Author : Queen Safiyyert Category : Romance
mishi da ido kan ya
cigaba da gashi. "A'a Batool, wallahi kin girmi
hakan, kinsan fa ina kaunar ki, believe me... Sai
yasa hannu a wuya halamar ya rant'se, tuni sai
ta fara hawaye, da zummar samun nasara ya
kara k'allon Ahmad, da halamun d'ai shi ya kit'sa
mishi komai. Sai Fure ta k'alleshi da tuhuma tana
k'anne ido d'aya, da sauri ya daga kafada
halamar ba ruwan shi. "A'a, g'wara ka auro mai
haihuwa,, kaga k'wanka kaima a duniya koh? Ni
kuma banni rai.. Kawai sai ta fashe da kuka. Da
sauri ya matso ta kara ja da baya.. " A'a Fatee,
gashi ai Allah ya bamu, kiyi hakuri nayi kuskure..
Sai ya k'allo Ahmad da ke girgiza kai halamar ya
k'wafsa, bai aune ba ya ji ta doko kofar. Bugo ya
fara akan ta bud'e dan Allah, tana kuka tace dan
ciki yazo ba dan ita ba, kuma ciki nata ne ya tafi
kawai. Yin duniya taki bud'ewa. Dak'yar yabar
gun Ahmad ya jashi suka fita, "gaskiya kai su6ul
d baka, sai da nace kar ka nuna mata kasan da
cikin nan, za ta d'auka shi ya kawo ka. Kai ya
dafe, "toh ya zanyi? Wallahi ni Fatiman ce d'uk
ta ban tsoro,sam bamu ta6a haka da ita ba.
Dak'yar yace ya dawo gobe kan sun shawo mishi
kanta. Sai bayan isha'i ta bud'e dan yunwar
cikinta. Fure na parlour, harara ta sau wa Furen,
kan ta zauna, "yi hakuri, ga nan abincin ki kici,
k'allota tai, "baga nan irin halin mazan da nake
fad'a ba, sarakan san kan tsiya, Allah ya kaimu
gobe da safe ku ga. Ita dai Fure murmushi kawai
take. Washegari bak'wai da rabi a gidan ta mishi,
Ahmad ya dawo a jogging ya tarar da mutum a
kofa. Sai ya jinjina kai,lalle Fatee ta kunno wuta.
Matar da ta gama shirin tafiya sai gata ta bingire
da bacci,har d'akin Ahmad yace ya bita, ganan
jaka ta had'a tai "ready". Gadon yaje ya zauna a
kusan ta cikin sand'a, tana t'saka da bacci taji
ana kamar shafa mata mara, da sauri ta bud'e
ido, tana ganin shi ta sau kara tun k'arfinta, da
sauri yasa hannu ya rufe mata baki,batai wata
wata ba ta gant'sara mishi cizon da ba shiri ya
cire hannun, "waya baka izinin shiga d'akin
jama'a? Cikin jin zafin hannu yace "ban sani ba
d'in,, kofa ta nuna, "toh fita, matsowa ya fara,
"ba inda zan fita fa, mai gidan yace in shiga.
Ganin yana kara matsowa yasa ta fara duben
abin duka,kasa ta s'akko da filo a hannu,"kar ka
matso nan, tsayawa yai, kan ya kara zubewa,
"toh kiyi hakuri, wallahi na tuba, harara ta sakar
mishi, "kai kasan wannan, ganin ta ki da lumana
shima ya fara fad'a, "dole ki koma, a tunzure tai
parlour tana "toh sai naga dolen, kawai sai yaja
mata jakar chan, "haba Fati.. Ganin su Ahmad
yasa yai shiru, "Dan Allah ku bata hakuri.
