Author : Faddy baby Category : Romance
ta bi bayan shi. Billy ko da mamaki ta bi su da kallo, baka mar abinya yafi d'aure mata kai ba, ganin Habib ya ba Hassana ATM card d'in shi".
Hassana ko a hanya ta sa Bilya ya tsaya ya cirar masu kud'i, sannan suka biya suka sai duk wani abu da suke buk'ata. Hassana na zuwa ta shiga kitchen ta fara girki, ta ce," coconut rice zan yi irin wadda mu kai practice jiya. Cikin k'ank'anin lokaci Hassana ta gama duk abinda ta ke yi, sannan ta had'a masu lemun kwakwa, masha Allah. Ta jera komai a derning space. Bayan Hassana ta gama ko mai ne, ta shiga wanka, ta sa doguwar rigar da Hajiya Turai tai mata ta shadda, sanna ta samu Bilya a waje, suka tafi wajan makeup d'in ".
Bilya da kanshi ya ya yi magana da su akan ai mata mai kyau. Wayyo sister haka suka zauna suka cancara ma Hassana kwalliya. Wajan sa eyelashes ne aka samu matsala, dan Hassana cewa tai bata so, da kyar dai ta bari aka sa mata.sannan zuka amshi d'an kwalin suka d'aura mata".
Wato had'uwa iya had'uwa Hassana ta had'u, dan shi kanshi Bilya da Hassana ta fito da kyar, ya samu ya kauda idon shi akanta, azuciyar shi kuma yana ganin sakarcin Habib, ya ce, "wai kawai kasa matarka tai ma abokanka kwalliya kawai dan kar a raina ka,Allah ya kyauta ".kiran Habib ne ya katsema Bilya zan can zucinsa".
Bayan Bilya ya d'aga, Habib ya ce, "Bilya sun fa iso kun koma gida ne". "Eh gamu a mota zamu koma". Habib datse kiran ya yi, dai-dai nan kuma su Faruq suka shigo Sanat yughurt ".
Habib da fara'a ya rirrin gume su, zai yi Office d'in shi da su, Faruq ya ce, "Kai Malam gidanka za ka kai mu". Habib murmushi ya yi, sannan yaja Office d'in ya rufe, dama tun Kafin su iso Habib yasa an kawo mai mota agida. Habib da kanshi ya tuk'a motar zuwa gidan shi".
B'angaran Hassana ma kusan zuwan su kenan taji alamun hayanir zuwan abokan Habib d'in. Hassana bedroom d'in ta ta ruga. Su Faruq ko da fara'arsu suka shigo falon".
Bayan sun zauna , Faruq ya kalli Habib ya ce, "Kasan nifa banda dauriya, ina amarya?, na zaci ita zata tarbemu, ko dai kasa ta gudune". Faruq ya fad'i maganar yana dariya. Dan yau ya shirya rama duk abinda Habib ke musu akan duk budurwar da suka kawo mai, yadda ya ke kyarar su, daga ya ce bata da kaza sai ya ce, bata iya kwalliya ba, abubuwa dai Kala-kala ".
Habib tsaki ya yi, ya ce ma, "Faruq, tom bari kaji ko kad'an bana fargabar ku ganta, saboda ita d'in ba zab'ina bace kamar yadda na cema, zab'in Mommy ce, dan haka sai ku taya ni fad'ima Mommy ba ta yi ba, dan na riga ku fad'a, ya idasa maganar yana yin hanyar bedroom d'in Hassana".
Hassana zaune kusa da mirro sai kallan kanta ta ke, dan in dai mudubin nan ba k'arya ya yi mata ba, ta yi ma kanta kyau sosai ".
Ta mirro Hassana ta hango Habib, aiko da sauri ta sa hannu ta rufe fuskar. Habib ma da sauri ya idasa gunta ya sa hannu ya janye hannunta, ya ce, "Da Allah can zaki b'ata kwalliyar, ni cire hannun ki in gani ta yi kyau". Hassana cire hannunta ta yi ".
