Author : Queen Safiyyert Category : Romance
a d'uk duniya babu Wanda Annabi yafi
So irin Nana Aisha,, tabbas wannan ma Aya ce
da Allah yake son nuna ma dan Adam, amma na
rasa ina "TA'UHIDI" na yaje a lokacin.
"Gashi yanzu na rasa falala biyu a rayuwa, ta
farko hakuri,na biyu mukami, dan nasha jin ana
fad'in cewar ''Allah yana kunyar had'a ido ga
wanda bai bawa haihuwa ba har ya koma gare
shi ranar gobe kiyama.. Nayi imani ba abinda a
duniya Allah zai hana ka ya kuma ji kunyar ka
irin wannan, amma na manta,har sai da ya kure
kan na hango shi, na rasa wannan falalar. Sai ta
fashe da kuka.
A gaskiya yau Fure ta kara samun tuni a game
da rayuwa, har batasan itama ta fara kuka harda
shassheka ba. Chan cikin kuka Fatee tace,"shi
yasa nake son dan Allah ka'r kiyi ma Allah
butulci irin nawa, ki k'ar6i K'ADDARA a d'uk
yadda tazo miki, dan gudun irin wannan rana ta
kunyar Allah.
Kai Fure ta k'ada.
"Idan anyi Duniya dan Manzon Allah daga rana
irinta ta yau bazan kara da na sani akan ban
haihu ba.
"Zan d'au hakuri,na kuma juri jin yadda ake
kirana da JUYA.
"Tabbas yau na gane kuran kuka,sannan na
tsorata da jin labarin D'an Allah banin waccan
matar.
Kai Fatin ta k'ada mata, kan tace.
"Kawai na amince miki ne tafar d'aya a ganin ki,
ubangiji ya baki damar cinye jarabawar ki sister,
kar ki bi yewa mutane, za su kai ki ne kawai su
baro.
"Sannan ki d'aina sanya tunanin kowa a ranki sai
Allah,InshaAllah za kiga d'ai d'ai...
A takaice Furen ta sanarta itama tarihinta,
sannan da address nata, suna cikin haka sai suka
ji dirin mota a kofar gate, sannu a hankali sai ga
nan mata na shigo wa da dangin mijinta su biyu.
A wulakance y'an uwan su Salman d'in suka
k'allo su,ba koh gaisuwa suka cewa dangin
amarya su shiga ga nan "part" d'in amarya.
Da ido Fure tace tai musu magana.
Sai ta d'aure ta gaida su, sosai da ganin su
tasan za'a buga da amaryar.
Har suka gama dak'yar ta kai musu ruwa shima
da sa bak'in Fure.
D'uk dangin amarya sunyi waje,sai dangin
Salman da suka t'saya karewa parlourn Fateen
k'allo suna ta6e baki, ganin ya sauya mata kaya.
Ci kanku bata ce musu ba, sai d'ai sukai kitchen,
d'uk dan su takali fad'a.
Wannan karan kam fatee kasa hakuri tai kitchen
d'in Fure na kira amma sai sa ta karasa.
A bak'in kitchen d'in ta t'saya, bud'e bud'e suke
mata suna fad'in "haka d'ai, sai d'ai a ware ciki
aci aka iya ai kashi, sai ta basu hanya, K'anwar
Salman d'in sai da tazo d'ai d'ai kusanta ta sau
mata t'saki.
Batai wata wata ba ta sharara mata mari, tuni ta
dafe kunci, "ni kika mara? Tass! Ta kara mata
wani, wai sai tazo zata rama, ina, Fati da wa
Allah ya had'a ta, tuni ta hau jibgarta kamar
Allah ya aikota.
Fure da d'ayar K'anwar tashi suna ko'k'arin
bambare Fati, ganin taki dagata yasa tai waje,
sai da ta huce d'uk wani haushi da suka zuba
mata tukun ta bari Fure ta k'waceta tana haki.
"Ihu yarinyar take dan sosai ta bugu gun Fati.
Da gudu Salman ya shigo da K'anwar da dangin
amarya.
Tuni Fati ta sauya kama ta rike k'ugu, wallahi
yau yadda take jinta tai imani ko Salman zata iya
nad'a mai duk'a.
