayi taficce waje abinta.
            Mikawa Hassan hannun nayi idanuna cike da kwalla, nace.
"Ba laifina bane, soyayyar Mahaifinkune bazata taɓa barina na rayu da kowa ba sai, shi."
          Ciro mishi nono nayi na mika mishi, kauda kanshi yayi yana kallon ɗan uwanshi, kama bakin nono yayi ya gatsa min cizo, wanda yasani runtsa idanuna sai da kwalla suka zubo dama suna cike a idanun.
         Dariya yayi ya kalli ɗan uwan wanda yazo da sauri ya kama rigana, nifa Yarana basu da wayo dan basu iya ciro nono a riga ba sai dai na ɗaga musu.
  Ganin zasu zuke ni nayi maza na kwace kaina ina musu dariya nace.
"Bari na baku tea."
   Mikewa nayi na ɗauki feeder ɗinsu na wanke sannan na haɗo musu tea ɗinsu na mikawa kowane.
Jifa da feeder Hassan yayi, ya tsalla ihu har sai da Mama ta shigo.
Ganin feeder a kasa yasata ɗaukarshi suka fita, Damo sarkin dawowa jikina yayi ya kwanta ya cigaba da shan abinshi. Ina shafa bayanshi, ni kaɗai ina zancen zuci.
   "Ina Yau da Yunus zai dawo, yaga yaranshi ya kaunacesu ya so su kamar Yanda yake fatar samunsu, I love my Man"
     A gaskiya Yunus ya shammaci zuciyata, fiyye da kima. Baxan iya son wani namijin bayan shi ba, dan sonshi daban yake, a zuciyata.
"Ya Allah kai kafini sanin sirrin sarari da boye Ubangiji ga shigo Al'amarina."

               Haka nayita addu'a....
    *****
Kwanansu Alhaji huɗu a china suna bin gidajen Yari, sai da suka kwana goma sha ɗaya sannan sukayi katari da wani gidan yarin dake can iyakar china da Japan.
   Anan aka samishi a gigice sai dai Karfin Ibada ya hanashi ɗimauta dan azaba ake musu, cikin dare a sake musu wasu mugayen ɓeraye suyita cizonsu.

       Yunu yaga Jarabawa, amma dukda haka yarda da Allah da karfin imani ya hana aga tashin hankali sai dai, a jikinshi wanda ya kare da wasu cututtuka da cizon ɓerayen nan.

   Yana sallah walaha, aka buga kofarshi bai amsa ba sai da suka shigo, lokacin yayi sallama, ya kallesu masu tsaron gidan yarine yana da labarin luwaɗi suke da firsunoni, har a kusadashi anyi abun ɗakin dake gabanshi suka shiga sukayi da wani.
     Dake Allah ya kare shi, basu taɓa yunkurin taɓashi ba. Saima wani kwarjini da yayi musu, akan wannan abun.

          Nuna mishi kofa sukayi ya fita a hankali mutum mai kuzari da haiba ya koma tafiyar kamar ana turashi, har indasu Aman suke jira nan aka kaishi.
           Fuskarshi nan ta haɗa, gashi baka ganin komi sai hanci da baki.
            Kafin ya iso Ahmad ya tare shi, rungume juna sukayi tare da fashewa da kuka, Alhaji kam bai iya magana ba, sai kallonshi yake yanda ya koma.
     Murmushi yayi yana buga Bayan Ahmad yace.
"Haba Mazaje kace yanzun ka koma mataye."
  Janye jiki Ahmad yayi Aman ya kalleshi sai kuka komawa gefe yayi, ya zauna yana kuka. Gaban Alhaji yaje ya durkusa tare da dafe gwiwar Alhaji cikin sanyi rai yace.
"Alhaji ! hakkin maryam yaki barina na huta."
       Shafa kanshi Alhaji yayi yace.
"Maryam ta yafe maka tuntuni, sai dai kanime Yafiyar Ubangiji, Zamanka a nan k'addara ce, da taimakon ɗan uwanka. Sabida soyayyar dayakewa Maryam wanda kai ka gaza mata, shi kuma yana jin zai iya bata abinda kai kagaza bata shine yasashi aikata haka, amma koma miye Allah ya yafe mana baki ɗaya."

