OGA HABIB Bacewa da Samuwa by Faddy baby

Author :  Faddy baby Category :  Romance

Chapter   20 / 41

57K to 60K   out of 121.2K words

ta yi,"Farida ki yi hak'uri zuwa anjima sai ki kuma kiran Hajiya Turai awaya, kin san in tana kan aiki bata amsa kira".


Farida tom kawai ta ce ma Mahaifiyarya ta kashe kiran, Farida d'akinta ta shiga ta kwanta tana ta malele kuwa , dan jinta ta ke indai ba Hassana ta bar gidan ba, tom bata da sauran na tsuwa, bakamar yau ba da Hassana ta kuma in gizata, dan ta yi ran tsuwar sai ta nuna ma Hassana ruwa ba tsaran kwando bane. Farida da ke kwance da sauri ta ta shi Saboda wani tunanin da yazo mata, hakan yasa ta tashi da sauri ta nufi site d'in worker's d'in gidan"..


Farida tsaye ta yi tana Waige-waige, tana nai man wadda tazo gani, cikin sa'a Farida ta hangota tana shanya. Farida da sauri ta k'arasa inda ta ke, cikin sakin fuska, Farida ta kalleta ta ce, Sannu ko? ". "Yauwa Aunty Farida Sannu". Farida cikin sakin fuska ba irin yadda ta saba yima worker's d'in magana ba, ta ce, "Yauwa dan Allah ya sunan ki". Jimmai da mamaki ya cika ta, tun zuwan Farida gurinta, ta ce, "Sunana Jummai". Farida cikin yaudara irin na wayayyun mata ta ce, "Wow nice name, tom dan Allah Jimmai wani tai mako zaki min, zan biyaki konawa ne, na zab'eki kimin wannan aikin ne, Saboda na lura duk gidan nan babu wadda ta fi kusanci da Hassana kamar ke, tom dan Allah Jimmai zaki min wani taimako ne, ba mai wani wuya ba ne".Farida maganin da ke jikin zaninta ta ciro ta mik'ama Jimmai ta ce, "Jimmai dan Allah zaki barbad'amin maganin nan ne, a part d'in Oga Habib". Jimmai ta ke tsoro ya kamata ta ja da baya tana mai mak'e hannunta ta k'i amsar maganin, dan sosai ta tsorata da jin abinda Farida ta ce".


Farida ko ganin Jimmai ta tsorata da maganin da ta ke mik'o mata, murmushi ta yi, ta ce, "Malama Jimmai karkiji komai ba maganin cutarwa bane, na san dai kin san ina son Oga Habib, dan nasan duk wanda yake agidan nan yasani, tom maganin nan da kike gani Jimmai bana cutarwa bane, idan ma k'awarki kike ji, itama ba cutar da ita maganin zai yi ba, ni nai miki alk'awari babu abinda zai samu k'awarki, na naimi kimin hakane dan nasan ke kad'ai ce agidan nan ayanzu zaki iya shiga part d'in Oga Habib kai tsaye, dan Allah ki tai makamin ki amsa".


Jimmai da ke tsaye al'ajabi ya isheta, amsar maganin ta yi tana ma jin tsoran karna cutarwa ne ya fara aiki akanta".


Dubu goma Farida taba Jimmai , ta ce, "Wannan ba biyanki nai ba, sai kin cika aiki sannan nima zan cika ki da abin arzik'i kala-kala".


Jimmai godiya taima Farida, ta amshi kud'in , Farida kuma ta wuce tana mai jin dad'in burinta ya kusa cika".


Jimmai ko tana ganin Farida ta wuce ta yi sauri ta shiga toilet ta jefa maganin, dan acewarta idan na zutarwa ne k'ilama ita zai fara cutarwa ita da take rik'e da shi. Jimmai sai da ta jefar da maganin sannan ta ji hankalinta ya kwanta. Murmushi ta yi, ta ce, "Aunty Farida baki da arzik'in da zaki ban kisa in zutar da Oga Habib bare kuma Hassana, ya Allah na godema da ka ba ma wannan baiwar taka zuwa guna, bata je inda zata bata ba burinta ya cika, Allah kaika san mai take nema da yarinyar nan, Allah kakareta daga shairinta, duk abinda zata mata Allah ka mai da mata aniyarta". Jimmai zama ta yi gun tana sake yima Hassana addu'a, akan Allah ya kareta daga shairin Farida."