"Fatima kiyi hakuri, d'uk dan Adam yana da
hakan, amma ki duba yai nadama, Fure ta k'allo
wace ke magiya,"bai ba wallahi, Ahmad
yace"yayi man Fati, kawai sai ta sa musu
kuka,nan suka had'u suna bata hakuri,komai
sukace Salman sai yai kalar tausayi yace ''na
daina. Sai ga Fatee ta fara kukan shag'wa6a, su
Fure sukai d'aki suna leken su, tun in ya mat'so
tana ture shi har ya runkomota t'sam, sai kuma
yace mata yunwa yake ji, kai suka k'ada, "lalle
Fatee matsala, cewar Ahmad. K'allonshi Fure tai,
sai suka rufe d'aki suna dariya. A ranar suka
d'inke t'saf da Salman d'inta. Da zasu tafi suka
shige d'aki da Fure, dariya take mata kan ta
g'wara bawan Allah, "Hmm,bazaki gane ba, ni
nasan mey nasha a baya ai, sai d'ai wallahi har
na haihu ba mai gani na a dangin shi, amarya
yasan inda zai kaita ba a gida na ba. "Na haihu
kuwa, in kika cire Umma.. Toh ba d'an uban da
zai d'au d'ana wallahi, dariya Fure take, "a
assasauta d'ai, tace "za ki gani ai.
************************ Sadakin Maryam aka kai,
d'uk Wa'inar nan da ake toyawa sam Hassana
bata ji ba. Anan yayan su Ahmad ya fallasa
Momy taji wai K'anwar Fure aka kaiwa, nan ta
tada tsiya. Kan wallahi in dai za'a auro Maryam
toh Sai an auro Rukayya. Takanas Momy ta
Wanki K'afa har gidan Fure ta kare mata tass!
Wato wai so take ta gaje musu dangi da t'siya?
Toh tasan da saninta, indai har ta yarda auren
Muh'd ya faru da Maryam, toh wallahi itama
Rukayya sai ta shigo mata.. Da sauri Fure ta
rint'se ido hawaye ya zubo. Tab,ana wata ga
wata. Tunda har Momy ta rant'se toh k'wa tasan
Rukayya ta shigo ta gama... Hannu ta d'aura aka
hawaye na zubar mata, a hankali ta furta "wayyo
ni.. tama kasa koda ihu ne taji dad'i,kukan ma
sai hawaye, koh wata biyu ba ai da kashe "case"
d'in Fatee ba ga nata ya d'anno. By Feenat
Ja'afar. 庐NWA Feenat.mywapblog.co
9/29/16, 2:41 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
36_Tamkar mara lafiya haka tai lamo akan
kujera,har maigidan ya dawo, sam shima bai
shigo da walwala ba, sai d'ai yana ganin Furiin ya
rikice mata. Dan yanzun daga gidan yake Momy
ta sanar shi tazo, ga yaje gun Abba,Abba yace
tunda an nace abu kusan shekara nawa kawai ya
hakura ya aure tan, dama bai bi takan mama ba,
dan t'saf yasan abinda Momy tai agun ta ido ne.
"Pretty... Ido kawai ta zuba mishi, sai ya dago
ta,d'uk ta sau mishi jiki k'allo ne nata, tuni sai ya
tsorata, da k'arfi ya jijjiga kafad'unta "Furera... A
firgice ta k'alloshi,cikin sanyi tace "uhmm.. Suna
had'a ido ta barke mishi da kuka.
Juyin duniya Fure taki d'aina kuka, kawai sai ya
sa mata ido shima kamar zai sau kukan.
Jijjiga kafad'unta kawai yake halamar rarrashi
yana share mata hawayen,sai d'ai yana goge wa
wasu na zubowa, kawai sai ya d'auke ta tuni ta
damke ido tana cigaba yai d'akinshi da ita,
"bathroom" ya shiga,ya cika "bathtub" da ruwa,
sai ya bar kofar a bud'e, tana t'saka da kuka ta
jita cikin ruwa.
Da azama ta bud'e idon,ya k'ada yai jajjajir tana
k'allon shi, tuni shima ya fara ko'k'arin shiga ciki,
kawai sai ta kara jiniya tana dan bubbuga ruwan
da shura K'afa.
Shiru kake ji Fure, kuka ya kare. Shi kad'ai yasan
"week points" na prettyn shi, dan ka burkita mishi
ita da kanshi zai samo kanta, gashi yanzu harda
waka kamar ba ita ce dazun ba.
Shi kam yana a bak'in gado yana k'allon yadda ta
zubo da gashi ta gaba tana gogewa da "towel"
daure da wani, tare da wakar "mayafi na bargo
nah.. Sai murmushi yake.
Da hannu tasa tai baya da gashin fuskarta ta
baiyana,mutumin kawai ya zuba mata na mujiya.
