Author : Faddy baby Category : Romance
da Inda zata zauna shine dalilin ma da yasa M, D, barinta gidansu, nina rok'anmata, yanzu idan ya koreta ina zata?, ki yi hak'uri daga yau zata gyara ". "Shikenan badamuwa amma ta kiyaye ta rik'a zuwa aiki da wuri". cewar Billy, sannan ta fita daga Office d'in manager".
Hassana ko komawa ta yi taci gaba da aikinta, Hassana na tsaka da aiki ne, wata staff ta kalli Hassana ta ce, "Ke ce Hassana? ". "Eh ni ce". "Tom Supervisor ta ce idan kin gama morpping d'in ki je tana kiranki". Hassana da tom ta amsa. Aiko Hassana na gama wa ta je office d'in supervisor ta ce, "Supervisor ance kina kirana". Billy sai da tagama abinda ta ke yi, sannan ta ba Hassana wani Cup ta ce taje ta wanke mata. Hassana amsa ta yi ta je ta wanke mata ta kawo mata. Bayan Hassana ta dawo ne, Billy ta kalli Hassana ta ce, "Hassana ki ke kome, dama kunne zanja miki, sannan kinsan ya zama dole a hukuntaki abisaga laifin da ki kai, na fashin da ki kai baki zoba, daga yau sai 10 o'clock zaki rik'a close". Hassana kallanta Billy ta yi ta ce, "Supervisor dan Allah ki yi hak'uri,Oga Habib ya ce kar in wuce magriba ban dawo ba".Billy Cikin d'aga murya ta ce, "Oh!, kina nufin duk da laifin da ki kai har wani ragin lokaci kika samu, tom wannan kuma ke ya shafa ni dai kinji abinda na ce miki, idan kuma kink'iji zamu rage a salary d'inki". Shiru Billy ta yi sannan ta nuna ma Hassana hanyar fita, ta ce, "fitar min daga office. Hassana fita ta yi tana mamakin yadda Billy ke nuna mata tsana k'iri-k'iri".
Hassana magriba na yi, kamar yadda Habib ya ce mata ta koma gida, magriba na yi Hassana ta shirta ta koma.
Tun daga wannan rana ya zamana kullum Hassana ta je aiki Billy ta dinka sata aiki kenan, daga yi min wancan sai yi min wancan, har wankin toilet d'in gun Billy Hassana ta ke sawa, acewarta abakacin tashin da wurin da ta ke yi. Ita kuma Hassana ta yi ma kanta alk'awarin duk abinda Billy ta sata zatayi baza tai mata musuba, hakan ya sa Hassana ta kuma ramewa sosai.
BAYAN SATI D'AYA.
Hassana sosai ta dage sai goge-goge ta ke yi so ta ke tagama tai ma manager magana ta tafi gida, saboda ciwan da kanta ya ke mata. Hassana na Cikin aiki wata staff ta ce, Hassana kije Office d'in manager ana kiranki". Hassana sauri ta yi tak'arasa abinda ta ke yi, sannan ta je office d'in manager. Hassanan da mamaki ta ke kallan shi ta ce, "Oga Bilya kaine, yau she kadawo? ". Bilya murmushi ya yi ma Hassana sannan ya ce, "Hassana tun jiya na dawo,ya kike ya aiki? ". "Lafiya klau, barka da dawowa Oga Bilya". Bilya kallan Hassana ya yi yace, " Yauwa Hassana, zaki iya ko mawa ki ci gaba da aikinki, dama nakiraki ne mugaisa. Hassana kallan manager ta yi tace, "Manager bani da lafiya, dan Allah ina son zuwa gida yau da wuri in samu magani insha". Manager kallan Hassana ya yi, sannan ya ce, " ki fad'ama supervisor ". Hassana shiru ta yi dan tasan in dai ita ce ma babarinta za tai ba, amma ance mai naima baya fushi, hakan yasa ta fita Office d'in manager ta shiga na supervisor. Hassana na zuwa ta kalli supervisor ta ce, "Supervisor bani da lafiya, ina son zuwa gida dan Allah, zan sha magani". ko inda Hassana ta ke Supervisor bata kallaba, ta ce, " Idan kin je karki dawo". Hassana najin haka tafita office d'in supervisor dama tasan ba barinta za tai ba. Hassana haka ta koma guri d'aya ta zauna dan bata iya komai tsabar ciwan kan da kanta ke mata. Hassana ba ita ta tashi ba sai magriba kamar yadda ta saba tashi. Hassana tafiya ta rik'ayi a k'asa kafin tasamu napep ga wani irin ciwo da kanta ke mata".