WASHE GARI:
Farida da wuri ta yi sammakon zuwa gun Jimmai jin shiru bata ga Hassana ba, dan acewar in dai magani ya yi Habib ya kusanci Hassana ai ya isa ace ta ji alamun motsin Hassana. In da in dai akan yadda Malam mai biyan buk'ata dole ya ce musu ne, Hassana da kanta zata bar gidan, wata zuciyar kuma sai ta ce mata" tom koma Hassana ta bar gidan baki sani ba ne bama". Hakan yasa Farida zuwa ta tambayi Jimmai. Farida har cikin d'akin su Jimmai ta shiga ta kira Jimmai".


Farida kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Jimmai na ce kin ko zubamusu maganin? ". "Eh Aunty Farida na zuba". Farida cikin jin dad'i ta juya ta nufi part d'in Habib, Farida na zuwa ta yi nocking d'in k'ofar, ta ji shiru ta kuma yi nan ma shiru".


Hassana ko lokacin ko tashi basu yi ba, dan takan dad'e tana addu'ar in ta idar da sallar asuba, hakan yasa idan ta koma baccin safe ta ke jimawa. Hassana cikin bacci ta ji bugun k'ofa, da saurinta ta tazo dan jin waye. Hassana na zuwa cikin murya mai kama da ta bacci ta ce, "Waye? ". Farida sumar tsaye ta yi, tana tunanin tom idan rannan ance Mommy ta ce ci Hassana yau kuma fa, yau dai daga ita sai Oga Habib, "anya ko maganin mutumin nan nayi?".Farida ta tambayi kanta, dan acewarta ba zai yuwu ba, ace haka na faruwa, sai dai in ko Malamin k'arya ne". Farida shiru ta yi bata amsa ma Hassana ba tabar gurin, tana zuwa ta kira Mahaifiyarta awaya ta ce, ta shirya gata nan zuwa kuma Wallahi yau babu abinda zai hanata zuwa Nijar, dama tun farko Mommy na ce miki bana son aiki irin wannan k'ila wa k'ala, tom gashi nan dai Oga Habib bai kusanci 'yar iskar yarinyar nan ba, dan haka gani nan yanzu ki shirya Wallahi bazan bari Hajiya ta dawo ta isketa a gidan nan ba". Hajiya Murja ko da bata da abin cewa wanda ya wuce ta yi biyayya da abinda Farida ta ce , ta ce, "Shikenan Farida ki zo tom dan nasan kona ce miki ki bari sai gobe ba bari zaki ba".


Farida na zuwa ta iske Hajiya Murja ta shirya ita taje jira, direct suka nufi airport sai dai inda suka je sai dai jirgin da zai kai su Katsina suka samu. Cikin isshan lokaci suka isa katsina, tun a airport d'in Katsina suka samu maimotar da zata kai su Nijar ".


Kasan cewar ba cancikin Nijar za su shiga ba , farko-farko ne yasa k'arfe hud'u na yamma suka isa gidan friend d'in Hajiya Murja wanda zata tai masu jagora zuwa gun bokan da zasu, in da dama ita ce ta tab'a yima Hajiya Murja hanyar shi".


Kasan cewar friend d'in Hajiya Murja ta sanda zuwan su Hajiya Murja yasa a ready ta ke, suna isa babu hutawa babu komai, danma sunci abinci akan hanya"..


Hajiya Bilki k'awar Hajiya Murja a motarta ta d'auki su Hajiya Murja ta kaisu har k'auyan da bokan ya ke".


Koda suka isa sun iske layi dan har sai da suka jira, sannan suka shiga. suna zuwa ya dakatar dasu ya ce, cikin muryar shi mara dad'in sauraro, "mai buk'ata kad'ai muke son gani, bama son 'yan rakiya, ku jirata a waje".


Hajiya Murja da Hajiya Bilki komawa sukai suka bar Farida kad'ai."..