A yadda yaga Fatin tabbas shima ya tsorata, dan
Sam bai ta6a ganin ta burkice haka ba, "Fatima
ya haka fisabilillahi? Abinda ba halinki ba shine
yanzu zaki t'sira saboda zan kara aure? Wannan
ai hauka ce.. Wata uwar harara ta sau mishi, kan
ta k'allo k'annen yadda suke doka mata harara,
data zabura tace "ku t'saya,ba akan ku na
haukace ba? Sai tai kitchen,''yau wallahi za kaga
d'anyen kai.
Bai nufa yaga ta fito da gudu da muciya tai kan
k'annen shi da dangin amarya, habawa,takai ta
kai, kowa hanyar gudu yake nema, har gate ta
bisu tana muka musu a d'uk inda hannunta ya
kai.
Fad'i take "ba haukatar ni kuke so kuyi ba? Bari
toh na fara ta kanku, haki take tana "naga wata
shegiyar da zata kara zuwa har gidana ta ci
mutunci na d'an... Saukar Mari taji a fuska, da
sauri ta y'ar da muciyar ta K'alloshi tare da dafe
kunci.
"Salman... Mari? Ni ka Mara? Cikin tunzura
yace"an mare ki d'in.. Koh nima zaki dake nin?
Kai ta girgiza,tai cikin parlourn, kawai sai ya bita
yana kara sauke mata sababi,
"Aure ba fashi, wallahi sai d'ai kiyi abinda zakiyi,
dama tunda naga har yau baki tanka a auran nan
ba nasan da abinda kike shirya wa.
Da mamaki take K'allonshi.. Kan ta rint'se ido da
murmushi ta furta "Na Miji?Namiji? Kawai sai tai
k'wafa.
" Ba laifinka bane, sai d'ai ka sani, wallahi na
bazan zauna na jidi wannan rainin hankalin ba
har wata ma ta shigo ta kawo min raini ba..
Hannu ya hard'e kan ya k'allota, "yanzu mey kike
so ayi? Da sauri tace "saki.. Kai Fure ta hau
girgiza mata, sai ya k'allo Furen yai
Murmushi, "toh wallahi bazan saka ba,aure kuma
kamar anyi an gama ne.. Cike da bala'i tai woo
kanshi, "wannan ne kuma baka isa ba wallahi.
kawai sai ta rufo kofar parlourn,"in har ka fita a
gidan nan toh ka Sake ni, na tsane ka, ban son
ka, koh kaunar ganinka yanzu bana yi.
Kafada ya make, "kiyi komai amma wallahi bazan
sake ki ba, sai d'ai zaki iya zuwa ko'ina ne in ma
baki son ganin zuwan amarya bazan hanaki ba. A
masife ta ta kutuntumawa Amaryar zagi, kawai
sai ya hau mata dariya.
Ganin tana neman fita a haiyacinta yasa Fure
kamo ta. Sai sukai d'aki. Tuni ta hau tattare
kaya. "A'a sis Fatee, jama'a za su miki k'allon
kishiya ce ta kore ki fa... A masife tace"sumin..
In dai jama'a ne ai ko na zauna zasui komai,
wallahi bazanyi kaffara ba sai na bar gidan nan.
Yin duniya Fatee taki hakura.
Sai da tai katuwar "trolley" kan ta janyo taiyo
parlour kan ta koma d'akko hijab,, yana ganinta
ya mike, dan sam bai zaci da gaske take ba.
"Fatee kar muyi haka dake, a masife ta ja jakar
har tana bi da ita ta kan kafarshi, har ta kusa
kofa ta tuno da jakarta, ita d'ai Fure sai binta
take a baya tana tai hakuri.
Jakarta ta zuge, cikin masifa take birkito kayan
ciki, "ga Fatee matsiyaciya, "cheque" dinshi ta
hulla mishi, kan ta d'au mukullun mota, "duk ka
jika kasha, ni ba masiyaciya bace, sannan ka
sanarwa da dangin ka su zuba ruwa a kasa su
sha, na barka har abada.. "And 2 hell with
amaryar ma.