"Towel" d'in ta hulla mishi a fuska, tuni ya shaki
kamshin "shampoon" jikin na "vatika" yana
lumshe ido,cire wa yai da zummar hulla mata ta
kawar da kai tana murmushi.
Bata aune ba taji ya janyo ta gaba d'aya suka
suka zube suna dariya.
"Wallahi ki tada musu hauka na fad'a miki, tuni
zance zaisha ban-ban, cewar Fatee da suke
waya.
"Hmm, sis Fatee bazan iya ba, in fa wani yaci
riba,wallahi wani duka zai ci, kar ki manta a
gidan su fa take? Babbar riba ta yanzu na samu
Maryam ta shiga gidan Hassana, wallahi ko
Rukayya tazo naci riba.
"Bari banja da ikon Allah ba, amma in dai kece
Furera Muh'd, Matar Ahmad AAA, wallahi
Rukayya sai d'ai gani da ido t'sakaninta da Mijin
ki.
Ki rubuta ki ajiye, bana ke zakiyi "wining" a
wannan "battle" d'in, InshaAllah daga wannan
karan kin zamarwa Momy ciwan ido,kin zama
k'arfen K'afa, InshaAllah ke da AAAn ki
TAKALMIN KAZA ne.
Ajiyar zuciya tai, sam ta ma sa a ranta Rukayya
fa ita ta shigo ta gama, amma bata isa ja da Sis
Fatima ba, yanzu sai ta hau mata.
"Amin toh, yanzu ma haka ina gida gun shirye-
shiryen bikin Maryam d'in, Fatee tace "ita
Maryam taji zancen? Kai ta k'ada mata, "mutum
d'aya yasan auren Maryam shine fansar zuwan
Kishiya ta ba...
"Sis wallahi ji nake kamar zuciya zata fashe in na
tuno AAA za'a d'aura mishi aure da RUKAYYA.
"Ina matukar son Mijina, shima yana sona, ance
ba'a "BA'A YABON DAN KUTURU" wai sai ya
girma da yat'sa.. "Believe me.. Na aminta da AA,
dan shi ya so ni a yadda nake, gashi yanzu ya
fiddo ni cikin jama'a.
"Sis Teema ya zanyi na rage kishi pls... Buh ki
d'aina k'wantar mun da hankalin kishiya bazata
zo ba, ki barni na zama "ready'' dan t'ar6ar ta.
Shiru Fateen tai, wallahi bata tara sani ga Allah
ba, amma a jikinta take jin tabbas auren nan ba
mai yuwa bane.
Sai dai ya ta iya, kawai sai ta hau lallashinta kan
tai hakuri tai ta adu'a in da alkairi toh.
Kamar Yarinya haka ta sau kuka a d'akin su
Maryam lokacin da suka kare wayar.
Hawaye Maryam ta goge, wacce tazo d'aki d'an
nuna wa Furen gadon da su Ada suka za6a
achan t'sakar gida.
Ba koh sallama ta shiga d'akin, da sauri Furen ta
hau goge hawayenta.
Zama tai tana k'allon fuskarta, sai Furen tai kasa
da kai kamar marar gaskiya.
"Ya Furera kishiya za'a miki amma ba wanda ya
sani? Kai ta dago tana k'ada mata, "toh mey
yasa zaki zabi ki muzgunawa kanki dan kawai jin
dad'in kanki da nawa? Kai Furen tai kasa dashi,
kawai sai Maryam d'in ta tashi tai waje, sai ta
d'aura bayanta.
"Umma! Umma!!.. Cikin shesshekar kuka take
k'wala mata kira, tana zuwa ta wat'sar da hoton
gadon kasa, d'ai-d'ai Fure ta taho,
"Lafiyar ki kuke kuka?
Kawai sai Maryam d'in ta k'ada kai da takaici,
"ku zama sheda toh Umma, na fasa auren nan
wall... Da sauri Fure ta rufe mata baki tana
girgiza kai.
Ture hannun tayi tana hararar Furen, "bari kiji
Fure, wallahi nafi k'arfin ai "playing" wannan
"game" d'in dani daga ke har har dangin Muh'd
d'in..
Fad'i take ita kam sam bazata d'au wannan ba,
tun wuri yazo ya debi sadakin shi ya ware, ita
za'a rai nawa hankali?