Habib ya kai minti biyar yana kallan Hassana. Dan shi dai in dai ya lura da kyau, sai ya ga kamar kwalliyar ta yi. Hassana bud'e idon ta ta yi da ke arufe, bud'ewa ta yi tana kallan Habib ta ce, "Kwalliyar ta yi kyau? ". "Friend's d'ina zasu tantance hakan, bani ba".Habib ya ba Hassana amsa. Sannan ya kamo hannun Hassana ya ce, "Meje su ganki suna falo".
Haka Hassana suka jera da Habib hannunsu cikin na juna, suka nufi falon. Faruq da sauran abokan tafiyar nasu, fira suke, amma suna ganin Hassana dukkansu bakinsu ya mutu, dan sosai kyanta ya tafi da imanin su. Jameel ne ya yi k'ok'arin sai ta nazuwar shi, ya ce, "Barka da fitowa Amrya". Sannan su Faruq ma suka dawo na tsuwar su".
Faruq yana d'an soka kai ya ce, "Barka da fitowa amarya agi dan Habib, gaskiya kin ciri tuta, ace duk gudun shi sai da kika cin mai, jinjina Amarya". Hassana da ke zaune kusa da Habib murmushi ta yi, ta ce, "Barkanku da zuwa, da fatan kunzo lafiya? ". "Lafiya kalau amarya". Cewar Usman Kenan". Bayan sun gaggaisa ne, Hassana ta kalli Habib ta ce, "Oga Habib ga abincin su a darnin area, ko akawo nan". "To fa Oga Habib, kunji wani love name". Cewar Faruq yana dariya". Habib ne ya amshe zan can Kafin su Jameel su tanka, ya ce, "Da Allah can kuzo muje kuci abinci, kun tsaya kuna gulma".
Habib tasa su Faruq ya yi har derning space d'in, Hassana zuwa tai ta zizziba abincin a plate hud'u ta aje ma kowa a gaban shi, sannan ta aje jug d'in lemun kwakwa da tai masu, sannan tabar gun tana mai cewa, "aci lafiya".
Tun kan su Faruq suci abincin k'amshin da ya ke yi kad'ai ya tabbatar masu abincin ya yi. Wayyo dad'i haka suka ci gaba da ci ba ma mai kowa magana. Faruq bayan ya gama cinye wanda Hassana ta sa mai, mik'ama Habib plate d'in shi ya yi, ya ce, "Ni dai idan akwai Habib k'aramin, Wallahi ka yi da ce, yarinyar ta yi ga shi ta iya girki, wato Habib naso ace yau in huce fushina akan abubun da kai mana da, amma matarka bata da abinda zan rama abinda kai min, tabbas Hajiya ta cikama burinka da kace sai First class baby zaka aura, wannan yarinyar ta kai, wai ya sunan ta ne? ". Habib yana mai jin dad'in kunyar da Hassana ta fidda shi, ya kalli Faruq ya ce, "Sunan budurwarka da ta rasu". "Kana nufin sunanta Hassana? ". Kai Habib ya jinjina ma Faruq".
Tabbas ba a Hassanar banza, gaskiya ne dole ta zama kyakkyawa, dan kasan Allah ban tab'a ganin Hassana munmuna ba, duk inda zaka gansu zaka ga suna da diri, Allah sarki Allah ya gafarta ma Hassana". Cewar Faruq cikin damuwa. "Ameen ". Habib ya ce".
Nan dai suka kama cin abincin su suna santi. Bayan sun gama cin abincin ne, Faruq ya kalli Habib ya ce, "Habib end of this month ne fa bikin Jameel, yanzu haka yana daga cikin abinda ya kawo mu, dan haka sai ka shirya muje gidansu Yarinyar tare, dan yau d'in nan zamu juya". Habib tashi ya yi, ya ce, "Tom ku tashi muje ". "Ok, kira Hassana sai muyi sallama". Cewar Faruq ".
Habib bedroom d'in Hassana ya shiga ya kirata. Hassana zuwa tai ta ce, "Ba dai har zai ku wuce ba? ". "Wallahi amarya tafiya za muyi, zamu dawo babu dad'ewa auran Jameel". Kud'i masu yawa suka ajema Hassana a darning d'in, sannan suka tafi".
