BACCIN SO BY M SHAKUR

Author :  Category :  Romance

Chapter   44 / 51

129K to 132K   out of 150.2K words

zaune suna kallon Ammi harta mike layin tai kwana tacigaba da tafiya sai Daddy ya kunna motan dasauri yace  yauwa! Yaja motan zuwa dayan layin da ba mutane sosai yayi parking yace  go as planned gardi daya ne yafito dawata yar tsumma a hannunsa yabi bayan Ammi da sauri sauri, yana zuwa bayanta jin mutum nabin Ammi dab da dab toe to toe yasa tadan dakata anatse tareda matsawa gefe irin shi yazo yawuce dinnan sai kawai yasha gabanta yace  Hajiya inada magana dake dai another dayan gardin yazo ta bayan Ammi kawai taji saukan abu a hancinta within seconds kawai ta suma daukanta sukayi wasu yan yaran anguwa suka fara ihu yan yankan kai, dasauri suka sata a mota, Daddy yaja motan da mahaukacin gudu, while gardawan suka ciro igiyoyi, daya na kulle ma Ammi hannu, daya kafafu, suna gamawa daya ya yago salatep dinnan mai ruwan toka dake kama abu da kyau aka manna abakin Ammi datake a sume Daddy na bazama motan wuta yana murmushi yana tuki yana kada kafa baimasha wahalan dayayi tunani zaisha ba, ance rannan dazatai kyau daga safiya kake ganewa, ya kunna wakan barmani choge yana murmushi yace  it s about to be a very good day today yana tuki yana kallon Ammi dake sume zaune tsakiyan maza biyu ahaka sukai tafiya na kusan 1hour chan bayan gari sukaje, wani waje haka da ba mutane da akwai gininuwa suka shiga suka bude gate aka shiga wani gida mai bene haka da bama agama ginasa ba Daddy yayi parking yafito suka fito da Ammi akai ciki da ita akwai wata yar yaloluwan katifa anan aka kwantar da Ammi dan babu any furnitures Daddy ya tsaya yana kallonta kaman zai cinyeta one of the boys yace  ga jakanta Alhaji karban jakan Daddy yayi saiya bude yana kallo yana ciro abubuwan ciki, littatafan islamiya ne ciki sai yan kudade dabasu wuce 5k ba sai kuma wayanta, wani murmushi yayi wayansa na ringing yaciro wayan ya kalli saiyakai kunnensa Maman Baby tace  kun kamota ? Ammi Daddy ya kalla yace  kwarai gatanan a sume Maman Baby tace  an ina kuke nima gani nan zuwa ? Dasauri Daddy yace  nooo I don t want you here ki zauna a gida, ke kika kawo shawaran nan nadauka, ai ya isa basai kinzo"

"nan ba, bye ina zuwa I m busy zan baki labarin komi kafin tai magana ya katse wayan ya ijiye."

"Wayan Ammi yadauka, one thing daya sani about Ammi is wayanta ba password to ta inama zatasa"

"password wayanta dake nan abin wasan mahaukaciyar yarta, dasauri yace  abani kujera plastic chair"

"aka kawo masa yazauna saiya danna wayan Ammi his aim is tayaya zaiyi contacting Amirah, Call log nata"

"yashiga dubawa yaga sunan Amirah dana Miemie, yadan tsaya kadan yana kallon number Miemie sai kuma yawuce, hakanan saiya shiga duba call log dinta har karshe ko zaiga tana waya dawani namiji baimasan mesa yake dube duben ba amman sai baiga komiba banda yaranta sai Lami da Baffa sune a call log dinta, wani ijiyan zuciya yasauke mai karfi da baimasan ya sauke ba, saiyayi dialing number Amirah da wayan Ammi yakara wayan a kunne yana gyara zama yadaura kafa daya kan daya yana hade"

fuska.