"Mai suka maida ki? Sakaryar da baki san abinda
kike ba ko mai?
da har za'a fanshi aure na da kishiyar ki? Kai ta
k'ada tare da rike k'ugu.
Da taga suna bata hakuri ma tai waje, ba ita ta
dawo ba sai da taji kiran Muh'd yana sanarta
yazo.
Ba jima wa ta karaso, wankin babban bargo ta
rufe ido tai mishi, sannan ta jaddada mishi ba ita
ba auren shi, dan sunfi k'arfin cin zarafi.
Gaba d'aya yai mutuwar t'saye jin masifar
Maryam, har ta shige gida kamin ya farga fara
t'sayarta.
Wasa-wasa d'ai Maryam ko waya ta d'aina amsa
nashi, ga a gidan kullum kuka, barin ma da taji
irin cin kashin da dangin ke ma Fure, mamakinta
d'aya "wai shin ina masifar Fure tayi? Ina
wayonta?
D'uk da tana matukar son Muh'd amma mutuncin
y'an gidan su yafi k'arfin komai a gunta.
Sai d'ai shi Abba yace sam bai san zance ba,
tunda taki fad'a mishi dalilinta na fasa auren
k'anin mijin Fure.
Tanan kawai suka samu cikas.
Biki saura sati uku, in kaga Fure d'uk zabge,
amma k'arfin halinta yasa sai mai kula zai gane.
Yauma tana gida, Umma sai tausarta take kan ta
cire damuwa, tabar wa Allah komai, Maryam ta
k'alla wace tun ranar ta d'auke mata kai, sai tai
murmushi.
"Maryam.. Banza ta mata, d'uk da tabar abinda
take. Bata damu ba ta kara cewa
"Maryam tun ranar chan naso son kisan k'in
auren ki da Muh'd tamkar kin bawa Momy damar
cin galabar mu ne, dan dama so take a fasa naki,
wanda nai imani baza'a a fasa na Ahmad.
"Maryam.. Kiyi hakuri kibi zuciyar ki, ni ki bar
nawa gurin Allah, ki sani fasa auren ki, bazai
sauya zani gun Momy ba. Matsowa tai ta dafa
hannunta,d'uk Umma na k'allon su.
"Maryam, kai ta dago tana hawaye, sai ta share
mata.
"Ki min alkawarin sauke gammon nak'in nan da
kika d'aura, ki duba so,da kuma kaunar da bawan
Allah nan yake miki, da naso auren ramako dake,
ashe kana taka Allah na tashi, kar ki bawa Abba
kunya, ki manta dani, ki fuskanci Moh'd, ina
rokon ki...
Dago wa tai ta k'alli Umma, sai Umman ta tashi
ta basu gu, sai ta jijjiga wa Furen kai.
"InshaAllah, amma fa ki sani, wallahi d'uk dan
uban ni da ya nemi takani zan murje mutum.. Kai
ta k'ada mata, "wannan ban hanaki ba, ba kuma
zan fara hanaki ba.
Da wannan ta samu suka d'inke da Muh'd d'in,
aka cigaba da hidimar biki a gidan guda biyu.
Dan sam ko kusa Ahmad bai ko mot'si, asalima
Fure ke tambayar shi wataran kan abinda yake
shirya wa, banza yake mata.
Ita kam bangaren Momy koh a jikin su, d'an ko
ita ta isa yiwa Rukayya lefe, yayinda a bangaren
Mama tasa wa kowa ido, daga Ahmad d'in har
Muh'd,dan ba mai ne manta cikin harkar kara
auren shi.
Ku tambayen ina labarin Hassana man?..Lol.
Hassana d'ai sai ana saura sati wata d'aya biki
kan taji labari, akanzo har gida ana tambayar ta
da gaske mijinta wai zai aure?
Wataran harda shewa zata bada amsar A'a,
Yayanshi ne zai kara aure dan matar ba ta
haihuwa.
A ranar Momy ce ta tare ta da zancen ba koh
rufi, haka ta dawo gida ta hauka cewa Muh'd,
yayi lallabin duniya taki, a fafur sai ya fasa, sai
d'ai a ranar da tasan wa zai auro mata tattare ta
bar gidan.
