Matar So 1 Complete Hausa Novel

Author :  M Shakur Category :  Romance

Chapter   58 / 64

171K to 174K   out of 190.6K words

baka taɓa tsamanin ba, mi yasa bazaka rabu dani ba? Mi yasa bazaka fita a rayuwata ba? Nifa bana sonka bana kaunarka, don Allah ka kyaleni."

Ina gama faɗar haka na mike nabarshi a gurin ko magana naki bashi damar yi min.

Zaman dirshan yayi ya kama kanshi da hannunsa duk biyu. Ina fita ɗakin Mama na wacce, na kwanta har lokacin jikina da numfashi na basu daidaita ba.
Dakyar yaja kafarshi ya fita a gidanmu duk sun tafi, koda ya shiga motarshi kifa kanshi yayi tare da sauke kwalla masu zafi. Mi ya aikeshi aikata abinda zai zame mashi tashin hankali.

Kamfaninsu ya wucce a gigice, yayi parking. Yana shiga gurinsu Ahmad ya zube musu akan kujera tare da dafe goshinsa yace.
"Ku taimaka min, zasu rabani da matata."
A tsorace suka ɗago kai tare da cewa "kamar Ya?"

Zama yayi ya shiga basu labarin abinda ya aikata da irin hukuncin da...

"Alhamdulillah, karshen tafiyarmu tazo yunus, nasan ban kaika samu da kuma buɗi ba, amma na hakura duk wani haɗakar dake tsakaninmu zan cire kaje ka zauna da Aneesah da ta baka shawaran sannan ita kuma maryam Allah yakarɓa mata sakinta a hannunka taje ta auri wani, ashe duk hiran da mukayi ka zauna kabugi cikina ne, lallai kayi kuskure ni ko sau dubu Rahilah zata haifa min yarana ina so, kuma bazan taɓa gajiya da ita ba, ada dan matsalata na aureta a yanzun kuma dan ta zame min wani yankin rayuwata ce, koda wasa bazanyi kuskure rabuwa da ita ba ko kuma naja dalilin da zasu rabani da ita ba, yayi maka kyau."

Inji Aman, yana gama faɗar haka ya tattara kayanshi yabar ofishinsu baki ɗaya.
Bakin ciki ya hana Ahmad magana, kayanshi ya haɗa ya bar Yunus shi ɗaya. A ofishin duniya tayi mishi zafi kowa ya juya mishi baya, ji yake kaman ya haɗiye ranshi ya huta amma ba halin haka..

Daga zaria kullum sai Alhaji ya buga mishi waya akan sakin, ga Hajiya ma da ta sakashi gaba. Mama kilishi ce take kulawa da lamarinshi idan akwai.
Idan yaje gurin aiki ba kowa a ofishinsu sai shi ɗaya, duk su Aman sun daina zuwa, sai dai yaje shashin ma'aikata yayita kallon yanda kowa ke farin ciki, da walwala, toh.mi yasa shi baida farin cikin mi yasa ya rusa nashi farin cikin. Yana cikin ɗimuwa,

****
Tsautsayi ya rufta da Aneesah, suna cikin aikinsu tare da abokiyar aikinta wacce take cikin damuwa, kallonta Aneesah tayi sannan tace.
"Rita mike damunki, naga kwanan nan kina shiga damuwa."
Juya kujeranta rita tayi cikin cunkushewar fuska, tace.
"Bari kawai Neesah, kinsan mahaifina sojane toh burinshi na auri soja irinshi, ba'a bukatar naja miki labarin. Yanzun dai sojan da ya nima min, zan aura shine muka ɗanyi making love da shi, tsautsayi yasa bamu saka goldenring ba, yanzun ina da cikin 2month na rasa yanda zanyi da cikin dan a coci ɗinsu Papa ba'ayarda da ka amshi cikin da za'ayishi daga waje ba yankan zama masifa da bala'i a cikin family da society."

