KIDA A RUWA BOOK1 BY BILLYN ABDUL

Author :  Billyn Abdul Category :  Adventure

Chapter   23 / 49

66K to 69K   out of 146.5K words

dan har abada bazasu ga Haysam Abdul-rasheed a ƙasan takalmansu ba in sha ALLAHU”.
         “In sha ALLAHU kuwa ƴan wahala.”

__________★

      KOMAI NISAN JIFA....

   Alƙawarin ALLAH ya cika. Shekaru sun wuce cikin wahala da zafi, ƙura da ruwan sama harma da sanyi. Haysam Abdul-rasheed Shehu da abokinsa Imran Abbas sun girma a cikin NDA kamar ƙasar da take haifar da ƙarfin hali da gwagwarmayar neman ƴanci.. Tabbas zuwa yau an manta da lokacin da ake kiransu “new boys.” Yanzu sune manya Seniors dake faɗa aji da shugabantar masu shigowa har ma da masu bi musu. Tabbas shekarar ƙarshe shekarar ƴanci amma shekara mafi tsaurin gwagwarmaya da karatu mai tabbatar da yaro soja. Haka su Zak-Shadow sukai juriya ƙwarai da gaske wajen tsallaketa tamkar yanda suka shallake na baya da suka shuɗe. Alhamdullah ga burin ƴan maza ya cika, NDA ta zama tarihi tamkar yanda primary da Secondary suka zama tarihi suma.
       A daren da suka karɓi takardar kammalawa, Zak-Shadow ya tsaya yana kallon harabar NDA, zuciyarsa cike da tunani. Wajen da ya sha ruwan sama, gudu a cikin laka, da azabar push-ups har yatsunsa suka kumbura, yau shi ne wurin da zai barwa tarihin da sai dai a tuna a bama ƙanne da ƴaƴa labari watarana.
      Imran ya matso kusa da shi murmushi na bayyana cikin fuskarsa mai tarin nutsuwa, “Zak-Shadow” ya kira sunansa da murya mai sanyi, bai jira amsawarsa ba ya cigaba da faɗin, “ka tuna ranar farko da muka shigo nan?”.
       Juyowa yay yana kallonsa fuskarsa da murmushi mai nauyi, cikin buɗaɗɗoyar muryarsa mai fita da amon mazaje ya amsa masa da, “Idan zan mance da wannan ranar tabbas zan mance da kai My Imran. Yanzu kamar jiya ne... kai da kukan nan naka da yasa na tsaya ina kallonka tamkar Ma'aruff ko Ja'afar a gabana”.
      A tare sukayi dariya, abinda Zak-Shadow bai cika son yi ba. To dama mai ganin suruntun nashi kamar hakan sai dai Imran ɗin ai.
     