Bayan sun tafi Hassana tazo ta gyara gurin. Habib ko bashi ya dawo ba sai gaf da magriba. Lokacin Hassana na kitchen tana ma Habib kunu. Habib na zuwa side d'in shi ya shige, yana zuwa ya yi wanka, ya tada sallar magariba. Habib sai da ya yi sallar issha'i sannan ya fito falon. Lokacin Hassana bata falon. Habib guri ya samu ya zauna, yana nan zaune Hassana ta fito zata nufi kitchen d'akkoma Habib kunun shi dama wajan shi zata".
Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Zo". Hassana ci gaba da tafiyarta ta yi tai kamar bata ji ba. Habib da d'an k'arfi ya ce, "Ke bada ke nake ba". Hassana zuyowa ta yi, ta ce, "Oga Habib nifa ba Sunana ke nan ba". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Zo ki zauna nan? ". Ya nuna ma Hassana kusa da shi". Hassana dawowa ta yi ta zauna inda Habib ya nuna mata, ta ce, "Oga Habib gani".
Habib kallan Hassana ya yi ya koma hannun ta ya ce, " HaK'ik'a Kin fiddani kunyar Friend's d'ina naji dad'i sosai, dan haka ki zab'i duk abinda kike so, zan miki? ". Hassana bata san sanda ta tashi tsaye ba, ta ce, "Oga Habib kace duk abinda nake so? ".
Kai Habib ya d'aga ma Hassana. Hassana zama ta yi tana kallan Habib, ta ce, Oga Habib so nake ka ban matsayin Supervisor..... .. ✍️
Idan kin karanta daure ki comment sister 🤝
Share
&
Comment please 🙏.
📚 OGA HABIB 📚
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*
https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby).
https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7
https://www.facebook.com/groups/301023561618950/
Shafi na 70&71.
Kai Habib ya d'aga ma Hassana. Hasssana zama ta yi tana kallan Habib ta ce, Oga Habib so nake ka ban matsayin Supervisor ". Hassana ta fad'i maganar cikin k'osawa. Habib kallan Hassana ya yi ya ce, "kamarya in baki matsayin Supervisor,bangane ba, yi min bayani? ". Hassana k'ara gyara zama ta yi, sannan ta ce, "Oga Habib nufina ka sauke Billy a matsayinta kaban". Kai Habib ya girgizama Hassana ya ce, "Haka ba zai yuwu ba, ki canza wani abun". "Tom kaban manager ". Cewar Hassana ".
Habib dariya ya yi, jin abinda Hassana ta ce, wai ya bata manager. Hassana tsayawa ta yi, tana kallan Habib, dan bata tab'a ganin shi yana dariya ba. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib dama kana dariya? ". Hassana ta fad'i maganar tana turo baki dan ta san ita yake ma dariya dan ta ce, ya bata manager".
Habib bayan yadan dara, kallan Hassana ya yi, ya ce, "kin ban dariya, me zaki da matsayin manager?". "Tom ai ni matsayin nake so, kuma ai kai kai min alk'awari kace duk abinda nake so, dan haka ni babu abinda nakeso wanda ya wuce, haka". Cewar Hassana tana turo d'an mitsitsin bakinta". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Kizab'i wani abun zan miki, amma banda wani abu a Sanat yughurt". "Ni dai acan nake so". Hassana ta fad'i maganar cikin shagwab'a".
Habib tashi ya yi, ya ce, "Shikenan kin rasa, ni kam bazan miki wannan ba". Habib na fad'in haka ya tashi ya nufi bedroom d'in shi".
