Matar So 1 Complete Hausa Novel

Author :  M Shakur Category :  Romance

Chapter   31 / 64

90K to 93K   out of 190.6K words

baki saya karki karanta sabida na kuɗine, idan kika samu an sato toh karki faɗa min maganar banza dan zan iya miki Allah ya isa, duk wacce ta fitar min Na barta da Allah_

*BOOK ONE👈*

*Page.8*

      "Amin Ahmad, rabu da ɗan iska yaje yayita fama da guzumayenshi kai ba sa'ar Huda ba, ko Sa'ar Samee ne i don't care tunda mace ce, kuma zata ɗauki lalurata da damuwata ai da sauki ko ɗaura min mai shekaru 21+ akayi a kafa finciketa zanyi na kara gaba."
       Aman ya faɗa musu a fusace,

                Shiru Mai Nasara yanda yaga Aman ya ɗauka da zafin nan, shi kuma baya son tsawaita magana, sai ya kyalesu ya cigaba da abinda ke gabanshi ta waya.

      ........
      "Hindu baki ga mijinki ya shigo da yar malaman nan bane, kin zauna kin buɗe baki da hanci kina kallon mutane, lallai fa dani ce Ahmad yayi wannan gigin haukar da tuni na hautsina taron nan." Inji Hafsat,

       "Hmm kyaleni da bakin ciki zan sami yarinyar naci Uwarta babu abinda ya dameni," haka hafsat ta cigaba da zugata,

          .......
   Wayar hannun Rahilah ne ya kama haske tasaka a kunne amma sabida sautin, wakar da aka saka ya hanata ji mikewa tayi tace.
"Maryam Sajida bari nayi picking call, yanzun zan dawo."

     Da sauri tafita sabida an sake kiranta a karo na biyu, yanda take tafiyar Ahmad ya kalla cike da bakin ciki dan gani yake idanun sauran mazan akanta yake, jiknshi na tsuma ya tashi yabi bayanta.

               Taɓa Hindu Hafsat tayi tace.
"Kinga ni, ko kinga abinda nake faɗa mishi har ya kirata kije kice ubanta shegiyar yarinya sai kace aljana."

        Fita hindu tayi itama ranta a ɓace, tabi bayansu.
  .......
   Lokacin da Rahilah tafita  kiran Yaya Hayat ne, ɗauka tayi cikin dariya.
"Kaiii Bro irin wannan kiran haka. Ko Aunty ta juye mata yan biyu."

       "Auta ina wasa dake, dama na shiga gida ɗazun aka ce min kuna zaria biki shine nace bari na kiraku ina sauran yan uwan naki." Inji Hayat,

        "Eh wallahi Yaya suna cikin hall, nima sabida wayarka na fito, amma ynx zan koma,"

     "Toh ku kula da kanku sai kun dawo ko."

     Sallamah sukayi da juna, sannan ta juya zata, Wani matashi ta gani a bayanta sai murmushi yake dokawa, "Princess har kin gama da Bro ɗinmu, kinsan da za'ayi gasar kyau dole ma kicinye dan haskenki ya dushashe na sauran matan tunda kika shigo nake bin motsinki har da kika fito waya, da fatan Yariman zazzau bai takura gimbiyar zuciyarshi ba."

   Dafe goshi tayi cike da gajiya da surutunshi, raɓa gefenshi tayi zara wucce, yayi masa ya riko hannunta cikin murmushi yace.
"Baki ce min kome ba,kuma..."
     Fincike hannunta tashiga yi.
(Kalubale gareku Yan mata masu zuwa wani event na dare, karki kuskura tsautsayi ya fitar dake toh idan Allah bai kareki ba akwai ɓata gari a waje Allah ya karemu."

             Kokarin fauce hannunta take, yayi saurin rungumeta da ɗayar hannun, cikin tsananin tsoro tace.
"Nikan kyaleni,nace ka rabu dani bana so."

              "Haba baby babu abinda zan miki na shiryawa rayuwarmu tanadi me kyau bazan barki kiyi kuka ba, kawa...."

         "Saketa dan ubanka, tayi maka kama da kananun karuwan da ke bine, dan Ubanka." Inji Aman, yana takowa gurinsu yayinda idanunshi suka birkice da tsabar ɓacin rai koshi bai shirya dadumarta a haka ba, wani ɗan iska ya rungume mishi tanadin shi.