"Wani kalan masifaffen ciwon mara Amirah keyi bana wasaba, ga Marwan bacci mai nauyin gaske yake"

"harda minshari, ga zazzabi na nukurkusan ta, kaman daga sama wayanta ne yashiga ringing anan closet taji karan, tasan wayan na daki kan gado, jiya data koma dauko tsimi tanasha tana danna wayan akan gado maybe Marwan yashigo da wayan closet, bamata da karfin tashi but jin yanda wayan ke kuka hakanan tasan kodai Ammi ko Miemie one of them ne ke kiranta sukadai ta taba kira da wayan nan, har wayan ya katse kasa motsi tayi, akaro na biyu wayan yafara ringing kuka tafashe dashi ahankali gwarama ta tashi tadauko wayan tagayama Ammi tazo tadauketa she s tired Ya Marwan zai kasheta, cikeda tsiwa tasa hannunta ta fizge boobs dinta dake bakinsa bacci ya shiga Marwan ko motsi baiyi ba da kyar ta yunkura ta tashi daga kwancen tana shivering na zazzabi tana kallon wayan da baida wani nisa da ita yana kan kujera amman azaba yasa batasan tayaya zatai reaching wayan ba, ahaka second call din yakare wayan yashiga ringing ganin Ammi is calling her akaro na uku yasa ta tattaro duka karfinta ta wani rarrafa takai wajen tasa hannunta tadauki wayan taga number Ammi ne dasauri takai wayan kunnenta da muryanta da baya fita sosai tace  Ammiiiiiiii kizo ki daukeni banda laf&  cikin wata"

"kakkausan murya Daddy yace  Keh! Chak maganan ya tsaya a wuyan Amirah jin muryan wanda bazata taba mance muryansa ba, azafafe Daddy yace  idan kikai ihu kokika bari akasan nike waya dake saina kashe Ammin ki! Wani sarawa kanta Amirah dummmm! Takai hannu daya dasauri ta dafe kanta, jin muryan wanda bazata taba mancewa dashi arayuwanta ba Daddy Kafin tai wani abu saiya katse"

"wayan dasauri jikinta nawani kalan rawa ta shiga kokarin sake kiran wayan saiga kiransa yana kiranta facetime dan yanzu iphone garesa, dasauri Amirah tashiga dauka, fuskan Daddy tagani daya hade fuska kaman Ibilis, thank god yanda tarike wayan fuskanta kawai ake gani dan ba kaya jikinta, hannu Daddy yadaura abaki alamun tamai shiru saiya juyar da camera wani gida Amirah tagani dabata sani ba ko cilin na sama babu agidan saitaga wasu gardawa sanye da bakaken kaya a tsaitsaye the next thing kawai ya hasko mata Ammi agado sun daure hannuwan Ammi da igiya da kafafunta da igiya, an kulle mata baki, idanunta arufe bamata gane ko tana raye ko mace ba, dawani irin sauri Amirah tace  Ammiiii! Muryanta baya fita sosai dan ya shake, tafashe dawani irin kuka jikinta narawa kaman na mahaukaciya tama kasa magana sai sunan Ammi kawai datake kira, Daddy yace  ke saurareni nan, kinason Ammin ki ko? Dasauri Amirah ta gyadamai kai tana kuka ba wasa, cikin wata murya yace  nabaki 60seconds wato minti daya kiwuce kije waje kofar gidan nan akwai wata mota koriya ki shiga za a kawoki nan bance kizo"

"da wayanki ba, inhar kika wuce minti daya saina kashe mahaifiyarki! Dan haka idan bakiso na kasheta, if"

"you want your mother alive you have 1min to get to the car, time starts now, and kika sanar dawani"

"abinda ke faruwa ko inda zaki saina kasheta shima, time starts now!!! Arude Amirah tace  dan Allah karka& .. katse wayan Daddy yayi kai Amirah nada trauma a Daddy akanta sosai she watched how he beats mahaifiyarta growing up, yanzu dataga Amminta kaman ma a maccen take a daddaure kawai her entire world come crumbling akanta, kanta yafara bugawa the only thing dake ringing a brain dinta is Mamanta cus Ammi is her entire life, gown dinta dake nan kasa tadauka tasaka da hijabin ta jefar da wayan yafara kokarin yunkurawa ta tashi tama kasa kuka kawai take saita shiga rarrafe tana bala in sauri cus she has just 1min fitowa daga closet tayi zuwa bedroom din tayi wajen kofa tana rarrafe shima"

gabanta ciwo yake mata bana wasaba.