      Kuka Yunus yasaka sosai, tare da rike hannun alhaji. Takardu aka kawo Ahmad ya cika komi sannan suka mikar dashi.
        Daga nan basu tsaya ko ina ba sai asibiti, nan aka shiga duba shi. Sosai tare da bashi kulawa.

              Sai da suka kwashi sati kusan uku, sannan suka tattaro zuwa kaduna. Koda suka iso zaria aka wucce dashi tun a can yake son tambayar maryam amma ya gaza cewa komi, suma kuma sunki ce masa komi.

              Sun isa zaria da karfe biyu na rana yan uwanshi da danginshi duk suka mishi kawanya, suna kukan farin ciki murmushi yake ya kalli wannan ya kalli wannan.

           Da misalin karfe biyar su Ahmad suka dawo, kaduna.
             Ahmad ya ajiye Aman a gida, shima ya wucce gidanshi.
   Yana shiga yasami Hindu a falo ta zabga tagumi zama yayi kusada ita yace.
"Lafiya kike tunani."
          Mika mishi wayarta tayi tare da fashewa da kuka tace.
"Aman bansan ya akayi ba wasu suka ɗauki hotona suna, rubutun ɓatanci a kaina."

    Murmushi yayi sannan yace.
"Toh ai sai ki godewa Allah tunda baki yi abinda ake magana a kai ba, hmm abinda nake gudu kenan kin lalata gidanki kin lalata rayuwarki, idan kinga zaki iya ki gyara idan bai miki ba, kinsan dai bake ɗaya bace."
   Yana gama faɗar haka ya mike zuwa ɗakinshi yayi wanka, ya sauya kayanshi ya nufi gidan Mamie dan har yanzun yaki yarda Rahilah ta dawo gidanshi,gani yake hindu zata iya kashe masa mata da ɗanshi.

               Koda ya isa gidan yasame su a kitchen suna aiki da mamie sai hira suke, abinsu ga Sayeed da yake fama da kekenshi.

         Yaron naganin Baban shi yace.
"Papaaaa"
Da gudu yazo kan uban ya ɗagashi sama. Yana jijjigashi sannan ya sumbaci goshinsa yace.
"Mr Mandara faɗa min, miye Mominka da Mamie suka ce."
   Dariya yayi ya shiga shirme abinshi, cikin nutsuwa ya gaida Mamie tayi mishi barka da arzikin dawowan Yunus, wani kallo yabi Rahilah dashi sannan ya wucce falon Mahaifinshi nan suka tattauna sannan yafito ya shige sider ɗinshi. Bayan yabar Sayeed a gurin  takwaranshi.

            "Tashi kije, kinyi amfani da abubuwan da nabaki ko."
    Kan rahilah a sunkuye ta gyaɗa mata.
   "Toh maza jeki Allah ya baku xaman lafiya."
   Da sauri tafita, tana murmushi.
      A ɗakinshi tasame shi ya kwanta, yana ganinta ya mike zaune ya buɗe mata hannunshi.
         Shigewa jikinshi tayi, tana sauke a jiyar zuciya tace.
"Papa nayi miss ɗinka, kwanakin da kayi kaman nayi hauka."

   Murmushi yayi sannan yace.
"Ai abubuwan ne sai a hankali kuma bama son mu dawo da Yunus a yanda muka same shin nan kar Yar uwanku tace batayi."
      D'ago kai tayi tana shafa fuskarshi cikin salonta tace.
"A duniya babu namijin da zai iya samun maryam Sajida ta bashi soyayyarda tabawa Yunus ko yaya kuka kawo mata shi zata amshe shi hannu biyu."
        Zuge zip ɗinta yayi ta kalli cikin idanunshi,  hmm tace a rainta jaraba an dawo.
             Shafin soyayyar Aman da Rahilah ai ba sauki.

    ....... Haka ma ya faru a gidan Ahmad tunda ya shiga ya sami Rahimah, ta bashi abinci yaci kaɗan yace.
"Nifa ba wannan yunwar nake ji ba."
        Tun da ya faɗi haka, san abinda yake nufi lallaɓa yaranta tayi Ta kunna musu tap suna game, rufe kofar kitchin tayi sannan ta koma ɗakinta ta gyara jiknta tabi Ahmad. Jirgin soyayyar suma suka haye.