Dariya Aneesah tayi sosai, sannan ta kalleta tace.
"Yanzun sabida Allah sabida ɗan karamin cikin da kika ɗauka shine kika jefa kanki cikin damuwa yo Allah na tuba ina zan saka damuwa a raina, ciki ko na wata nawa ne zan iya cire shi ba tare da nayi nazarin ya zanyi dashi ba, idan kin shirya muje na kaiki a cire miki."

Kamar rita ta fasa ihu dan murna, ana tashi a bankinsu suka suri jakarsu sai Rigasa.

Koda suka isa, dr nacan yana aikiwa wata sai ihu take sabida burge mata cikin da yake.
Suna zaune yafito sharfan da zuba hankalinshi tashe, ya nufi ofishinsa ya kira nurse aka fito da Yarinyar da aka burge mata ciki kamar matacciya, dake da uwarta suka zo nan ta riƙeta suka fita,
Yana zaune ya dae goshinsa kimanin sati huɗu knn tun da yake fama da ɗimauta da zaran yaje cire cikin da aka zo zubdawa sai ya saka injin ɗin yayita aiki fiyye da kima yana ganin jini na gudu a jikin macen.

Koda su Aneesah suka shiga ɗakin kallonta yayi cikin fara a yace.
"Madam barka da zuwa, ya aiki."
Yatsina fuska tayi tace.
"Ga aiki nan, amma ina ganin allura za'a mata, dan ni bana son wannan burge cikin allura yafi sauki."
"Ok ba damuwa bari nakira nurse tayi mata kinsan kuɗin alluran dai 25k ne."

Kuɗin ri ta ciro tabashi, kiran norse yayi a waya can sai gata. Faɗa mata abinda zatayi yayi taje tazo da alluran, tayiwa rita sannan sukayi godiya suka tafi.

Babban Rita babban sojane anan kaduna,Yaransa maza huɗu sai rita mace ɗaya tal jida ita yake kamar rai ɗaya.

Koda ta koma gida, ɗakinta ta shige, takwanta sabida yanda cikinta yake ciwo. Har dare bata fito ba dakanshi ya shiga ɗakin ya sameta kwance cikinta ya kumbura, ga jinin dake fita ta hancinta da bakinta.

Kiran yayan ritar yayi Nike, yana shigowa ya cincinɓeta sai waje aka fita da ita sai cikin mota, inda suka nufi asibiti.

Dakyar aka amshesu sai da mahaifinta ya fida id card ɗinsa na babban soja suka karɓeta.

Nan likitoti suka shiga aikinsu tun takwas har karfe biyun dare sannan suka fito da ita, aka kaita ɗakin yan ɓari.
Bin bayansu Babanta yayi har aka sauya mata gado, kuma zuwa lokacin jini bai daina zuba ba, bayan fitar wanda suka kawota tabuɗe idanunta cikin wahala tace.
"Am sorry Papa, naci amanar tarbiyan da kaimin, gashi nayo ciki a waje wai dan karka sani naje zubdawa ashe nice zan mutu."

"Wani likitane yayi miki wannan alluran?"
Dakyar ta iya buɗar bakinta tace.
"Kawata Anee."

Jinin ne ya fara zuwa ta baki tana amayar dashi, tun tanayi.a hankali yar yaci karfinta karshe dai Rai yayi halinsa.

A kiɗime Uban ya fasa ihu. Yana kiranta.

D'ago kanshi yayi idanunshi, yana kallon Yayanta, jikinshi na rawa tsimin sojar ta motsa. Nurse aka kira suka rufe gawarta, aka kai inda ake ajiye gawa.

Gida suka komo, uwarta da suka faɗa mata mutuwar Rita ihu take tana dukar kirjinta.
Washi gari Aneesah ta nufi bankinsu, tun kafin ta isa taga yanda sojoji suke cin uban ma'aikata ana nima Anee. Tana zuwa gurin suka taso mata a gadarance tafito makale da id card ɗinta.