Thank god key na jikin kofan ta murza tabude Saleem tagani gaban dakin bacci yake meyake iho amman

idanunsa arufe ta gefensa tabi tana rarrafe tayi stairs tashiga dauka tana kukan azaba da radadi kofan falonsu a wangale tawuce tafita ganin kaman one minutes yawuce tashiga wani kalan sauri tafito compound tanajan knees nata akan interlock gate dinsu ma abude tawuce tafita taga motan a kofar gidan gawani mutum da bakin kaya da bakin glass yabude mata baya lallabawa tayi tashiga dafa bango tamike kafanta daya akasa daya takasa ijiyewa akasa kafin ta runtse idanu cikeda jarumta ta ijiye duka kafafun akasa tabudesu saita fara dingishi tana taka kafan tana kuka tawuce tashiga motan mutumin

yarufe yashiga gaba yaja motan da mahaukacin gudu.

Rawa jikin Amirah kawai yake acikin motan idanunta na juyawa wani kalan zazzabi takeji data dade

"bataji kalansa aduniya ba gashi kanta namata wani kalan zafi a tsakiya da batasan menene dalili ba, sai tuna Daddy take da halayyansa da abubuwan dayakema Ammi da yanda yakesa Ammi kuka sosai da yanda yake zaginta, kanta yadauki zafi, zafin da kanta ke mata yafi zafin da gabanta ke mata, Daddu is like the monster of her entire life and now the monster is about to eat the most precious thing arayuwanta Amminta, one of the reason hankalinta ya kwanta aduniyan nan is because Ammi tabar gidansa she s in a place da ake sonta, how did Ammi ends up awajen sa? Meyama Amminta? Yakashe"

mata Ammi ne????.

JAMA A A GANINKU ME DADDY KE SHIRIN YI???

GA SALEEM NA GIDAN WAI PARALYZE YAYI NE????

MARWAN YATASHI BA AMIRAH SALEEM NA GIDANSA MEZAI FARU???

KUNA GANIN AKACE AMIRAH TA ZABA KO AMMINTA KO MARWAN AYANZU DATAI HANKALI WAZATA

ZABA???

SA KANK0 IN HER SHOES KE WAZAKI ZABA MIJINKI KO MAHAIFIYARKI??

KUNA GANIN TRAUMA DADDY ZAI IYA MAIDATA GIDAN JIYA??????

EPISODE

Almost 2hours da fitan Amirah yanzu! Cikin bacci mai wani kalan dadi kaman yana aljanna Marwan ya

"mirgina yana wani turo bakinsa zai karajan nono yasa abaki yaji baiji nono ba, yadan juya kansa ko zaiji taushin nono fuskansa still baijiba, hannunsa yakai ahankali dan idanunsa arufe har lokacin yamika zai kamota ya tattaba wajen yaji bakomi sai lallausan carpet dayake tabawa, bude idanunsa yayi ahankali yamika hannu side nasa yadauki glasses nasa yasaka sannan yakalli gefensa yaga wayan bakowa dasauri yatashi zaune yanabin wajen da kallo ina Amirah? Tana bayine? Ya tambayi kansa but kalan cin dayama Amirah she s in no condition dazata wani iya daga kanta harta fita daga closet dinnan taje bayi, dawani kalan sauri yatashi, boxer yaja yasaka yana kallon wayanta daya gani akasa yaduka yadauka cus yasan akan kujera ya ijiye wayanta da hannunsa ya ijiye wayan, yawuce dasauri yafito daga closet din, chak ya tsaya chakkkkk yakalli kofan dakinsu ganin kofan abude ga Saleem da gabaki daya wallahi wallahi ya mance dashi banda yanzu dayagansa kwance gaban dakin idanunsa a lumshe kaman bacci yake, wani bugawa kirjinsa yafara but he locked the door, ya kalli key still yana jikin kofan that means daga ciki aka bude kofan Amirah ta iya tashi harta fito nan ne? Ta gudu daga dakin nan taje another daki ne sabida tana tsoron karya kara mata sex? Abinda yazo kansa kenan, bayin dazai duba yafasa yayi kofan da sauri to be honest bata Saleem yakeba ta matarsa dayasan batada lafiya yake, tsallake Saleem yayi yawuce"

dakin Amirah dake kallon nasa yana bude kofan yaga dakin baiyi kama da dakin da aka shigoba kawai

gabansa yashiga fadi dasauri yace  Baby kina bayi ne ? Yayi maganan yana bude bayin dakin amman