Bilya ko yadawo bakin aiki, saboda Hajiya Turai na dawowa tasa Habib ya dawo da shi. Habib da sauri ya fito domin tafiya gida baya son magriba ta sa mai anan. Bilya ko dama yana ganin time d'in tafiya gidan Habib ya yi, ya shiga motar yana jiran fitowar Habib. Hakan yasa Habib na shiga Bilya jaya motar suka kama hanya. Bilya tsaye ya hanki Hassana can gefan titi daga gani abin hawa ta ke jira. Bilya Kallan Habib ya yi, ya ce, "Oga Habib dan Allah ga Hassana can ko zamu rage mata hanya? ".Habib banza ya yi da Bilya. Bilya ko jin Habib ya yi banza dashi yi tunanin ko be ji abinda ya ce bane, hakan yasa ya k'ara cewa, "Oga Habib ga Hassana can na ce, dan Allah ko murage mata hanya? ". Habib tsaki ya ja alamun Bilya ya da mai, Bilya ko najin haka ya kama bakinsa yayi shiru. Bilya yana ji yana gani suka wuce Hassana tsaye badan yaso ba, sai dan bashi da yadda zai yi. Habib sai da ya yi Sallar magriba sannan ya shiga site d'in Mommynsa. Habib na shiga ji yayi kamar ya juya ya koma, sai dai bashida yadda zai yi tariga ta ganshi, hakan yasa Habib ya kuma tamke fuska ya shiga falon.Farida da saurinta ta tashi zata yi welcoming d'in Habib. Habib hannu ya d'aga ma Farida. Farida ja tai tatsaya tana Kallan Habib kamar za tai Kuka, ta ce, "Broz Habib kana nufin bakai murnar ganinaba? ". "Yess ". Cewar Habib. "Farida bana murnar ganinki saboda shirman da kike min". Farida Kallan Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Mommy kinji fa abinda Broz Habib ya ce, wai baya murnar ga nina". Farida ta fad'i maganar kamar zata yi kuka. Hajiya Turai hannun Farida ta kamo tana murmushi ta ce, Farida rabu da Habib shi bai san wacece Farida bane"., Habib ko ji yayi ba zai iya jure zama ba afalon Hajiya Turai hakan yasa Habib Kallan Momynsa ya ce, "Mommy zan shiga ciki ki bada tea akawomin". Hajiya Turai Kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib gobe zan wuce, jirgin safe zan hau". Habib Kallan Hajiya Turai ya yi , cikin damuwa ya ce, " Kai Mommy wannan karan kin koma da wuri".murmushi Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Habib kamar kana da damuwa Allah kalli face d'in ka ? ". "Babu abinda ke damuna Mommy". Habib na fad'in haka ya wuce. Habib falon shi ya je yana jin wani iri acikin jikin shi, amma yarasa gane shikan shi me ke damunsa. Habib na nan kwance Farida ta shigo rik'e da tea a glass cup. Habib bai cika cin abinci ba da daddare sai dai yasha tea. Farida har inda Habib ya ke , ta k'araso, tea d'in hannunta ta mik'ama Habib ta ce, "Broz Habib gashi in ji Mommy ta ce kasha dan Allah badan ni ba".Farida ta yi hakane saboda tasan da wuya Habib ya sha tea d'in. Habib amsa ya yi ita kuma Farida ta fita dan bataga fuskar zama ba. Habib haka ya ke jin shi wani iri ahaka ya samu sha tea d'in. Yana gama sha ya tashi ya yi Sallar issha'i sannan ya kwanta, dan sosai ya ke jin jikin shi ba dad'i, bakamar brain d'in shi ba tana mai ciwo sosai, haka dai Habib ya samu wani wahalallan bacci ya kwasheshi.