Hassana da sauri ta tashi itama, tabi Habib tana rik'o hannun shi, ta ce, "Dan Allah Oga Habib kai fa kai min alk'awari!,". Hassana tana rik'e da hanun Habib tana mai magiya har suka shiga bedroom d'in shi. Habib zama ya yi, bakin gadon Shi, Hassana ma ta zauna tana mai k'ara cewa, "Oga Habib dan Allah kaban". Habib gaba d'aya baya jin dad'in yadda Hassana ke mai, shiya ya koma bedroom d'in shi, ya zaci bazata bishi ba. Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Ki je ki kwanta, gobe sai muyi magana". "Wayyo Allah na Oga Habib, Allah ni bazan iya bacci ba, dan Allah kafad'amin yanzu". Habib kwanciya ya yi, ya rufe ido kamar mai bacci, dan bai san me kuma zai kuma cema Hassana ba". Hassana ma kwanciya ta yi, gefan Habib tana kallan shi, ta ce, "Oga Habib bacci kake? ". Habib juyawa ya yi batare da ya tankama Hassana ba, ya juya mata baya".
Hassana ma juyawa ta yi side d'in da Habib ya juya, ta ce, "Oga Habib dan Allah". Hassana ta fad'i maganar tana mai kara shigema Habib". Habib bud'e ido ya yi yana kallan Hassana, ya ce, "Banda lafiya ki je ki kwanta gobe zamu yi magana". Habib ya fad'i maganar da sanyi sosai".
"Ayyah sannu Oga Habib, Allah yabaka lafiya, tom kace Eh kawai dan Allah sai in tafi". Habib tashi zaune ya yi, ya na kallan Hassana , sannan ya ce, "Shikenan ki zama ma taimakiyar manager". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "da shida Supervisor wane ya fi? ". "Naki yafi". Habib ya ba Hassana amsa". Wayyo Hassana dad'i kasheta. Rungume Habib ta yi tana mai jin dad'in matsayin da Habib ya bata. Ta ce, "Wayyo Oga Habib Nagodeee". Hassana sakin Habib ta yi, ta tashi ta fita daga d'akin".
Habib ko runtse ido ya yi, jin shi cikin wani bak'on yana yi. Yana mai jin sanyi cikin k'ofofin ji kinshi. Habib na nan yadda Hassana ta bar shi, Hassana ta shiga rik'e da jug d'in kunun Habib. Hassana cikin sanyi ganin Habib d'in kamar bai da lafiya da gaske kamar yadda ya ce, dan taga kamar yana ciccije baki, ta ce, "Oga Habib ga kunun ka, ka tashi kasha". Habib banza ya yi da Hassana sai da ta sake maimai tawa, sannan ya ce, "ki aje, kije ki kwanta idan na tashi zan sha". Hassana aje cup d'in kunin ta yi, sannan ta hau gadon, ta ce, "Oga Habib baka da lafiya ne? ". Habib cikin fad'a ya ce, "Ban sani ba, tun d'azu bikiji abinda nace bane, ki tashi kije ki kwanta! ". Hassana da sauri ta tashi tun Kafin ta idasa k'ure shi, dan tunnuni ma ta zaci zai mata haka".
Habib ko bayan fitar Hassana tashi ya yi ya je ya watsa ruwa, ko zai ji shi ya dawo yadda ya ke da. Bayan ya fito kunun da Hassana ta kawo mai ya samu yasha sannan ya kwanta yana ta juyi shi ka d'ai, ahaka dai Allah ya tai ma kai bacci ya kwashe shi".
Washe gari Hassana duk yadda taso ta tashi da wuri sai da ta makara, hakan yasa ta hak'ura da yin abin break fast, ta yi wankanta kawai tashirya. Hassana ta fito zata tafi Habib ma ya fito, Hassana cikin jin dad'in ganin Habib d'in ya ji sauk'i, ta gaida shi, tare da cewa, "Oga Habib kaji sauk'i kenan? ". Habib banza ya yi da Hassana, Hassana kuma kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib kura gemin hanya mana dan Allah ". "Akan me?, kije ki hau abinda kike hawa ya kai ki". "Ayyah Oga Habib kaga fa gidanmu d'aya dan Allah ". Habib banza ya yi da Hassana dama sunzo dai-dai motar shi, ya shige, Bilya ya ja zasu tafi, Habib ya ce yana zuwa ya yi mantuwa. Habib gida ya koma ya d'ako abinda ya manta. Sannan ya dawo suka tafi, tsaye suka iske Hassana tana jiran Napep. "Tsaya" Habib ya ce ma Bilya, bilya tsayawa ya yi,Habib kallan Bilya ya yi, ya ce, "Yi mata magana, tazo mu tafi".