...... Tana fitowa suka kalle id card ɗin, aikuwa cikin hargagi suka ce ga Anee ɗin. Wani basamuden cikinsu yace.
"Kece kawar Rita Uchenna."
Jikinta narawa tace.
"Eh"
"Ok muje kace ubanka."

Suka tasa keyarta cikin motarsu, sai barrack suna kaita aka turata wani ɗaki inda aka zuba kartin mata sojoji, rufe da fuskarsu aka buɗe mata hayaki maisa tari da kwalla bayan cin ubanta da suke da bulala. Ta ko ina suke zaneta sai da suka mata likis sannan Baban rita ya shigo ya kalli yanda ta koma zama yayi cikin zafin rai yace.
"Zaki faɗa min, inda akawa Yarinyata allura ta mutu."

A firgice ta mike zaune tare da dafe kirjinta ta fashe da kuka,tace.
"Ritaaaaa! Ce ta mutu, wayyo Allah na shiga uku wallahi bansan zata mutu ba, ce min tayi tana da ciki kuma bata son ta ɓata maka rai shine nace akwai inda nasani ana cire cikin, shiɓe tace na kaita wallahi Papa bansan zata mutu ba,da nasani bazan fara zama sanadin mutuwarta ba."

Mikewa yayi yace.
"Kufito da ita muje asibitin."
Kamar kayan wanki aka suka kwasota aka watsata a hilux, har rigasa suka isa, lokacin ana wani tashin hankali, dr yaje cire ciki wata budurwa ta mutu, shine abin ya zama rikici har da yan sanda. Ana cikin wannan sai ga su Aneesah.

Nuna musu dr tayi gyaɗa kai Baban rita yayi take sojoji suka sauka, har inda yake suka rufeshi da mugun duka, tare da nurse.

Dukanshi suke tun yana ihu har ya daina, haka suka masa mugun duka suka kuma jefashi cikin mota aka wucce da shi barrack.

.......
Duk wanda yaga yanda na koma sai ya sake kallona, dan gyarani mamah amarya take tare da min nasiha akan hakuri nayi kiba daidai misali.
Kullum sai daddy yazo nikuwa naki zuwa, idan suka ga van fita ba sai su fara min faɗa, ni kuwa sai naje kofar gida nayi zamana a ɗan barandar malam, dake gurin a kewaye yake gurin idan na zauna bana gurin sai naji tashin motarsa nake fitowa.

****
Zaune yake shida Huda ya zuba tagumi, cikin damuwa tace.
"Daddy kayi hakuri, Aunty Mom zata sauko. Dole tayi fushi amma kayi hakuri."

Murmushi yayi sannan ya mike yace.
"Ba damuwa."

Haka yabar makarantar zuwa masaukinshi,
Washi gari ya nufi kaduna inda ya samu muguwar labarin abinda ya sami Aneesah.

Nan aka tashiga da fita, iyayensu dashi kanshi, da farko sunbi baban rita cikin ruwan sanyi, ya nuna musu karfin kakinshi shine su kuma suka nuna mishi karfin kuɗi da sanaya, inda aka shiga aka fita karshe haka juya case ɗin kan Dr. Ita kuma akace shawara aka nima a gurinta ta bayar kuma bata da laifi.

Sai dai tunda ta dawo, itama ta shiga firgici sabida mafarkan da take, wani lokacin idanunta biyu zatana ganin jini, yana gudu ko kukan babys. Lokaci guda ta sambatu da ihu.

"Wayyo dasu nan zasu shige min jiki." sai aka ɗauka ko zafin bugun da tasha ne. Amna da suka sami labarin halin da Yunus yake ciki take suka mike da niman taimako,

Na yunus ya haɗu masa da zafin tashin hankali da yake ciki. Karshe sai da balkisu tayi magana da su hajiya aka maidashi zaria.
Dan kamar zai haukace, koda maganar yazo min taɓe bakina nayi nace.
"Allah ya kyauta nima haka suka hanani farin cikina can da yawarsu."