Washe gari tun asuba, Hajiya Turai taima Habib magana, ya shirya dan seven o'clock Am, ta ke son tafiya. Habib tashi ya yi badan wai yaji sauk'in yadda ya ke ji ba, wanka ya yi, ya yi shirinsa Cikin wata dark blue suit. Habib mota ya zauna yana jiran fitowar Hajiyarsa. Hajiya Turai da Farida suka fito Farida na rik'e da jakar Hajiya Turai. Hajiya Turai amsar jakarta ta yi hannun Farida ta ce, Farida ki koma gida. Farida ba Hajiya Turai ta yi saboda bata so tana mata musu. Bayan Hajiya Turai ta shiga motar, kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib ko dai zuwan Farida ne yasa naganka haka so silent". Habib kallan Mahaifiyarsa ya yi, ya ce, "Mommyna bashi bane, nima haka na ke jin jikina duk babu dad'i, ga jiya nayi wani mafarki da yaban tsoro sosai, amma karki damu nayi addu'a, kuma yanzu normal na ke jina". Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Shikenan Habib, amma dan Allah kaje Hospital ka yi check up, dan Allah Habib na sanka da shiririta". Habib ganin Hajiya Turai ta damu, yasa ya kalleta yana murmushi, ya ce, "Mommyna normally fa nake jina yanzu, karki damu yanzu daga na kaiki airport zan je ganin likita". Habib action ya rik'ayi kamar mai lafiya, dan yasan in ya nuna ma mommysa ba ya jin dad'in jikinsa tom bazafa tatafi ba. Koda Habib ya kai Hajiya Turai airport. Hajiya Turai rak'on Habib ta yi sosai akan ya je Hospital aduba shi, nan dai Habib ya yi mata sallama ya nufi sanat yoghurt Company".
Habib na zuwa Office d'in shi ya shiga, Habib na shiga ya kira Bilya awaya, ya ce, "Hello, Bilya ina sanat yoghurt, ka biya restaurant d'in kusa damu ka tahomin da abin break fast". Habib na fad'in haka ya katse kiran.
Bilya ko lokacin da Habib ya kira shi tashinshi a bacci kenan, hakan yasa Cikin sauri Bilya ya shirya yaja motar shi yafita. Da safe da kuma dare Habib tea kawai ya ke iya sha, sai wainar k'wai. Bilya na shiga Sanat yughurt , ana sauke Hassana ita kuma a napep. Bilya kallan Hassana ya yi, ya ce "Yauwa Hassana dan Allah amshi break fast d'in nan ki kai Office d'in Oga Habib. Hassana tsayawa ta yi tana kallan Bilya ta ce, "Oga Bilya dan Allah ka kaimai da kanka Allah bana son shiga office d'in Oga Habib. Bilya mik'ama Hassana ya yi, ya ce, "Hassana haka nan zakiyi Hak'uri ki amsa, tun d'azu Farida ke kirana in zo in kawota Sanat yughurt, Wallahi na manta sham sai yanzu na tuna, tom shine ke so inje in d'akkota, yanzu idan na shiga office d'in Oga Habib zai iya sani wani abun, ba zai barni in fito yanzu ba, dan Allah ki amsa ki kai mai". Hassana amsa ta yi ta ce, "Haba Oga Bilya, ai Umarni zaka bani na aikata ba sai ka rok'eniba". Dariya Bilya ya yi ya ce, "Bakomai Hassana girmanki ne, bari in je in dawo dama Wallahi ina son wata magana mai mahimmanci da ke". Hassana itama murmushin ta yi tace, "Tom Oga Bilya sai kadawo". Bilya tafiya ya yi Hassana kuma tana rik'e da break fast d'in Habib ta nufi office d'in shi".