           ****
Haka kawai aka sani a gaba da maganin mata, tun bayan komawar Aunty Gausiya aka shiga ɗura min magani,  ga Mai gyaran jiki, kullum sai tazo an gyara min, kai an buwayi rayuwata gabaki ɗaya.
     Kamar na fasa ihu haka nake ji.
            Sai da aka samu kusan wata biyu ana abu ɗaya, ranar jumma'a na tafi makaranta, na shigo a gajiye, na shaki kamshin da ya kusan tarwatsa min zuciyata, a hankali na shiga gidan banga alaman komi ba, yaran ma ba ji, hayaniyarsu ba. Ɗakinmu na wucce nayi wanka na kwanta dan yau nake tsamanin bakona zai ɗauke,

                 Can wajen magarib sai ga yaran a guje sun shiga ɗakin Umma bana nan suka leka na Mama ma haka, shine suka shigo ɗakinmu. Suka zuɓe a kaina kallonsu nayi, nace.
"Yaran Mamansu ina kuka je."
      Jan hannuna sukayi da na mike, dole nasaka hijab na bisu, har falon baki.
       Anan zuciyata ta tsinke, sabida kamshin Yunus, a hankali na shiga ciki yana tsaye jikin window dake kallon harabar waje. Gani nake kaman gizo yake min, kallon yaran nayi da suka isa gurinshi da gudu suna cewa.
"Dadyy." dan haka nake faɗa musu daddy duk namiji daddyne.
       Juyowa yayi, ya durkusa a gabansu yana shafa fuskarsu.
          Mutuwar tsaye nayi, ina kallon Yunus,, ɗago kanshi yayi ya kalle ni, murmushi yayi sannan ya mike, tare da ɗaukarsu duk biyu, ya iso gabana. Ja da baya nayi har muka kure bangon ɗakin, rungume mu yayi baki ɗaya.
      Muryanshi can kasa yace.
"Duk nawa ne wannan."
          Kukan da nake haɗiyewa ne na sake, a hankali tare da gyaɗa mishi kaina nace.
"Duk nakane har da Mahaifiyarsu."
                  Sauke yaran yayi ya ciro chocolet ya mika musu yace.
"Maxa ku kaiwa Umma tasha."

  Suna fita, ya tallabi fuskana da hannunshi, yace.
"Maryam sai kuma kika ji labarin na mutu."
           Janye hannunshi nayi, nakifa kaina a kirjinshi ina kuka, bani da wani bakin magana, kallonshi nake ina shafa fuskarshi nace.
"Ai ban yarda ka mutu ba, dan zuciyata bata aminta da haka ba,"
"  Nidai abinda nasani shine, na shiga garari adalilin rashinka kuma da nace zaka dawo karyatani akayi ana min kallon na haukace. Daddy kaine cikon rayuwata, bansan ina sonka ba sai da kayi nisa dainda nake nasan cewa kaine rayuwata."
Rungume ni yayi kamar wani zai kwace ni.

        Mun jema sosai a haka, kafin yace.
"Maryam zaki iya zama dani kuwa, kinga yanda na koma fa?"
      Murmushi nayi nace.
"Yunus nake so ba wani ba, dan haka ni bani da damuwa ina son Haske rayuwata haka."
           Haɗa fuskarmu yayi, yana goga hancina da nashi. Yace.
"Maryam zan wucce dake gida, ins kewarki sosai."
           ɗaga kaina nayi, ina murmushi nace.
"A'a kabari dai su umma su maidani da kansu."
                 "Toh ki barni mu gaisa a nan."
        "A'a baza'a kuma dani ba ga nifa ma ina hutun sallah."
         Na faɗi haka ne dan ya kyale ni wallahi bazan iya jaraba ba.
         "Toh taimaka ki min wani abu."
  Kaman ban fahimce mi yake nufi ba nace.
"Dame fa, Yunus."
    Jan bakina yayi yace.
"Yanzun zaki gani."
   Hannunshi ya tura a rigar nayi maza na rike nace.
"Karka taɓa amanar H² kaga babu daɗi na bari a ci amanansu."
   Dariya yayi dakyar na lallaɓashi muka rabu lafiya.