"babu alamun an shigo bayin dasauri yafito, four rooms ne asaman one by one yashiga shiga dakin amman babu Amirah, toko yunwa takeji? Yana tunanin yataho stairs yana kallon kofarsu dayake abude wanda baikawo ita bace yasan aikin Saleem ne yawuce kitchen dasauri amman babu alamun wani mahaluki a kitchen din yashiga store shiru yabude kofan backyard babu ita kai kirjinsa dukan uku uku kawai yakeyi, yadawo kitchen din they have a room anan falo yawuce yabude dakin yashiga bayi same thing babu alamun wani ciki hannusa biyu yakai yadaura kan kirjinsa yace  Innalillahi wa innailaihi raji un dan he s panicking and he don t wanna panicked, toko taje gidansu wajen Mami? Wait tayaya Amirah zata iya takawa harta futa taje gidansu that s impossible tsaya kobai duba da kyau bane, second search yafara ganin kaman bai duba ko ina da kyau ba ko taboye ne danta gaji yamata mugun ci yar"

karkashin gado yake dubawa dasu closet amman shiru.

Ya fito nan falon sama ya tsaya chak saiya kalli Saleem dake kwance awajen idanunsa rufe saiyahau fuzar

"da ijiyan zuciya first dukan dayama Saleem he regretted it koba komi Saleem yaci darajan Abba, and deep down he understands Saleem pains, shima lokacin da yadauka da Saleem za ayi auren ko kallon fuskan Saleem baya iyayi sabida kishi, ayanda yakeji yanzu idan yace zai taba Saleem zai iya masa kisan gilla har lahira so calm Marwan calm, yafadi yana dukan kirjinsa yana fuzar da ijiyan zuciya saiya sake tsallake Saleem yashiga dakinsu wayansa yadauka number Abba yaciro yayi dialing wayan ruwan yaji akan fuskansa dasauri yakai hannu ya share ringing daya Abba yadaga kafin yayi magana ahankali Marwan yace  Abba kana ina? Dan jimmm Abba yayi jin yanayin muryan Marwan, kai tsaye yace  meya faru? I m close ahankali Marwan yace  Abba dan Allah kazo gidana yanzu Abba yace  menene Marwan ijiyan zuciya ya fuzar zaiyi magana yakasa ya katse wayan kawai ya jefar da wayan ya runtse idanu yana dunkule hannu yana karanto ayyoyin Allah, Allah kabani ikon controlling zuciyata, Allah kabani ikon controlling zuciyata, saiya tashi yawuce yashiga closet yaciro jean yasaka yasaka t-shirt fara kirjinsa kawai dukan uku iku kawai yake yakasa believing baiga Amirah dasuke kwance tare ba, saiya sake fitowa yadauki wayansa number Mami yayi dialing just to be sure kaman Mami bazata dauki wayan ba tadaga tai shiru, cikin muryansa data karkace sosai yace  Mami dan Allah Amirah na wurinki ?"

"Muryansa kadai Mami taji tace  meya faru? She s not here gabansa bugawa yayi rasss, da kyar ya tattaro kuzari yace  don t worr& .  Marwan I said what happened? Kaman bazaiyi magana ba ahankali yace  banga Amirah bane Mami cikeda tashin hankali Mami tace  mene? Bangane bakaga Amirah ba ? Dasauri yace  ina zuwa Mami kaman ga Abba nan yazo Mami tace  Abba? Kawai tamike tadauki hijabi tazura tafito, saukowa kasa Marwan yayi Abba dake tareda driver nasa dake takasa yabude bayan motan yashigo gidan yana kallon Marwan yace  meke faruwa Marwan bai basa amsaba yacigaba da tafiya yashiga falo Abba ya bisa yace  meke faruwa? Why did you call me here you look so scattered? Kallon Abba Marwan yayi yabude baki zaiyi magana saiga hawaye hannuwansa biyu yadaura akan idanunsa yarike sAbida yahana hawayen zuba wlh bashi yake kuka ba kawai hawayen zubowa suke daidai Mami na shigowa falon sanye da hijab ta tsaya turus itama tana kallon Marwan yanda Abba ke kallonsa, dasauri ta matsa takai hannu ta kama kafadan Marwan cikeda so tace  kai Marwan, menene? Zare hannuwansa yayi dagakan idanun ya goge fuskansa tasss yamaida glasses dinsa yasaka yakalli Mami da"