Bilya sauka ya yi ya nufi inda Hassana ta ke tsaye. Ita kuma Hassana dama koda tai ma Habib magana akan yarage mata hanya ta yi mai ne, saboda idan shine tasan za tafi zuwa da wuri, kuma yau tana son taje da wurine dan ta fara cika aikinta yau, tana kuma addu'ar Allah yasa ta riga Farida zuwa, wannan ne da lilin da yasa Hassana ta rok'i Habib ya rage mata hanya".
Hassana na tsaye tana jan tsakin burinta ba zai cikaba, taji maganar Bilya, yana cewa, "Amaryar Ogan mu, ya ce, aimiki magana kizo mu tafi". Hassana hararar Bilya tafi sannan ta bishi suka tafi".
Hassana kusa da Habib ta zauna, tana kallan shi, ganin ya d'auke idon shi ya yi kamar bai san da ita ba, yasa itama ta yi banza da shi. Ahaka suka isa babu wanda ya yi ma kowa magana. Hassana na sauka da sauri ta yi ciki dan tana so taje ta gani Ko su Billy sun rigata zuwa".
Habib da mamaki ya bi Hassana da kallo yana mamakin saurin da take yi. Hassana ko na zuwa ta iske Billy ta zo, a wayance Hassana ta duba, ta ga Farida bata zo ba".
Hassana tafi hours biyu da zuwa sannan Farida ta zo. Hassana da ke zaune tana jiran zuwan Farida, Farida na zuwa Hassana ta tashi ta isa gunta, wani kallo Hassana tai mata, sannan ta ce, "dama wannan lokacinne ake zuwa Aiki? , tom ko mai Sanat yughurt tun d'azu yazo Aiki, dan haka bazamu laminci haka ba, mun baki suspection na One week, dan haka zaki iya komawa gida, nan gaba idan kika k'ara aikata haka, korarki za muyi". Farida tsabar al'ajabi ne ya hanata magana, kallan Hassana kawai ta ke, tunani Farida ta fara, tom ko anba Hassana wani matsayine, wata zuciyar ta ce mata, tsabar rainaki ne da tayi, ta yi ma Supervisor mana. Farida a zuciyarta ta ce, "Tabbas yau zakici ubanki, yau zaki tabbatar ni ba sa'arki bace"., Farida juyawa ta yi zata shiga ciki, "Hassana ta ce, "Zaki iya jama wadda kika shiga gurinta itama". Farida bangaje Hassana ta yi tashige ciki".
Farida Office d'in Supervisor ta shiga,Farida cikin damuwa ta ce, "Supervisor anba yarinyar nan wani matsayi ne? ".Supervisor kallan Farida ta yi, ta ce, "Wata yarinyar kuma? ". "Wata yarinya fa in ba Hassana ba! ". Cewar Farida ".
"Ai idan za aba wani matsayi a Company nan sai anyi meeting, da an bata da ke ma kin sani ai, ". Cewar Billy. Shiru Farida ta yi, sannan ta ce, " ke dai kikira manager muji, dan baki ga yadda tai min magana ba, wai ta dakatar dani na sati d'aya, kuma idan na k'ara ai kata haka korata za tai". Billy cikin masifa, kamar ita Hassana ta ce ma haka, ta ce, "Bari mu kira Manager awaya, yau dama ya ce min ba zaizo da wuri ba, amma inda ko karya take Wallahi yau sai ta san ita k'aramar mara kunya ce".
Billy kiran manager awaya ta yi, manager na d'agawa, bayan Billy ta gaida shi, ta ce, "Dama dearie naki raka ne in tambayeka, na ce anba Hassana matsayine agunnan, naga sai zuba iskancinta ta ke son rai". Manager ko tsabar dad'in dearie din da Billy ta kira shi da shi, ya sa ya ce, "Ki bar wannan yarinyar kawai zanyi maganinta, duk dan akwai auran