Sai dawo wa yai yaga gida a bud'e tayi gidan su,
hakan ya bashi damar cigaba da shirin auren shi
cikin nutsuwa da aminci, bai ma kara bi takanta
ba.
************************
Ana saura k'wana d'aya aure har gida Momy tazo
ta chake shi harda kukanta kan wai ya mayarta
mahaukaciya, ita kad'ai take kid'anta a auren.
Tuni yai shiru, Fure dake kitchen d'akko ruwa
tana jin yana fad'in "nifa Momy kar a kaini bango
nai ba d'ai d'ai ba, dan wallahi bazan auri
Rukayya b... Mari ta sauke mishi, tuni Fure da
akai akan idonta tasau "tambulan" din lemon ya
fashe tana k'allon Momy.
Haka ta taka ta durkushe gaban Momyn da
g'wiwa biyu wacce ke kukan dan ba ita wai ta
haife shi ba, amma ai wai ita taci kashinshi har
ya zama mutum
"dan Allah Momy kiyi hakuri, dole zai bi umarnin
ki, zai auri Rukayya, dole ne wannan.
Tun fitar Momy ya kasa ko mot'si daga inda
yake, cikin d'auriya Furen ta fara lallashin shi da
kalamai masu sanyaya rai, kan Momy kam Mama
ce, dole yabi umarninta, kodan ta fita zargin ba
sa hannunta a kin aurenshi ba, dan Allah, kuma
domin ta... Har kuka tai mishi, shi d'ai kala bai
ce ba.
A t'saye yake gaban madubi kamar kullum tana
shirya shi, sai d'ai yau shirin na daban ne, dan
wai shirin d'aurin auren kishiyarta take mishi.
D'uk inda tai K'allonta yake, sam tun jiya har yau
baida walwala, sai yaga ma kamar shi kad'ai
yake kin auren, dan har wani wasa ta d'au abun.
Turare take fesa mishi, kamar kullum taja baya
tana yaba mishi k'yaun da yayi, sai d'ai wannan
karan ci kanki bai ce mata ba, d'uk yadda tai
haka yake binta da ido.
Muryar y'an gidan Angwayen ne a parlour kan
wai sunzo tafiya dashi.
Takalmin shi sabo da jiya tasa Muh'd ya siyo
mata "half cover" takai gaban shi zata sa mishi,
cikin zafin nama ya dagota cikin masifa, cikin
t'sawa yace "Mey kika d'au abin ne? Wasa?
K'arfa ki mayarni yaro... Gaba d'aya ya burkice
mata.
Murmushi ta k'ak'alo na dole, tare da d'an zame
hannunshi tana fad'in, "relax", sai ta sa hannu
kan maballin wuyar rigarshi, har yanzun yana
mat'se da ita, "yau fa ba ranar fad'a bane Dear,
muje ana jiran ka a parlour.
Hankad'a ta yai kan gado,cikin fusata ya bud'e
kofar ya doko mata ita.
Da sauri ta tashi tasa sakata.
Tuni ta zame kasa ta cire d'aurin dank'walin data
sha, ihu zata kurma ta tuno basui nisa ba.
"Wayyo! Shi kad'ai ta iya furtawa,kan tai ko'k'arin
tashi, tuni ta fara ganin jiri,ba shiri ta koma ta
zauna, sosai tai k'arfin halin kin nuna damuwar
ta gaban Ahmad, da rarrafe ta hau gado, tuni
wani irin kuka mai matukar daci yazo mata...
"Shikenan ita, ta faru ta kare mata.