Abba yace  jiya bayan sallan isha i dana ke dawowa gida i saw Saleem anan kofar g1da yay shiru bai fadi

maganan giyan ba dudda shi Abba dazai shigo gidan yaga kwalban gida daya fashe awajen kuma wlh

"saida zuciyabsa takawo masa Saleem, ahankali yace  we had little disagreement dai nashigo na kulle gidan nashiga falo shima na rufe na kashe komi as usual nawuce sama yayi shiru Abba yace  saime yafaru? Ahankali Marwan yace  bansan ya akayi ba he got the key na gidan nan yashigo har sama thankfully nasa key a kofarmu na bedroom saisa key dake wajensa couldn t work Abba yace  Innalillahi wa innailaihi raji un Mami tace  I saw him jiya da daddare nafito daga kitchen yana saukowa daga bene I was trying to talk to hi  ahankali Marwan yace  Mami shiru Mami tayi suka kallesa, ahankali yace"

" this morning mun tashi dagani har Amirah munyi salla mun koma bacci, yanzu na farka ban ganta ba! "

Atare daga Mami da Abba sukace mene? .

EPISODE

Saiga hawaye yasauke kansa kasa yace  babu inda ban dubawa agidan nan ba banganta ba Amirah is not

"in this house Abba yace  Innalillahi wa innailaihi raji un! Yashiga ciro wayansa Marwan ya goge hawaye yace  idan Saleem zaka kira he s still here yana sama Abba yace  what! Yana sama? Anan ya kwana? Gyadamai kai Marwan yayi yana lumshe idanu, Abba yawuce yayi sama azuciye Mami tabisa"

Marwan ya tsaya yabisu da kallo kafin shima yabisu saman.

Turus Abba ya tsaya dayakai karshen stairs shi dayaji ance yana sama yadauka yasami wani daki yama

"shige ya kwana ne but no Saleem na kwance akasa gaban master bedroom gaban dakin ma aurata, kirjin Abba dukan uku iku kawai yake ganin kanninsa na jini ciki daya, uwa daya uba daya yake abun nan, Mami itama just found kanta in a situation da sai tama kasa magana ta tsaya itama, Abba yakai minti daya tsaye awajen saiya yunkura cikeda karfin hali yakarasa gaban dakin hannu yasa yawani fizgo Saleem din zaune shuuu yabiyosa Abba ya kauda kansa sabida wani warin giya dayaji yanayi, saiya dawo da kansa ya kallesa still bacci yake ya bubbuga fuskansa  Saleem, Saleem, Saleem amman ina shiru sakinsa Abba yayi yakoma sharap ya kwanta Abba yatashi yashiga kalle kalle nan falon saman ya hango bottle water akan table yatashi dasauri yawuce yaje yadauki daidai Marwan na zuwa saman, Abba yana zuwa yabude ruwan yashiga tsayayawa akan fuskan Saleem da afirgice yatashi dan ruwan sanyi sabida AC ya yunkuro yatashi ya zauna daman tsabagen maye ne yasa since yakasa motsi kaman mai paralyzed idanunsa sunyi jajir ya shiga fuzar da baki yana yatsine fuska yana kakkabe duwan daya kama wanke fuskansa da wuyansa some har kunnensa yana kakkabe kunnensa Abba ya duka gabansa strictly yace  Saleem dago jajayen idanunsa Saleem yayi yakalli Abba yahade fuska sosai, strictly Abba yace  ina"

Amirah? Saleem banson tashin hankali? Kokai mayene yakamata ka hakura tunda an daura mata aure

"dawani bayan ka gudu, Marwan yatashi this morning baiga Amirah ba, she s nowhere to be found, nasan"

"somehow you have something to do with it, kafadamin inda Amirah take ko wlh zan mikama hukuma kai amaka hukuncin daya dace dakai, for the last time Muhammad Saleem ina Amirah? Tunda Abba ke maganan

44 / 51