   Kin tsaketa Yaron yayi cikin fitsara ya kai kanshi zai sumbaci wuyarta, zuɓewa yayi a kasa tsabar yasha karfin naushin da Aman ya kai mishi, sakw binshi yayi da kafa duk ta ruɗe rike shi tayi cikin kuka tace.
"Don Allah ka rufa min asiri karka kashe shi."

   Juyawa yayi ya ɗaga hannunshi zai mareta, ganin yanda ta rufe idanunta da kare fuskarta ya sashi sauke hannunshi, ya fincikota yana kallon yaron yanuna mishi yatsa yace.
"Rahilah Matar Aman Mandara ce, duk wanda ya kuskura ya kara zuwa inda take Allah ɓatar dashi zanyi."

        Bari gurin. sukayi, aikuwa sai ga Hindu ganin irin rukon da Aman yayiwa Rahilah gashi sai kuka take, shi bai ma ganta ba, da gudu tazo ta rufe Rahilah da duka,
          Tare da tara musu mutane, tana cewa.
"Shegiya karuwa, dan uwarki taxo tagama tallarku shine bari ki fara akan mijina da babu ruwanshi, sai na kasheki."
Da karfi ya tureta Aman yayi ya juya da Rahilah, suka koma gurin da ya ajiye motarshi buɗewa yayi ya jefata ciki, yace.
"Duk abinda ya faru kece sila, gobe zan mai daku gidanku tunda har kin fara haɗa crushe wa kanki."
Rufe kofar yayi ya kunna mata Ac, ya juya.
"Aman baka isa ba wallahi sai na lalata rayuwar yarinyar can dan Ubanta, kaima munafiki ananamimi kaje kaja yar mutane kazaka lalata ko mi zaka samu a jikinta waw..." Marin da baiwa Rahilah ba shi ya sakewa hindu cikn masifa tace.
"Ko kasheni zakayi sai na faɗa, karuwarka ce ai yarinyar wa yasani ko Uwarkac....."

     Baisan lokacin da ya rufeta da wani irin bugu ba, a cikin mota kuma Rahilah na bubuga mota.

      Dakw gurin parking ɗin babu mutane dukar tsiya yayi mata ya tsallakata ya wucce, bai taɓa dukar ko kanwarshi ba, amma hindu tasahi ya daketa dukar da zaiwa katon namiji, ciki hall ɗin ya shiga ta mike dan jaraba, ta biyo shi,

   Mu kuma a ciki ganin rahila bata dawo ba hankalinmu ya tashi muka nufi gurin Maminshi hankalinmu a tashe muka faɗa mata Rahilah tunda tafita bata dawo ba,

   Mikewa tayi, muka shiga nimanta a hall ɗin sai gashi ya shigo ganinshi ranshi a ɓace yasa tace.
"Aman ina rahila?"
  
   Cikin harshen shuwa yace..
"Tana mota, kanta na ciwo."
       "Karya kake munafiki, an gungumi, dan Ubanka tsinane la'ananen zuwa yayi ya kwanta da yar mutane itama dake karuwa ce, uwarsu ta gama wa'azin karya, gefe guda ta turo su karuwanci idan nai miki karya kije tana motarshi." Inji Hindu.
              Juyawa Aman yayi zai rufeta da duka Ahmad ya rike shi, shi cikin konar rai Mamie ta tsinke shi da mari ba adadi, dole sautin dake hall ɗin ya tsaya cak sai karan marirrukan da Mamie ke zabga mishi, zuba gwiwawenshi yayi kasa kuma bata fasa marinshi ba, sai da Hajiya Yabi ta rike hannunta, tace.
"Haba don Allah, Falmata me yayi zafi haka," jikinta na rawa tace.
"Ahmad ko Mai Nasara waninku yazo ya maidamu zaria,"

       Take gurin bikin ya ruɗe da tashin hankali,gaba mai nasara yayi zuciyarshi na zafi,
Ahmad ya ɗago Aman, wanda jikinshi ya gama mutuwa, mika mishi keyn motarshi yayi, cikin wani irin fitar numfashi yace.
"Yarinyar tana cikin motana, ka kaisu gida."

           Sakamu a gaba tayi muka fita muna kuka, sabida tozartamu da mahaifiyarmu, muna fita mai Nasara ya kawo motarshi, juyawa Mamie tayi cikin ɓacin rai tace.
"Ina ya kai musu yar mutane."