By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 2:47 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 37_Batta da mai
lallashinta kusa,saboda haka sai da tai mai isarta
tukun ta samu nutsuwa. A hankali ta daga kanta
zuwa ga agogon dake manne a d'akin na hutansu
suna k'allon juna. Sai tai lamo tare da kura ma
agogon ido,(10:50am), tasan d'uk inda suke
yanzu an d'aura na Maryam da Muh'd k'arfe
goma, kenan saura minti goma a d'aura na
mijinta? A hankali ta yunkura ta tashi,sai ta
furzar da iskar bak'inta ta k'ada kai, kaya ta hau
cire wa, d'uk k'walliyar ta goge da kuka. Bandaki
taje,cikin sauri tai wanka ta fito ta hau shiri,
sosai tai k'walliya kamar ma ita ce amaryar, sai
ta bud'e "wardrobe" d'inta cikin kayan da ta
tanada a fitar bikin ta hau zabi. Akan wata
dakakkiyar shadda ta t'saya fara ce,tasha zubi
da zare "Orange" da "blue" "gown". D'inkin yasha
"stones work" mai k'yau da t'sada, Kai ta kama
tattare achan kasan keyarta kan ta kamashi da
"ribbon" ya had'u waje d'aya a bayanta. Cikin
nutsuwa ta zira rigar kan ta t'saya gaban madubi
rike da dank'wali, ta baya ta d'auroshi, yadda
gashin zai shiga ya fito ta t'sakiyar d'aurin. Nan
da nan komai ya ji, sarka da "bangles'' had'e da
zobuna sun hau. Turare ta fara feshi, had'e da
murmushi lokacin da ta k'alli kanta a madubi.
K'warai ance in kana da k'yau, wai ka kara da
wanka, ita d'ai Pretty tanaji da d'an k'yaun nan
nata wajen kara k'wask'wareshi ta dawo mai
k'yau. D'akin ta g'yara kan ta fito parlour ta
kunna "burner", dirin mota taji, a hankali taji
gabanta ya fara fad'uwa, kila har an d'aura an
dawo... Da k'yar ta iya seta kanta ta had'iye
kukanta. Har tai hanyar d'aki taji Fatee na
k'wada sallama. Da fara'a ta juyo tana amsa
mata. Baki Fateen ta rike, "inye, ka ga uwar gida
a gidan AAA.. Kingan ki kuwa? Fuska ta K'awar
tana murmushin k'arfin hali. Fatee ta karaso
dak'yar tana tura ciki. "Allah ya kawo AAA
yanzun, na tabbatar za kisha k'arin angwanci,
kai! Ke ko a jikin ki koh? K'allon Fateen take,
tamkar ta sau kukan bak'in ciki haka take ji, wai
ko a jikinta? "Ki bari ka'r na huce tawa haukar
akanki da cikin ki.. Dariya kawai ta hau mata
tamkar taga shasha, kawai sai ta zuba mata ido,
ji take kamar ta rufeta da duka. Sai ta juya kanta
chan gefe kuka na shirin zubo mata, "wato ke da
zaki taushi zuciyata, ke kike min dariya ma...
Cikin dariyar keta Fateen tace "no,sorry, sorry,...
Sai d'ai fa taki t'sagaita dariyar, harda k'walla,
Fure na shirin fashewa da kuka ta t'sinkayi Fatee
na fad'in "Angon Furera... Da sauri ta rint'se ido,
gabanta ya cigaba da d'ukan tara-tara. Sai da ta
tabbatar ta had'iye kukanta tukun ta juyo had'e
da k'ak'alo musu murmushin dole. Shi da Salman
ne, sai d'ai kamar su ma dariyar suke,gogan na
ganin ta juyo ya g'imtse fuska, kawai sai taji
wani rauni yazo mata. Tun yanzu har ya fara
washe baki ni kuma yana had'en rai? K'wafa tai
a ranta, da gaske ne kam Namiji ba d'an goyo
bane ba. Ji fa yadda ya bar gida yana cin magani
amma daga d'aura aure har ya ware,ita kad'ai ya
dake wa. "Sannun ku da dawo wa, murmushi
Salman yai, kan yace "kinga taso mu tafi kan
wannan ''nuclear bom'' d'in ya tashi damu Batool.
Harara ta dan sau musu kan ta d'auke kai, sai
dai ko ita taga bala'in d'auriyar ta. Tashi Fateen
tai tana dafa cinyoyin ta, har yanzun dariya take
a ciki ciki, "toh K'awa, sai munzo d'anna kirji
anjima. Yake tai mata, suna dariya suka fuce ita
da mijin. Fure fa ta cika tai bamm! Kiris take jira
ta fashe da kuka. Kan maigidan ta dawo, kawai
sai taga yai d'aki ya barta, sam ba fara'a a
fuskarshi. Kai ta k'ada, sai ga nan wasu hawaye
masu d'umi sun zubo. "Wato ni AA zai manna
ma? Dak'yar ta iya tashi tai d'akin cikin goge
fuska, tana k'allon kiran