Ganin gaske ta d'au zafi yasa kuma ya kid'ime,
"Fati ka'r kuskura ki fita ba da izini na ba,
Fateema, ko ta kanshi bata bi ba, burin ta kawai
ta bar gidan, mukullin Fure ta k'ar6a ta bud'e
mota, a baya ta sa jakar, sai gashi ya fito, "Fatee
ki saurare ni pls? Yanayi yana k'allon Fure kamar
mey nufin ta sa baki, ita kam Fateen ma sai ta
fara bata tsoro,don d'uk ta firgice mishi.
Shiga tai da zummar tada motar ya rike kofar
gam, "Fatima pls, kira take "ka cikan murfi mota,
ba kace naje ko'ina ba? Kai ya girgiza, "hakuri,
wallahi da wasa nake.. A tunzure tace "wasa? Da
sauri ya jijjiga kai, "eh, kiyi hakuri.. Wallahi ko na
kira su Abba? Da tai wani kukan kura da k'arfi
taja murfin motar, "Allah baka sa'a.
"Reverse" ta fara yana kiran sunanta, amma ina,
ga unguwa kamar ta mayu ba kowa layin, da
sauri ya shiga dan d'akko waya yasan Abba
kad'ai zai t'sayar mishi da Fatima.
By
Feenat Ja'afar.
庐NWA
9/29/16, 2:39 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 33_Sosai take kudu
dan ma kar ya cimmasu tai ta k'wane-k'wane,
sai da ta tabbatar da ta mishi nisa kan tai
"parking" achan gefen titi tana k'allon gabanta ba
koh kiftawa, haki take tana jawo numfashi
tamkar da kafa tai gudun. Fure ta k'allo ta "Kiyi
hakuri ki kori shedan sis Fatee... A "stirring"
motar ta d'aura kanta ta sau wani kuka mai
k'arfi, kawai sai Furen ta zuba mata ido dan ko
zata huce ta hakan. Sosai tai tana mai kara
t'sanar halin mutum. Sai da tai mai isarta kan ta
share, a sannan Fure ta fara ce mata komai yai
zafi maganinshi Allah, ta duba halin da take ciki
kar ta jama kanta matsala. Ita d'ai uffan bata ce
ba,sai ma hawaye dake k'waranya. Wayan ta taji
yana kida, a hankali ta sa hannu a jakar ta ciro,
"Abba" ta gani, tuni sai ta seta kanta kan ta
d'auka. Ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba,
sannan ya sanar mata kar ta fara dosar inda
suke tunda akan kishiya zata sa6i mijinta. Har ya
kashe in banda kuka ba abin da take, sai ta
share idon, kawai sai ta raya mata tai yola
dangin Ummanta kawai, Fure ta k'alla sai tace
tazo ta tuka. Ba musu sukai musanye, "kaini
tasha.. Kai ta k'ada mata ba musu, sai ta d'aura
kai a gefen kujera tana k'allon gefe hawaye na
t'silalowa. Kai ta daga ta k'alli Fure lokacin da
taji tana "Horn" sai Furen ta d'auke kai. Har suka
shiga gida bata k'allo ta ba. "Tasha nace ki kaini
fa.. Fita Furen tai had'e da bud'e baya ta ciro
kayan Fateen. Kawai sai ta bita taga iya gudun
ruwanta. A parlour ta sauke, a takaice ta karewa
ko'ina k'allo kan ta zauna, sai Furen taje "fridge"
ta d'akko mata sassanya ta tsiyaya a cup tare da
tsayawa a kanta ta bata. D'uk sai kuma ta fara
kunyar Furen,ba musu ta k'ar6a tak'wa shanye
tare da mikawa Fure,kara mata tai kan ta zauna,
tuni sai ta sau ajiyar zuciya. Kai shedan mugune,
nan da nan zai sa ka tafka tsiya zuwa anjima ka
dawo kamar ba kai kai ba. "Koh kud'in mota baki
taho dashi ba,hala zasu kai ki k'yauta? Sai a
sannan ta tuna da ba ko sisi d'uk ta zube mishi
t'siyarshi. Yanzu mui sallah,sai muci abinci,"I
know babyn mu yau ya jigata, dan yau Momyn
shi taji k'arfi... Dariya suka sa Fateen na goge
hawaye. Sallah sukai ta d'akko mata dan
"snacks" ta rage kan ta tafasa musu ko taliya ne.