K'urama Farida ido ya yi yana kallanta, dan har sai da Farida ta fara tsorata da kallan da bokan ya ke mata, sai zuwa wani d'an lokaci, ya ce, " me kike so ai miki, auran za'araba?, koko yarinyar ce kike so a kora daga gidan baki d'aya? ". Farida cikin zuciyarta ta ce, "Alhamdulillah kaji aiki". Sannan ta yi sauri cikin jin dad'i ta ce, "So nake araba auran kuma a kori yarinyar daga gidan baki d'aya, sannan ina son a dawo mai da hankalin shi ad'ora mai sona mu yi aure yana cikin hankalin shi ". Batare da bokan ya kuma cewa komai ba, wani magani ya d'akko yaba Farida, ya ce, "wannan zaki tauna shine ahaka zaki cinye shi, wannan kuma zaki wanke fuskarki da shi, wannan kuma zaki yarfa mai ajikine , ai dama ke ce kika haukata shi". Shiru bokan ya yi sannan ya ci gaba da cewa, "Magani na farko da nace miki zaki tauna, duk abinda kika ce, kina so agurinsa zai yi, zai ji maganarki fiye da ta Uwar da ta haifaima, a haka ne zaki bashi umarnin ya kuri ita yarinyar kuma ya saketa, magani na biyu da nace zaki wanke fuska da shi, shi kuma duk wani abun k'i da yake gani wanda ya hana shi sonki tom kamar shine kika wanke, magani na uku kuma wanda nace ki yayyafame, shine wanda zai dawo da shi hayyacinsa". Yana kaiwa nan ya ce, "mungama miki aiki, saura kud'in aiki zaki biya".


Farida kud'i ta ciro masuyawa ta ajema bokan, sannan ta ce, "Amma abinda yake ban tsoro ta yadda zanga Oga Habib d'in, dan yarinyar bata barina shiga wajan shi? ". Wani magani ya d'akko ya ce, kikira sunanta sau uku, sannan ki sha wannan, harta bar gidan sai abinda kika ce zata rik'a yi, dan haka daga kince ta ta bud'e miki da sauri zata bud'e". Farida da d'i ya ishsheta , kud'i ta kuma d'ebowa ta ba bokan, sannan ta tafi tana mai farincin nasara"..


Farida a cikin mota ta samu su Hajiya Murja suka tafi, gidan Hajiya Bilki. Inda suna tafiya Farida na basu labarin yadda su kai da bokan. Hajiya Bilki ce ta ce, "Ai Farida karki damu tunda kikazo gun kafin gobe..., ai aikinki yagama biya, tun-tuni da muntab'a wannan hirar da Hajiya Murja ai da tuni kin auri Habib angama, nan dai suka ta hirarsu har suka isa gidan Hajiya Bilki inda a nan za su kwana sai gobe zasu wuce".


Haka ko akai, washe gari da wuri su Farida suka kama hanyar Katsina, dan daga inda suka je zuwa airport akwai nisa".


Su Hajiya Murja sai dare suka shigo Abuja, Hajiya Murja ganin dare ya yi , ta tsare Farida ta kwana awajanta".


Washer gari da sassafe Farida ta yi sammakon zuwa gidansu Habib.


B'angaran Hassana ko, tun jiya ta kasa gane kan mutuminta, sai wani irin bacci ya ke, duk yau kuma tun safe yak'i cin komai, tayi- tayi yak'i ci, yana cikin baccin ita kuma lokacin tana kitchen tana k'ok'arin had'a musu dinner ta ji wani irin k'ara wadda sai da k'arra ta firgitata, hakan yasa ta rigo da gudu daga kitchen d'in, ta nufi bedroom d'in Habib, tana zuwa zaune ta iske Habib tsayiyar gado yana dafe da kanshi da hannun wanshi guda biyu, yana jijjuya kan yana rirrintse ido. Hassana na zuwa ta hau kan gadon cikin rud'u da yanayin da taga Habib d'in, Hassana na zuwa ta rik'o Habib d'in tana tofa mai duk addu'ar da tazo bakinta. Can Hassana ta ji Habib ya yi wata uwar gyatsa da k'arfi. Can kuma sai taga ya saki kanshi da hannu wanshi da yasa ya daddafe kai d'in ".