Hassana nocking ta yi. Tad'an dad'e atsaye tana nocking sannan Habib ya bata izinin shiga. Hassana na zuwa Cikin girmama ta ce, "Barka da safiya Oga Habib ga shi inji Oga Bilya, ya ce yanzu zai dawo". Habib batare da ya amsa gaisuwar Hassana ba, dan zuwa yanzu sosai ya ke jin ciwo acikin jikin shi. Habib kallan Hassana ya yi, sai zuwa can ya tashi kamar zai amshi jug d'in hannun Hassana, sai kuma ya fasa, ya dafe kanshi da hannun shi guda d'aya ya mik'ama Hassana d'ayan hannun nashi, yana rin tse ido, ya ce da k'arfi dan har wanda ke waje sai da yaji. "Ahhhh rik'e min hannunaaaa!!? Habib ya fad'i maganar da k'arfi yana mik'ama Hassana hannun shi. Hassana sosai ta tsorata, Hakan yasa ta saki jug d'in hannunta ta bud'e k'ofar Office d'in zata fita. Sai dai ina ta makara kafin ta bud'e kofar sai dai taji anjawo hannunta da k'arfi.....................
A'A, WAI ME KE FARUWA NE?, NI FA BANGANEBA.
NASAN WASINKU DA DAMA ZASU CE HAKA.
KARKU DAMU ZAKU GANE.
LABARIN YANZUN YAFARAππ»ππ»ππ»ππ»
BANDA LAFIYA DAN ALLAH INA BUK'ATAR ADDU'ARKU.
COMMENT
&
SHERE
PLEASE π
π OGA HABIB π
π«π«
*π
οΈARUMAI π
¦οΈ WRITERS π
οΈSSOCIATIONπποΈ*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausaπͺ*_
*π«(π
οΈ.π
¦οΈ.π
οΈ)π«*
TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI ( Faddy baby).
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7
My Facebook group :Fadila Sani.
https://m.facebook.com/groups/565235401564189/
π Ibnul-Qayyim (Allah Yayi masa Rahama) yana cewa: *"Lalle damuwa, baΖin ciki da qunci suna faruwa ne ta dalilai guda biyu: _Daya daga cikinsu shine son duniya da nemanta (ta kowace hanya), na biyu kuma rashin aikata ayyukan kwarai da (kyautata) ibada"_*
π [Iddatus-Saabireen - P. 265].
Allah kasa mu dace.
SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!
YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM
YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI.
NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN ππ»
K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!!
KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI.
K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA ZA A FARA POSTING.
KI GARZA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE!
WHATSAPP CONTACT ππ»
08142904255.
Shafi na 18&19.
Hassana sosai ta tsorata, hakan yasa ta saki jug d'in hannunta ta bud'e k'ofar Office d'in zata fita, sai dai ina ta makara kafin ta bud'e k'ofar sai dai taji anjawo hannunta da k'arfi, an dawo da ita baya. Hassana cikin tsoro ta d'aga kai tana kallan Habib".
Habib ko rik'e hannun Hassana ya yi da k'arfi da d'ayan hannunsa, d'ayan hannun kuma ya dafe kan shi da shi.
Hassana da Habib kusan atare suka yi k'ara wadda duk kusan wanda ke cikin Sanat Company babu wanda bai ji k'ararnan ba".
Ita Hassana k'arar tsoran yanayin da taga Habib ne ta yi, shi kuma Habib ta sabon yanayin da yatsinci kan shi cike ce. Hassana cikin tsoro ta kalli Habib tana cewa, "Wayyo hannuna Oga Habib dan Allah ka yi hak'uri kasakanmin hannu". Hassana ganin Habib kamar ba cikin hanyyacin shi ya ke ba, kuma ya rik'e hannunta katakam, ga zafin rik'on da ya yi mata take ji. Hakan yasa Hassana ta dage sai ihu ta ke".