Zama tai lokacin da take dumama miya tana
murmushi, "Ashe kin iya fad'a haka sis? Kai koni
na tsorata fa, kai ta k'ada. "Mutane ke koya
maka d'uk wani hali da ba naka ba. "Amma
wallahi da gaske na t'sani Salman, ko ganinshi
na t'sani yi, sam namiji bai da tabbas. Kai Furen
ta k'ada, "kiyi hakuri, komai mai wuce wa ne. Ki
zauna anan zuwa gobe AA ya dawo sai ya bamu
shawarar yi.. Da sauri ta k'allota, "namiji ne zai
bamu shawara? Da rashin fahimta Fure ta k'ada
kai, sai ta girgiza kai,"toh a gaskiya bazan zauna
ba, dan maza sun shani tuni na warke... Kiran
Salman ne ya shigo tana ji taki d'auka, dan "ring
tune'' nashi "special" ne. t'saki ta ja ta tashi ta
d'au wayar ta d'anna "reject" kamar ta cire
"buttun" d'in wayar. Ko ajiye ta batai ba ya kara
kira. Kawai sai ta kashe wayar gaba d'aya.
Shikam suna fita ya dawo d'aukar mukulli ya kira
Abban Fateen, suna gamawa sai ga nan kiran
likita, da mamakin shi ya ji yana mishi "congrats"
wai ya zama Baba.. Kamewa yai gu d'aya lokacin
da yace ma likita shi bai fahimta ba ya sanar shi.
Sai ga nan takardar asibitin ya d'auka da ta bari.
Kai ya dafe kai, har da k'wallarshi, wanda bai san
ta meye ba. Abu d'aya ya sani yaso Fatee har
yau d'in nan. Tuni ya bisu ko zai same su, shine
har tasha amma ba Fatee ba kalarta. Dak'yar
Fure ta shawo kanta ta zauna suka k'wana,
kusan k'wanan zaune sukai suna firar duniya, fir
taki ma k'unna waya bare a kira ta. Washegari
Fure da taryar AA ta tashi, sai d'ai Fatee na
tayata tana ta6e baki, dan gaba d'aya maza sun
sane mata t'saf. Ita dai Fure murmushi kawai
take binta da shi. By Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 28
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 34_Sai kusan magriba
AA ya shigo, a gajiye yake, lokacin suna a d'akin
baki ita da Fatee kan lalle ita sai ta tafi, suna
cikin gardamar taji dirin motar shi, sai ta fita tare
da kulle Fatee ta waje, sam bata so ta tafka
kuskure. Kamar ba kowa ta t'ar6e shi da fara'ar
ta, kamar kullum ya kimtsa kan yaci abinci, sai
kawai suka hau soyewar su ta ma manta da
Fatee. A zabure ta mike a cinyar shi a parlourn
tai d'akin baki da gudu, da sauri shima ya mike
yana "lafiya pretty? Tana bud'e ta tana zaune a
gefen gado ta k'wando mata harara. Sai ta kara
rufota kan ta kama hannun AAn sukai d'aki. A
nutse ta sanar shi komai harda hawayenta, sai
kai yake jinjina wa, lalle taga tasku, amma yafi
ganin lefin mijin. Parlour suka dawo ta kara bud'e
Fatee, kamar mey jira sai gata sanye da g'yale
da Jaka a hannu, "dan Allah karki t'sayarni, ki
barni na tafi nagode k'warai... Shiru tai ganin
Ahmad, sai yai mata k'warjini har batasan ta
gaida shi ba, hakuri ya fara bata kan tai hakuri
yanzu magriba tayi, zuwa gobe sai su san abin
yi, ba dan ta so ba ta hakura,kawai sai taga
girman shi. Ita kanta Fure ganin AAn sai taji tana
d'an dari dari dashi, dan kawai d'aurewa take,
amma ace gaba haka ya faru da ita wai... Hmm
sai Allah kawai. Fitowarshi a wanka kenan yaga
ta had'a tagumi, sai ya k'ada kai, tabbas yasan
maganar dazun ce. Yana k'allonta har ya gama
shiryawa ta lula duniyar tunanin dabi'ar maza da
mutanen duniya. Sai ya k'ada kai,a hankali ya
tako ya iso gabanta ya tsuguna. Ajiyar zuciya ta
saukar,kan ta d'an k'ak'alo murmushi, sai ya dafa
cinyarta, "I love you pretty... En banson ki sanya
shakku, ki cire tunanin komai a ranki, AAA naki
ne... bazai ta6a miki haka ba InshaAllah..