  .......Tunda ya dawo kullum yana, zarya a gidanmu sannan ya kwashi yaranshi su tafi yawo, ina fama kintsa kayanmu da zan koma, dan yace ya dawo da sauran matanshi Saura nice.
         Sosai Umma da Mama da Rahilah suke haɗa min zafi, sai da na fara fita hayacina dan maganin karfine dasu, wasu wanda Rahimah takawo min daga, turaren tsuguno daga India Uwar mijinta ta kawo mata, sai wani na sha, haka kawai suka sani jin desires ɗin dole.

      Ranar jumma'a aka mai dani ɗakina nida Yarana,

   Bayan tafiyarsu Aunty Hamdiya, shima ya shigo, ya taramu a falo mu huɗu sai Yaran da suka haye mishi jiki, Balkisu da Fareeda na dariya, ina gefen Aneesah wacce har yanzun bata nutsu ba.
   Nasiha yayi mana akan zamanmu na baya da kuma kurakuran da ya aikata, ya rokemu da mu yafe mishi. Sannan yace za'a raba kwanaki ɗa'ɗaya, sannan ya kara da cewa.
   "Maryam Idan baki manta ba, kinyiwa Fareeda da Balkisu alkawarin basu..."
         "Ai dama Yaransu ne, dan ko da ake maganar auren Sulaiman niyyata na yayesu, na mika musu. Sune iyayensu ni bani da haufi na barnusu Yaran duniya da lahira."

         "Madalla da samun mace tagari kuma nagartacciya, mai zuciyar zinari, Allah ya albarkaci rayuwarki."
    Kallon Fareeda nayi cike da tausayinta, dama kuma yaran sukan je gurinta ko tazo ta ɗaukesu, balkisu kuma bata wata guda, bata zo kaduna dubasu ba,dan haka suna gaba tsalle a jikin Uban suka koma kansu.
    Hassan da barna ya tsikawa Balkisu ɗan abin wuyarta ta gwal, murmushi tayi ta sumbaci goshinsa tace.
"Wata rana zaka saya min sama da wanda ka tsinka."
Taɓe bakina nayi na zubawa mijina ido, ina wani lumshe su. Duk abinda nake yana gani, amma dan a zauna lafiya bai wani damu ba asalima jaddada mana zaman lafiya yayi kafin aka kawo abinci  wanda Fareeda ta girka, muka ci.

    Allah sarki huda na makaranta kamar tayi tsuntsuwa, a wannan shekaran zata gama. Mufeeda kuma tana gabansu hajiya yarinyar ta nutsu.

           ****
Yau wata biyu kenan da akayi wani kazamin hatsari a hanyar yola, kowa ansami danginshi amma banda sulaiman, karshe saka hotonshi akayi a network news, anan Alhaji yaganshi.

      Tunda Mama kilishi ta ganshi zata mike Alhaji ya maida ita, yace.
"Na yarda da tarbiyan da nabawa Yarana shaiɗan ne ya shiga rayuwarshi, ki yafe mishi Allah zai sassauta mishi bari gobe ns kira Yunus da abokanshi su tafi yolan.""

   Kuka tasaka tace.
"Wallahi na yafe mishi ina mamakin halayarshine, amma ya wucce."

   
        Lallaɓa ta yayi, har suka kwanta.
       .......A bangarenmu kuwa ban san iya adadin lokacin da muka ɓata muna hira inda yske bamu labarin rayuwar gidan kaso ba, sai da na shafa wayata, naga karfe biyu saura, mikewa nayi nace.
"Bayin Allah da alkhairi."
     Na wucce sama, dariya Balkisu tayi tace. 
    "Fareeda nima na gudu, dan nan gaba Maryam kuka da tasaka mana mun riƙe mata miji."

              Dukkansu suka miƙe suka hauro sama, shi kuma ya shige ɗakinshi yayi wanka. Sosai sannan yasaka kayan barci ya fito ya kashe komi na gidan, ya hauro sama.
      Ya shigo yasame ni, nayi wanka na kwanta, kunna wutar d'akin yayi yazo har inda nake.
          
           "Ya muna hira kika gudu?"
       "Hiran ce ba karewa zata yi ba, kuma ai sai a bani mijina, tunda ka jima da dawo dasu, nima sai a barni na mori mijina ko."

           Janyoni yayi na shige jikinshi,

63 / 64