......... Dr kuwa asibitinshi ranar gwanati ta kwace, inda aka shiga ciki aka samu abin mamaki, wani gurin da yake tara, ɗiyoyin da yake cirewa a cikin mata, yana bawa wani katon karen tsafinshi yana cinsu. Ganin girman kare, yasa jami'an tsaro suka juya da baya, karshe suka cinnawa asibitin wuta.

Yana can ya fasa ihu, tare da zabura da karyayyan kafarshi. Yana yaga rigar jikinshi. A bangaren nurse kuwa ba'a cewa komi.
****
Addu'a malam sa'idu yayi ya mikawa Alhaji, aka saka mishi abaki dakyar yasha tare da cewa.
"Don Allah karku rabani da ita."

"Bazamu rabaka da ita ba, ta lafiyarka muke." Inji Malam.

Shiru sukayi Aman da yazo har zarian ya rikeshi tare da Sulaiman. Kwantae da shi sukayi,
Ya rike hannun Sulaiman.
Cikin raunaniyar murya yace.
"Karka rabani da ita don Allah, dan uwana."

"Bazan rabaka da maryam ba, tunda kana son abarka."

Yana gama faɗar haka ya fita a gidan, motarshi ya shiga tare da kifa kanshi. A jikin sitiyerin yana magana cikin damuwa. Yace.
"Wannan wata irin kaddara ce haka? Mi yasa suka min haka? Ni na dace da Maryama nina fara ganinta, amma suka ɗauketa suka m bawa wanda bai san kimarta ba mi yasa bazasu min adalci ba, su gane cewa nina dace da ita."

Haka yayita surutunshi a gurin.

****
Bayan yan kwanaki gane ganen da Yunus yake yanzun ya daina, sai dai damuwar da yake cikin ranshi a kaina, a ynz su Hajiya sun janye maganar saki sunce yayi kokarin mun daidaita.
A cikin kwanakin ya dawo kaduna, inda ya cigaba da zuwa gidanmu ni kuma ina surfa mishi rashin mutunci dan banajin zan iya hakuri da abinda yayi min, ina zaune a tsakar gida, yaron makotanmu ya shigo wai.
"Baban Huda yana sallama da maryam"

D'if na ɗauke wuta nayi banza da yaron na cigaba da chtt ɗina, sai da Umma ta leko cikin faɗa tace.
"Allah ya shiryeki ynx mutum yayi magana malam yace ana k'inki toh tashi mara kirki ki shigo dashi falon baki."
Tura bakina nayi cikin jin haushi nace.
"Wallahi nikam bazan koma gidanshi ba, gwara ya daina zuwa min. Mutum sai kace mayye."

Kwalllll naji an kwaɗa min abu a goshina aikuwa na fasa ihu wanda sai da Mama ta gintse addu'ar da take tafito ganina dafe da goshina yasata cewa.
"Kaiii Maryam, dalla kimana shiru sai kace an yanki da wuka. Dalla saka hijab kije ki shigo dashi."

Figar hijab ɗin nayi, cikin kuka na fita. Nafita har waje yana jingine da mota, babu sallama cikin masifa nace mishi.
"Yau zaka sallame ni dan nagaji da zama da aurenka, idan kuma jikina kake bukata toh wallahi sai dai ka mutu, idan yayi maka kashigo dan kasan Iyayena kima ne dasu, da sanin darajan bakonsu tunda sunsan darajar kansu."

............Chaiiiiiiiii
[4/3, 7:56 PM] Addah Ramlah: 🌹🌹🍀
*MATAR SO*
🌷🌷🌻

*MAI_DAMBU*
*Wattpad:Mai_Dambu.*

Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai....