Hawaye ne ke ko'k'arin zubo mata, so take ta
gaskata shin gaske AAA nata ne? Sai kawai ta
sau su suka zubo, hannunta ya ruko,har yanzun
yana a tsugune, "Furii believe me, maza ba d'aya
ne ba... Tuni ya hau tsumata da dad'in
baki,Aiya,ita kam ta ziru t'saf, sai yasa hannu ya
sunkuyo da kanta da take murmushi hawaye na
k'waranya yasa ''lips" nashi yana tarar su. A
hankali ya dago ta suna k'allon cikin idon Juna,
tabbas ta aminta AAA na daban ne a sauran
maza, a hankali ta zamo itama tai yadda yayin
suna mai cigaba da karantar juna ta cikin ido, sai
ya tadasu t'saye tare da lafar da kanta a gun
zuciyar shi, a hankali tamkar wata baby yake dan
jujjuyawa kad'an kamar mai rawa,ita kam Fure
anyi luf..cikin nutsuwa ya kara karasa ta da
wakar da indai yai mata take jin a sama. Takanji
wani nishad'i, har ta manta da komai, sam in kaji
yana wakar ka zata shine mawakin, amma kawai
dan Furen shi baitin na "Nothing gonna change
my love 4 you.... Yake burge shi. T'saf acikin
daren ya ware Prettyn shi cikin sauki da lumana,
har ya lalla6ata tai bacci fuskarta d'auke da
murmushin son shi da jin dad'in baitikan, da yaso
yin shiru, sai ya ji tana ya cigaba. Murmushi yai,
Mata sai da lalla6a. Da safe suna kitchen yana
tayata had'a ''break" ta fito da dan gudunta, a
zaton ta ita kad'ai ce a kitchen, hannunta ta cire
a wuyan AAn taiyo gun Fateen da ta juya. "Sis
lafiya? Gaskiya a d'aina gudu da d'an mu.. kawai
sai taji ta ruko hannunta da murna ta d'aura kan
cikinta, "wallahi yau sai mot'si yake, cikin murna
Furen ta kara d'aura d'ayan hannun tana
murmushi, Allah sarki Fatee, fara'a take kamar
mey, shi d'ai Ahmad daga bak'in kofa yana ta
musu murmushi. Sai lokacin Fatee ta kula dashi,
a dan kunya ce ta gaida shi, sai ya amsa yana
ya Baby? Sai tai kasa da kai shi kuma ya shire
"apron" nashi yai waje. Kitchen d'in suka wuce
dan gama aiki, sai g'yada kai Fatee keyi ganin
yadda Fure ta zama "Chief ". Bayan sun gama
cin abinci ya shirya yace Fure ta kira Fateen. Sai
gasu sun fito sanye da Hijab. Sanarta yai ya ji
komai, sannan ta zauna anan zuwa yai ma su
Abban ta magana, ya d'ai lalla6a ta har ta yarda.