    "Mamie bari na kawota," inji Ahmad, bin bayanshi mukayi ya isa gurin motarshi ya buɗe ɗago kanta tayi cikin kuka, ganin mu yasa tafito da sauri ta zuɓe a jikinmu tace.
"Ku kaini Ummana bazan kara kwana anan ba, zata kasheni."

  Riko hannunta Mamienshi tayi ta janyota jiknta tace.
"Muje yau zaku kwana a jikin Ummanku."

       "Don Allah girman shi da isar mulkinshi ki bari gobe ku koma. Gida, Hajiya Falmata na haɗaki da mahaliccinki"

        "Kin min dabaibayi Iyami, Kaman Aman bai san yanda zai iya da gidanshi ba, sai matarshi ta tozartani a bainar mutane, kinsan yaran nan basa iya rabuwa da iyayensu nasa Mahaifiyarsu ta barmin su, shine zata lalata musu suna, Wallahi tallahi billahi azim gobe da Auren Rahilah Aman zan wuni, idan banyi haka ba, toh Usman Kyari da Kubra Goni, shegiyata sukayi, batace karuwai bane, ni sai nasa rahilah zama karuwar a gidan Aman yanda ko ita sai yayi mata kallon doki."

           Cike da tashin hankali Aman ya faɗa cikin motarshi zai tadda, amma Ahmad ya dakatar dashi fitar dashi yayi daga gabar motar ya mai dashi baya, shi kuma yaja motar suka can gidan bakin Mai Nasara Ahmad ya kai Aman,

       Tsabar tashin hankali da zaran yace zai yi magana, sai ya makale dan dole ya kwanta kashin na masa mugun ciwo,

           ......
    "Wallahi kinyi asara Hindu, wannan wani irin bala'ine haka zaki zo ki rusawa mutane taron da suke, jinki abinda kikayi zai hanashi kara aurene banza shashasha, a wannan zamanin wake kishin jahilci,"

   Inji Fareeda,
   "Kyaleta Hindu kinsan ita anshata ta warke, kuma wallahi duk wannan abotar da suke da mijinku yasa Aman tunanin Aure ni Ahmad ya isa yace zai fara wannan haukarne tuni ban takawa kowa birki ba, keni har mahaifiyarshi zan iya shiga tsakaninsu dan karta kawo min shamaki da mijina."

           "Lallai kuwa Hafsat sai ki ɗaura ɗan mara, sosai."

     Inji Fareeda.

     ****
   Tunda muka koma gidan bikin muka cure guri guda, muna kuka duk aka rasa wanda zai rarrashimu, haka muka kusan kwana muna kuka goshin asuba bacci yayi gaba damu, ina tsakiyarsu Rahilah, mun sarkefe hannun juna.

     Karfe shida na safe, Mamien tashigo tasamemu a cure, tausayinmu ya cika mata,zuciya buga pillow tayi muka farka da kyar, juyar da kanta tayi cikin damuwa Tace.
"Takwas nake son mushiga kaduna, kutashi."

    Mik'ewa mukaya Nice na fara shiga nayi wanka alola na fito, sai Rahimah sannan Rahilah abin karyawa aka kawo mana sama sama, muka ci, sannan muka fito ana ganinmu aka fara kuskus sai duk muka tsargu da kanmu, ɗakin muka koma ina jin wata nacewa.
"Bakarce fa, akace yayi sex da ita ba faran ba."
      "A'a ita ɗaya dogowar matar tace fa, aisu daga bayane suka ankara bata nan, namiji shege amma ai kinsan shi iyayenshi manyan ne maganar zata ɓoya,tund.."

          Ran Mamie ne ke kara ɓaci ta kallesu sannan ta shiga ɗakin ta fito da Rahilah ta tura musu gabansu cikin ɓacin rai tace.
"Wallahi ban taɓa zina ba, haka Mahaifin Aman itama yarinyar iyayenta tsarkakkakune masu kima, shine kuke jifanta da kalmar zina, ina shaidarku, ina tabbacinku budurwa wacce bata taɓa sanin namiji ba, ana ganota ta hanya mai sauki ku duba min ita idan Aman ya lalata musu yar mutane, budurwan da tasan namiji kuwa ana gane haka ne ta hanyar buɗewar mazauninta,kee Rahilah cire hijab ɗin jikinki su tabbatar, kaiiii koda Aman yasamu damar kusantarta toh zanyi bakin ciki amma na yarda da kaddara kuma ashirye muke mu nima mishi aurenta, ku matane iyayen kuma, Allah ya gwada muku kwantankwancin abinda kuka jefi bayin Allah dashi."