Sadaukarwa Ga Mai Nasara Team😂



*BOOK 2👈*
*Page....6*
Bakinta na rawa jikinta ma, haka ta kalle shi tace.
"Fatric kana nufin zubda cikin ma akwai hakkin Raiiii?."
"Kwarai da gaske ai kunso kankune duk abinda Allah ya baka yasan da zamanshi da wamzuwarshi, mufa bambancin dake tsakaninmu daku shine matukar akace Yesu yace kar muyi kaza bazamu taɓa yi ba, amma ku musulmai idan aka Allah yace Annabi yace sai kiga mutane suka famkama dan ko sunyi laifin sun dogara da Allah na yafe musu dan ku alummar Annabin karshe ne, kuma duk ba haka bane sonkai da son zuciya ke buwayar, karki ce ina ci miki fuska haka bane iyakar gaskiya na faɗa miki, kuma ina jajjanta miki rasuwar ɗanki."

Goge kwallar dake bin fuskarta tayi, sannan ta mike tare da cewa.
"Nagode."
Ta fita a officer ɗin tausayinta ne ya rufe shi, sosai.
****
Ina kwance a falon Hajiya dan tun safe aka sallamo ni,ina bin suratu ankabu naji sallamar Sulaiman, mikewa nayi naja hijab ɗina na rufe, jin na amsa mishi nace.
"Shigo Baban Arif."
Ya shigo fuskar shi a sake, ya nemi kujera ya zauna. Shiru mukayi dan shima ɗin wani miskiline amma ba irin ɗan uwanshi, yace.
"Kina bukatar wani abune?"
Jim nayi ina nazarin abinda raina ke so, zaro wayarshi yayi a aljuhu ya fara latselatse, sake ɗago kai yayi yaga har lokacin kaina a sunkuye, gyara murya yayi. D'aga kaina nayi nace.
"Babu sai ko masara gashashe."

"Bayan shifa?"
"A'a babu komi."
"Ok"
Yasa kai ya fita can bayan wasu mintoti sai gashi da masara har guda hud'u, magarya, kwakwa da dabino, ya ajiye min.
Har zai fita ya tsaya a bakin kofar cikin sanyi murya yace.
"Maryam miye matsalarki da Yayanmu, dan nakirashi nace mishi baki da lafiya kina asibiti yace min cikine ya zube."

Girgiza mishi kai nayi, muryana narawa nace.
"Wallahi babu komi."
Fita yayi kawai, dan yasan waye Yunus.
Bayan fitashi na shiga ruɗani sosai, dan haka kawai zuciyata ke sasasho min wani abu na daban, lalubar wayata nayi na kunnata..
Lambashi na nima, tashiga amma yaki ɗauka, sake kira nayi bai ɗauka ba, sai a na uku ya ɗauka cike da masifa.
"Toh mi zan miki? Dake ke ba matar rufin asiri bane shine kika fita ban sani ba, har zaria wato ni ban isa dake ba? Kinje haɗani da iyayena ko maryam? Shi kenan ban yafe ba."

A sanyayye na kira sunan shi.
"Daddy!!! Kayi hakuri ban kai karanka ba, kawai daddy ina wahala ne da abinda kake min, idan kace yau na dawo zan dawo don Allah ka janye batun Allah ya isa nan, kayi hakuri."

Yanda nayi maganar sai da jikinshi yayi, yace.
"A'a ki zauna ni zanzo ɗaukarki,"
A hankali na shiga jan shi da jira, har yasake damu muka kashe lokaci muna hira, wanda zallar shagwaɓa ce zalla da kiriniya nake mishi.