Cikin wayo yasa Fure tai mai "copying" numbern
mijin Fateen. Sosai take jin dad'in zama da ita
kamar sun saba a k'wana biyu. Iyanzu kam,ji take
Fure tamkar y'ar uwa ce a gunta. Cikin dabara
Fure tasa ta bud'e waya kan zasui "exchanging"
number. Tana bud'ewa "texts" d'in Salman na
shigowa, d'uk na ban hakuri ne zuwa wai ina
take? Tai mishi rai ta dawo, tabbas itace ma
had'in rayuwar shi, baki ta ta6e, "yau na gama
yarda da dad'in bak'in maza... Ji ni zai rai nawa
hankali? Wai mahad'in rayuwar shi? Fure tai
murmushi, kawai sai tai k'wafa ta hau goge su
tana mita. Ita d'ai Fure dariya take tana tai
hakuri. Shikam yana d'akin Fatee ya tasa "result"
yana k'allo, waya ake mishi kan yau za'a zo jeren
amarya, sai yai jim, "ba yau ba. Kawai sai ya
kashe waya. "Delivery report" ne ya fara shigo
mishi, da halamu kenan Fatee ta bud'e waya. Da
sauri ya fara dailing, da kamar bazata ta d'auka
ba, sai d'ai ta waske, ''ya akai? Cikin magiya ya
fara "Fatee, Fatima,Batool, haba Bintu na, dan
Allah ina kike? Kiyi hakuri pls... T'saki tai, "kaga
fa, ni wallahi wannan mayaudaran kalaman naka
bazasu min kom ba, ka ma d'aina tambayar ina
nake, dan wallahi bazan fad'a ba. " Haba
Batula,gaba d'aya kinsa na fita hayaci na, auren
ma d'uk ya ficen a ka, ga nan Umma ta tadan
nata akanki itama... Da sauri tace "kar ka maida
ni bi ta chan, ka zata fasa auren ka zai damen
ne?.. Kawai sai taja t'saki ta kashe. Fure tace "a
gaskiya yayi nadama fa man d'in nan.. Harara ta
dan sau mata, "ke fa na fuskanci bakisan halin
maza bane. Kai ta k'ada tana murmushi, sai ta
ajiye waya zata kama ruwa, tuni Fure ta sace
numbern Salman. Da yamma suna zaune suna
wainar filawa sai santi Fatee take, wani abu na
ciki, tunda taga positive Washegari ta t'siri
t'surfa. Fure sai dariya take mata, "haba mom
twins, Wa'ina ai sai Kano, kai ta g'yada tana
d'ang'walar y'aji, "haka ne kam, amma ke komai
naki ai "special" ne... T'sam Fure ta zuba mata
ido tana k'allon ta, ita kam sai zuba santi take,
"yajin ki ma na daban ne, a k'wana uku na koyi
abubuwa... "Lafiya wannan k'allo? Kai ta k'ada,
dan har ta Lula duniyar tunanin AAAn ta,tunda
tace koman ki "special" kawai shi ta tuno. By
Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 28
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 35_Bud'e gate suka ji,
Fatee tace "d'an mikon g'yale na, hannu ta mika
kan ta yafa mata. Shi kad'ai ya shigo yana
murmushi, kai kasa Fatee tai mai sannu da
zuwa. Sai ya nuna wa Fure waje da hannu, kan
ya dawo kanshi,yana nufin ta d'akko mayafi, kai
ta g'yada, sai yai waje, ta d'akko ta tarar Fatee
zata shiga d'aki, tace "A'a. Mui zaman mu, zasu
zauna taji Ahmad na fad'in"bissmillah man, shigo
daga ciki. Juyawa Fatiman tai zata tafi d'aki, a
tunanin ta ko bako yayi, sai ta ji yace "bissmillah
Fatima, dawo kiyi zaman ki, tana juyo wa tai
ar'ba da Ango. Tuni ta k'ank'ance ido tare da rike
k'ugu, sai ya marairaice mata, kawai sai yaga ta
kara mishi ma k'yau dafari. "Mey ya kawo ka?..
Cikin marairaita ya matso, ''haba Fati ta, kamshin
masoyi ai baya buya koh AAA? Sudai dariya suke
musu. Harara ta sakar mishi, "kar ka yaudari
k'anka, dan ka d'auka ban sanka ba All... Shiru
tai ganin ya zube mata g'wiwa biyu a gabanta.
Sai ta k'allo su Fure, itama k'unne ta kama kan
tai hakuri. Sai ta d'auke kai, "tashi malam,bani
da matsayin nan, tashi, maza ka rufan asiri..
Ahmad ya k'allo, sai yai