   Kamo hannun rahilah tayi wacce take kuka kaman ranta zai fita, tasanya mata hijab ɗinta muka bar gidan, gaskiya rayuka sun ɓaci sosai, muna cikin mota sai share kwalla muke, ita kuma rahilah kuka take sosai har muka shigo kaduna, kaitsaye gidanmu ta wucce,

    Tasamu malam bai fita ba, tunda muka shiga gidan muka sami Yan uwanmu a gidan ɗakin Umma muka shige, itama Mamie ta shiga ɗakin Mama.
      
  Gaisawa sukayi cike da mutunta juna, sannan ta basu hakuri da abinda ya faru,

              Dr Mohmud Mandara ne yazo suka tattauna tare da bada sadaki.

       A cikin mutuntaka aka tsayida kome sai an sako jumma'ah.

                    Godiya Mamie tayi sosai sannan tabar gidan.
          
     Ina zaune kan rahima na cinyata Rahilah na kwance akan jikinta, Umma ta shigo mikewa mukayi cike da tsoro muka ja baya,

               Zama tayi ta mikawa Rahilah Zuma dafaffe me ɗauke da dabino, a cikin wani bowl na tangaran tace.
"Ina son a cinye min sannan, a shanye min zumar."

           "Hmm naji abinda ya faru, da nasan haka zai faru da ban barku a gurin ba, amma kaddara ta riga fata,"

            "Rahilah zaki shiga wata rayuwa ce mai ɗauke da abin mamaki da alajabi, zaki ganshi tankar wata tafiya ce da bata da iyaka, Rahilah rayuwace wacce bata da farko balle karshe, yakine a gabanki mara makami, amma idan kika so zaki ya sayan makamanki ki shiga dasu, sabida baki san mi zaki tarda a inda zaki jeba, dan tafiya ce mai cike da tsire gashi dajine mai cike da kayoyi,
         A tafiyarki da zakiyi akwai bukatar guziri, wanda zaki nemi hakuri,juriya, biyayya, ladabi, amana, gaskiya, Iya magana, girki, tsafta, uzuri, da yafiya,fahimtar juna..... Idan kika duba kalamar yakin dake gabanki wancar bayanin yake bukata, haka idan kika duba kalamar daji me cike da kayoyi wancan jawabi yake bukata, Rahilah bansan waye Aman ba, amma ke zaki fini saninshi sai kinyi hakuri da halayarshi dan ba kabir bane ko Yayanku Hayat, ba kuma malam bane da zaki ce kinsan halinshi kece zaki san meyake bukata, miye baya bukata wani abinci yafi so, wani irin rayuwar aure yake so dake, shi yana da hakuri ko ma faɗacine, Rahilah, Rahimah, Maryam,ina faɗa muku ne, dan ya amfaneku badan raɗin kowa ba, ni baxan muku, show glass na kayan mata ba, dan bazai baku namiji a hanunku ba, idan kuka maida alamarinku ga Allah shine yake rike da zuciyar mijinku, kuma shine yake tallafe da al'amuranku, bazance rayuwar aure nada daɗi ba, amma nasan wuyarshi sabida ɗaɗinshi kalilane, kuyita addu'a da azkar ku yawaita sallar dare, idan ya barku ku rike axumin nafilla, iyayenshi da danginshi su zama sune, asama da iyayenki karki fifita iyayenki sama da nashi, haka zai kara miki daraja da kima a idanunshi, sai gaɓɓa na musaman, shine jikinki za'a wayi gari ya mallaki duk wani abu naki, a cikin yanayinda koda kiranshi kikayu ko rokonshi, kaiii duk abinda zakiyi kiyi bazai taɓa jinki ba, sabida kudirinshi da hakkin kasancewa dake zai bijiro masa,Maryam, Rahilah, Rahimah wannan ranar idan yazo ku kira kowa dan su taimakeku bazasu iya taimaka muku ba, sabida nauyi ne da ya rataya akanki ki sauke kuma zaki sauke shi, da zaran haka ya faru toh kin fita sahun yara kinshiga kwaryam Manyan, duk abinda muka sani kunsani, koda wasa karki bari mijinki ya gano kazantarki ko wani nakasu a jikinki, zan baku misali akanmu kun taɓa ganin Malam yace wani abu mara kyau akanmu,"