........Ranar jumma'a sai gashi a zaria ma yayi sallar jumma'a, bayan sun gaisa da iyayenshi nima muka keɓe yayi abinda yasaɓa taɓayya, da dare korani gurinshi Mama kilishi tayi, tabbas nayi kewar mijina, dake bai zo min yanda sai yasha magani ba yau a musulunce ya zomin, amma dake dama can da lafiyarshi sai da na fashe da kuka, sabida gajiya da wahala, kuma yan kwana biyu ba a jone ba, dakyar ya kyaleni yana sauke numfashi.
Tsaki yayi dan gani yake kamar cikin ne ya sani jin gajiya, juya min baya yayi a hankali naje na kwanta a bayanshi cikin sanyin murya nace.
"Kayi hakuri, bazan kuma kuka ba idan mukayi wanka kazo kasake, bazan kara ba."

Juyawa yayi cikin jin daɗi, yace.
"Ok jekiyi wanka ina zuwa."
Mikewa nayi na shiga bayin kamar jirana yake. Ya janyo jakarshi ya ciro maganin yajefa a bakinshi, dake akwai ruwan da na kawo mishi ya ɗauka yasha sannan,ya shigo ban ɗakin.
Wanka mukayi tare sam ban kawo yasha kwayar ba, sai da muka dawo yace zai koma.
Banki ba dan na rigada na amince mishi, hmmm basan mi Yunus ke nufi dani ba, amma dan wahala kan nasha shi, dan ina jinshi ina ganinshi sai da yagama cutar dani sannan ya duba ko abinda yake bukata ya faru, babu komi sai dan abinda ya fitarm daga jikinmu.
Shida kanshi ya shiga dani, kwalla nabin fuskana haka yayi min wanka shima yayi nashi muka fito.
Washi gari dana samu na koma ɗaƙin hajiya ban kuma yarda na haɗu dashi ba, da dare tace naje kuka nasaka mata, nace.
"Hajiya idan naje mutuwa zanyi don Allah ki barni Daddy ya sauya baki ɗaya, baya tausayina duk abinda yasan zai cutar dani shi yake min, don Allah karki mishi magana kawai zan zauna a nan har mu koma gida."

Shiru hajiyarshi tayi tana kallona, gyaɗa min kai tayi cikin sanyin jiki ta nuna ɗakinta na shige ina kuka, wannan wacce irin rayuwa ce. Nake ciki mai nayiwa Yunus yake son kashe ni da sauran numfashina. Kwalla masu zafi suka sauko min, duk yanda nake son shi baya gani bazai tashi wahalar dani ba sai lokacin da nake bukatar kulawarshi. Dakyar barci yayi gaba dani.

Allah yaso shi bai sha maganin ba, tunda ya lura naki musake haɗuwa ya ajiye maganin, burinshi yanzun bai wucce ya kaini gurin liktan a cire cikin ba, dan ya lura cikin ma yana son kawo mishi matsala.
.....Kwanakin da ya ɗiba mukayi sannan na shiga haɗa kayana ins kuka, dan tun ban bar gidan ba jikina ke bani akwai mugun al'amari a gabana, mama tashigo tayi min faɗa. Wai ya kai kara na gurinta bana son zama inda yake.
Kwarai idan ina falo na ganshi guduwa nake, sabida baki ɗaya ya sauya kaman ba yunus ɗin da na da sani ba.
Koda muka fito da kayanmu falon Alhaji muka shiga yayi masa faɗa, sannan Hajiya ma haka sosai tayi masa tijara.
Haka muka fito yana cika yana batsewa.
Ko a motar yaki kulani haka na jingina da kujeran motar ina kuka, gidan mai ya shiga yasha mai abin haushi warin fetir yasani na shiga amai.
Kallona yayi ya kaɗa kanshi ba tare da wani shakku ba, yace.
"Kina wahalar da kanki, sosai daga nan zan kaiki asibiti a cire *Cikin*"

Wani irin faɗuwar gaba naji tare da ɗago kaina, bakina a sake nake kallonshi, Nace.
"Kayi hakuri karka rabani da shi ina son abuna don Allah idan ma nice ka maidani gidanmu wallahi zan zauna a can amma daddy karka rabani yarona."

"Wow kina

58 / 64