Habib d'ago da kanshi ya yi yana kallan Hassana. Hassana kuma cikin jin dad'in ganin Habib ya bar abinda ya ke, da alamu ya ji sauk'i, ta rungumo shi, ta ce, "Ayyah Oga Habib Sannu ko, tsakanin jiya da yau kana shan wahal...... ".

Hassana tsawar da ta ji ce tare ta turota k'asan da Habib ya yi yasa bata k'arasa abinda ta ke fad'aba".


Allah sarki Hassana bata damu da abinda Habib ya yi mata ba, ta shi ta kuma yi zata hau gadon, Habib ya kuma daka mata tsawa , wadda tafi waccan, ya ce, "Ke ! , wacece ke!?, kuma me kike yi anan? ". Hassana cikin tsoro da al'ajabi ta ke kallan Habib, dan idan taji da kyau sai taji kamar Habib ne yake magana, kuma kamar yadawo hankalinshi abisa ga yadda ya ke maganar............ โœ๏ธ



Tofa wai meke faruwa ne, Habib kamar yadawo hankalin shi nake gani๐Ÿค๐Ÿค๐Ÿค๐Ÿค.


Ga kuma su Hajiya Farida da tarin Magunguna ko ya abin zai kaya???.


Idan kin karanta daure ki yi Comment sister, Comment ke k'aramin kwarin gwiwar update da wuri.



Share
&
Comment please ๐Ÿ™.

๐Ÿ“š OGA HABIB ๐Ÿ“š
๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ
*๐Ÿ…™๏ธŽARUMAI ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ WRITERS ๐Ÿ…๏ธŽSSOCIATION๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ*


https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa๐Ÿ’ช*_

*๐Ÿ’ซ(๐Ÿ…™๏ธŽ.๐Ÿ…ฆ๏ธŽ.๐Ÿ…๏ธŽ)๐Ÿ’ซ*
TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI.

https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7

https://m.facebook.com/groups/565235401564189/

Lale watan alkairi, watan da ummulkairi, Amina zatil fatahi ta haifi d'a al sugaba, lale watan da duka aljanu suke ta ce wa sun bani dan basu k'ara ci gaba.
Yau ne sha biyu ga watan rabu Auwal, wata mai girma mai daraja, watan da fitayyan halitta yazo duniya, Allah kak'ara mana k'aunar annabi Muhammadu (S, A, W).
Happy maulud.





Shafi na 48&49.



Hassana cikin murna da manta waye Habib, ta kalli Habib, tana mai k'okarin k'ara hawa gadon, ta ce, "Wayyo Oga Habib ka warkene ko ko magana ce ta samu? ". Hassana ta fad'i maganar tana mai saurin rik'o hannun Habib d'in. Habib ko da al'ajabi ya bi Hassana da kallo".

Hassana ganin haka, yasa ta d'an girgiga Habib ta ce, "Wayyo Oga Habib kafara magana ko? , dan Allah ka ce wani abu, ko zanji dad'i".
Habib da ke zaune yana jin maganganun Hassana mamaki ne sosai ya cika shi, wanda yasa ya kasa cewa komai, hakan yasa yafara tunanin wai lafiya ko dai mafarki ya ke, idan kuma mafarki ne tom wacece haka tazo mai da siffar da bai sani ba".


Hassana ko ganin Habib ya yi mata shiru yana kallanta, yasa ta kuma kai hannu da niyyar ta girgiza shi. Wani ma haukacin mari Habib ya wanke Hassana dashi yana mai sake turota k'asa, ya ce, "Wacece ke?, kuma me ya shigo da ke nan? ". A hankali sosai Habib ya ke maganar.
Hassana da marin Habib ya farkar da ita ta dawo hayyacinta, da fe inda Habib ya fareta ta yi, tana kallan shi da idonta da ya kad'a ya yi ja".

Habib ko cikin d'an d'aga murya ya kuma cewa, "Fita ki bar nan kafin inyi k'asa-k'asa da ke! ". Still Hassana na tsaye dan ko motsawa bata yi ba, daga inda ta ke. Take Hassana ta shiga wani hali mai wuyar fita, dan indai dai-dai ta ke gani, kuma jinta ma dai-dai ya ke, tom tabbas Habib ya samu lafiya, dan ko daga kalar kallan da yake mata, hakan ya tabbatar mata Habib ya dawo hayyacinsa".