   Girgiza kai mukayi, cikin kuka, tace.
"Yawwa sabida, mun yarda da kanmu karku bari mazajenku su gano illarku, a fagen girki da tsafta nasan renonane ku, a fagen hakuri da juriya renon Mamanku ce, sai iya magana wanda nasan wannan renon malam ne, kuma Alhamdulillah ta kowani fuska bamu da aufi akanku, sai da Rahilah kina da kishiya, kuma nasanta nasan halinta bazan ce miki komi akanta ba, ke dakanki zaki gano halinta karki rena mishi mata, naso da sai kon gama karatunki amma Mahaifanshi sun nuna bukatarki zaki karasa a gidan don Allah ki rufa mana asiri ki bawa mara ɗa kunya, ki tayamu ganin lafiyar Amarya ya inganta tunda gausiya ta dawo kullum sai Amarya ta shaki Inhelarta, sannan ki ajiye kunyarki washi garin ranar da kika zama Mace dan daga nan zaki mori aurenki, iya abinda zan faɗa miki kenan kuma Wallahi naji labarin yarinya tace kasuwar ganye ko wata banzar mata ta kawo mata maganin matq ta saya na rantse da Allah sai na mata shegen duka, idan kina son maganin mata, kiya shema'u magana balle hajiya falmata bazata barki haka ba, naji daɗi da kika sameta a surikarki, Rahimah kema an nan za'a zo niman aurenki, saura Uwar masu gida yarana sun mata wayo."

          Tana gama mana nasiha da huɗubar da yasamu cusa kai a cikin cinyoyinmu, tafita kuka Rahilah tayishi ba iyaka, musaman da aka zo ɗaukarta za'a mata wanka da lalle mai haɗi da miski, tana fitowa akasata a gaba sai da tashanye zumar nan, tana kuka tana kome,

            Abin tausayi, sai muka zama kamar wasu kala aure zai rabamu da Rahilah, kukanmu yaki karewa, sai da Umma tazo ta balbalemu da masifa sannan mukayi shiru, karshe sai ga Rahilah tana janmu da hira da wasa da dariya.

            ****
      A zaria kuwa sai da aka dangana da Aman asibiti, sabida jininshi da yayi masifar hawa, a daren suka kai shi, gari na wayewa, ya farka wajen karfe tara nasafe ya gabatar da  sallah yana idarwa ya juya ga  Ahmad, yace.
"Abokina ka yarda dani wallahi ban aikata abinda hindu ta faɗa ba, asalima kwato yarinyar nayi daga mugun hannun, Abokin.."

      "Toh mr romeo, aimunsan da haka, kawai ka rufe mana bakinka ka tashi mu wucce kaduna dan karfe biyu da rabi za'a aura maka jinjirar da kake suma akanta." Inji Mai nasara,

       Mikewa Aman yayi ya naɗe abin sallar Ahmad ya amsa, sannan ya koma bakin gadon ya zauna, ɗago jajayen idanunshi yace.
"Ba auren yarinyar bace mafita, fahimtar Mamie shine mafita, dan nasan halinta akan wannan abun zata iya daina min magana."

   Shigowar likita yasasu sukayi shiru mika musu hannu yayi sukayi musabaha,, yace.
"Mr Mandara ko zaka iya kwanciya a dubaka."

    Kwanciya yayi likitan ya,shiga duba lafiyarshi, ya tabbatar musu da kome lafiya sai dai ya kiyayye ɓacin rai,

        Sannan ya sallamesu, daga nan ko minti ɗaya basu kara ba, sai kaduna, kwantar da kujeran yayi ya lumshe idanunshi, cikin tsananin damuwa yace.
"Dole na rabu da Hindu, dan haka ne mafi alkhairi a gareni."

     "Hmm aikuwa a jaridar Aminiya za'a wallafaka wani yasaki matarshi sabida zai auri jinjira waccw bata fara kirgan dangi ba," Inji mai nasara,

               Juyawa yayi ya kalli Ahmad da yake tuki, sai danne dariyarshi yake, juyawa Aman yayi ya kalle Mai Nasara cikin jin haushi yace.
"Eh gwara ni, jaririya zan aura kai da katara, jakuna

31 / 64