Dai-dai likacin ne kuma Bilya da Farida suka shigo Sanat company. Bilya da Farida da saurinsa suka k'arasa shiga cikin Sanat company. Inda suke jiyo ihun suka nufa. Dai-dai lokacin shima Manager ya fito daga Office d'in shi da sauri ya nufi na Oga Habib dan anan ya ke jiyo sautin k'arar. Atak'aice dai duk wani ma'aikacin da ke cikin Sanat yughurt, da saurinsa ya ke nufa inda ya ke jin alamun k'arar mutum".
Manager da Bilya kusan atare suka turo k'ofar office d'in Oga Habib, inda Farida da Billy suka mara masu baya. Bilya cikin tashin hankali ya nufi inda Habib ya ke, ganin yarik'e hannun Hassana kata kam, yak'i saki, sai wasu magan-ganu da yake yi kad'an-kad'an, bazaka iya jin me yake cewa ba, kodan ihun da Hassana ta ke yine".
Bilya cikin girmama da fargabar ganin yanayin da yaga Habib, ya ce, "Oga Habib lafiya karik'e mata hannu?, idan laifi taima dan Allah ka yi hak'uri ". Habib kallan Bilya ya yi yana zazzare ido. Bilya kallan Habib ya kuma yi da kyau, dan sosai abinda Habib ya yi ya ke naiman d'aure mai kai, dan asanin Bilya mata ma masu aji Habib bai kulaba bare kuma Hassana da ke a k'ark'ashinshi. Sannan idan ya lura da kyau kamar Habib bacikin hayyacin shi ya ke ba. Hakan yasa Bilya kama hannun Habib da niyyar fusge hannun Hassana.
Wani duka Habib ya ke ma Bilya a wuya, wanda sai da Bilya ya yi k'ara. Bilya da sauri ya matsa yana kallan Habib. Bilya manager ya kalla yana dafe gefan wuyan shi inda Habib ya nusai, yace, "Manager lafiyar Oga Habib k'alau kuwa? ". Manager kallan Bilya ya yi, ya ce, "Nima abinda nake tunani kenan, amma bari mugani".
Manager matsawa ya yi kusa da Habib ya ce, "M. D, dan Allah ka yi hak'uri idan laifi taima, kasakar mata hannu yau zamu koreta daga ma'aikatar nan baki d'aya ". manager ganin Habib ya yi banza da shi yana kallan shi, hakan yasa ya kama hannun Habib da niyyar b'amb'are na Hassana".
Habib duka ya kawo ma manager.
Allah ya tai maki manager ya kauce da sauri. Tun daga nan fa kowa ya fara baya-baya.
Hassana ko ganin haka suna nai man fita subarta daga ita sai Habib, ya sa ta fasa kuka tana cewa, "Wayyo Allah Oga Bilya dan Allah karku tafi, manager dan Allah kuzo ku taimaka min".
Bilya kallan manager ya yi dadamuwa yace, manager akwai damuwafa, Wallahi Oga Habib baida Lafiya, dan kai kasan wannan abinda da yake yi ba halinsa bane, idan zaka kalli idon shima kamar baya cikin hayyacinsa". Manager numfasawa ya yi sannan ya ce, "Wallahi maganarka hakane, nima abinda nake tunani kenan, yanzu ya kake ganin za ai? ". Shiru Bilya ya yi, Sannan ya ce, "Ni gani nake kawai mu kwaci yarinyar nan daga hannun shi, mu kai shi gida, ala bashi sai a kira likitan k'wak'walwa ya duba shi". "Eh haka za ayi". Cewar manager. Manager wasu k'arfafan samari da ke aiki gurin guda biyu yasa su tai maka masu".
Bilya da manager ne suka yi jarimtar rik'e Oga Habib, sannan sauran staff d'in guda biyu suka k'wace hannun Hassana daga hannun Oga Habib da kyar. Sosai su manager suka sha wahala wajan sa Oga Habib a mota. Sannan Bilya ya shiga ya tuk'a motar da manager da Faruq kuma suka rik'e Oga Habib. Ahaka dai suka samu suka k'arasa gidansu Oga Habib".
Hassana ko bayan ta samu