Habib ko ganin Hassana kamar bajin abinda ya ke cewa ta ke ba, sakkowa ya yi daga kan gadon, ya na kallan Hassana cikin ido, ya ce, "Wacece ke?, kuma me yakawo ki nan?, nace ki fita ko! ". Hassana cikin rawar murya ta fara magana, da cewa, "uhm ba komai". "Ba komai ".Habib ya mai-mai ta. Hassana d'aga ma Habib kai ta yi, ta ce, "Eh".

Kasan cewar rashin k'arfin da Habib ba ya ji ajikin shi koka d'an, dan ji yake kamar zai fad'i, dan ko maganar da yake ma Hassana da kyar yake mata ita, hakan yasa batare da Habib ya kuma cewa komai ba, ya nuna ma Hassana k'ofar fita da hannu, shi kuma ya koma bakin gadon ya zauna yana mai dafe kan shi".


Hassana juyawa ta yi ta kama hanyar fita bedroom d'in Habib, har ta kai bakin k'ofa ta juyo ta kalli Habib d'in da yake dafe da kanshi yana rirrin tse ido. Hassana da sauri ta dawo cikin bedroom d'in, dan ita har yanzu bata gama yadda Habib ya warke gaba d'aya ba. Hassana cikin damuwa da yanayin da taga Habib d'in ta kamo hannun Habib d'in ta ce, "Ayyyah Oga Habib Sannu, nasan yunwa kake ji, inda yau kak'i cin komai, in kawo ma abinci kaci? ". Habib da mamaki ya d'ago kai yana kallan Hassana, gashi abin haushi yana jin kamar baya iya magana, tsananin ciwan da kanshi ya ke. D'agowar kan da Habib ya yi Hassana ta kalli k'wayar idon shi ta ga ta yi jawur. Hassana cikin tausan Habib d'in kamar zatai kuka, dan ita harga Allah bata mai kallan wanda ya warke gaba d'aya, kawai dai tana mai kallan ciwan nashi ya canza sifiri ne. Hakan yasa Hassana ta kuma cewa, "Oga Habib in kawo ma abinci ko? ". Hassana ganin Habib ba amsa mata zai yi ba, yasa ta rabu tashi ta je kitchen ta zibo mai jolop rice d'in da ta yi, ta kawo mai, dan dan tun jiya take fama da Habib akan cin abinci yak'i".


Hassana kusa da Habib ta zauna ta d'ibo abincin a spoon, kamar yadda ta saba yi ma Habib d'in wani lotun, ta ce, "Oga Habib bud'e bakinka please kaci ko kad'an, kaga tun jiya baka ci abinci ba". Habib ko da ciwan kai ya dama, da mamaki ya ke kallan Hassana ga magana ma wuyar yi ta ke mai. Haka nan Habib cikin k'arfin hali ya ce ahankali canciki, "Kin san Allah idan har biki bar d'akin nan ba, na tashi,,,,, ". Habib ya k'arasa maganar da girgiza kai". Hassana aje abincin ta yi, tana mai k'ara gasgata maganarta ta Habib ya warke. Hakan yasa Hassana aje mai abincin ta juya ta fita. Hassana wayar da Hajiya Turai ta bata ta d'auka, ta kira Hajiya Turai, Allah ko ya tai maka, kira d'aya Hajiya Turai ta d'aga".

Hasssana cikin murna, ta gaida Hajiya Turai, bayan sun gama gaisawa ne, Hassana ta ce, "Mommy Wallahi Oga Habib ya warke,yanzu haka maganar da nake yi dake Oga Habib na magana". Hajiya Turai cikin tsantsar farinciki ta ce, "Daughter nasan ba kimin wasa, dan Allah da gaske Habib d'ina ya warke?, kuma har kinji maganar shi? ". "Mommy Oga Habib ya warke tabbas, kuma naji maganar shi". Cewar Hassana. "Tom me yace miki, daughter? ". Hassana shiru ta yi, dan sai yanzu ne ma taji zafin abinda Habib ya ce mata".

Hajiya Turai ko jin Hassana ta yi shiru ya sa, ta ce, "Hello daughter kina jina, kuwa, ba Habib d'in wayar". Hassana koma wa bedroom d'in Habib ta yi, har yanzu Habib na

20 / 41