      ★Alƙawarin ALLAH ya cika, Haysam ya samu cikar burinsa daya ginu bisa burin mahaifinsa. Ya kammala NDA bayan shekaru huɗu na wahala, gwagwarmaya, juriya da jarumta. A yau suke bikin Passing Out Parade ɗin su, musalta irin farin cikin da yake aciki abu ne mai wahala. Ba shi kaɗai ba, hatta Mammah da ƴan uwansa da malam Sulaiman da kawunsa da yazo daga Bauchi, da Innarsa Khadijah da Alawiyya suna cikin farin ciki. Domin kuwa sun halarci bikin passing out ɗin nasu su duka. Yanzu Haysam ba ɗan takara ba ne, soja ne cikakke, Second Lieutenant Haysam Abdul-rasheed Shehu (Zak-Shadow).
     Sun yi parade a gaban manyan jami’an soja da iyaye da ƴan uwa da abokan arziƙi. Ɗalibai da yawa da suka nuna ƙwazo a fannoni daban-daban sun samu ƙyautittuka na girmamawa, ciki kuwa harda Haysam. Lokacin da aka kira sunan Cadet Haysam Abdul-rasheed Shehu, sai dukan ɗakin ya amsa da ihun kiran sunansa daga mate ɗin nasa.
      “Sarki! Sarki! Zak-Shadow! Zak-Shadow!”.
     Kai kace zasu fasa hall ɗin ne har iyaye da suka halarci taron najin ƙagara da mamakin wane yarone wannan mai farin jini ga yaransu haka?, sai da aka tsawatar musu saboda ihun kiran Haysam da ya kasa miƙewa sai da Imran ya kama shi ya miƙar tsaye. Cike da nutsuwarsa ya tako ya fito inda ake buƙatar ganinsa. Ba ƙaramin ƙyau kayan sukai masa ba, sun zauna a ginannen jikinsa na asalin zakin ga ƙƴawu ga nutsuwa ga addini, dan goshinsa kawai ya isa baka shaidar shi mai ibada ne kodan damɓareren tabon sallar da yake da shi. Ba tabon salla kawai ba a yanayin nutsuwar Haysam kawai zaka tabbatar da akwai ilimin addini sosai a tare da shi..
Zak-Shadow ya amshi lambar yabo ta Discipline and Endurance. Ya kuma samu ƙyautar girmamawa ta Best in Field Tactics & Discipline, abin da ya sa Mammah da ƙannensa suka yi kukan farin ciki a wajen kallon taron da suka halarta. A tare ƙannensa suka tashi mazansu da matansu sukaje suka rungumeshi. A karo na farko idonsa ya cika da ƙyallin hawaye, wannan ba kawai nasara bace, ƙarshen tafiyar jarumta ce da cika burin Abiy da samar da farin ciki a zukatan ƴan uwansa da Mammah, inama Abiy na raye ya cimma wannan rana.. isowar Imran daya ɗan buga kafaɗarsa da dariya ya sashi haɗiye hawayen nasa. Sai kuma ya juya yana kallonsa, suma ƙanensa sakinsa sukai suka koma wajen zamansu.
      Kashe masa ido ɗaya Imran yay da faɗin, “My Zak-Shadow yanzu zai koma gida a matsayin soja na gaskiya. kaga yanda Mammah take kukan murna ita da su Ma'aruff.”
      Haysam ya murmusa, yana mai lumshe idanunsa ya sake buɗewa akan su Mammah sannan ya dawo da su kan Imran.
         “Tabbas Mammah tana kuka ne irin na farin ciki da cikar burin mijinta Imran, ba kukanta ita kaɗai take ba harda kukan Abiy da Umma duk a tare. Amma nima ba zan taɓa manta nan ba Imran. Wannan wuri ya juya ni daga maraya marar gata, zuwa mutum mai ƙarfi da damammaki da samun cikar burin mahaifi. Imran in sha ALLAHU sai na kaima Abiy wannan albishir har Bauchi a gobe-goben nan in dai ina da rayuwa”.
         “ALLAH ya cika maka burinka, kuma ba kai kaɗai zaka Bauchi ba harda Imran Abbas ɗan Abiy da bai sani ba”.
       Wani ɗan dukan basawa Zak-Shadow ya bama Imran a kafaɗa, sai kuma ya rungume shi hawayen da yake ta shanyewa suka samu damar ɗigowa. Shima Imran hawayen ne ke zubo masa. Yana ƙaunar Haysam, yana tausayinsa ƙwarai da gaske. Dan shi har yanzu bai san maraici ba, uwa da uba duk suna raye, kai shi tunda yasan kansa ba'a taɓa mutuwa a gidansu ba ma gaskiya. Sai dai a dangi haka sai kakarsu da ta rasu yana yaro sosai. Sannan gidansu su suna da kuɗi.........✍🏼



_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*


*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*


*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*


*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*


*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*


*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*


*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._



_Chapter 33_

__________________

https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt
Link na grp


07077532253
https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm


https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok

IMZEEDVENTURE
Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu.

Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa?

Kayan yara masu kyau unique na yan gayu?

To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo!

Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳.

IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu.

Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki.

https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1.

Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_*

Muna da account aTikTok@imzeed _venture.
https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1

Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃

__________________


*_TELEGRAM GROUP_*

https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk


*_WHATSAPP CHANNEL_*

https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F

*_TIKTOK_*

https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/

*_INSTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

______________________

.......Zak-Shadow da su Mammah sun wuce Kano, zasuyi hutu na makwanni har shida. Ashe walima Mammah ta shirya masa. Dan haka suka iske gida cike da danginta anata girki. Ƴan Bauchi dai iya kawunsa ne kawai sai Khadijah da Alawiyya suka zo. Bai damu ba, wanda ya gani ɗin ma sun wadatar. Anci ansha an masa addu'oi kala-kala harda mutanen anguwa.
     Bayan kwanaki biyu gida ya koma sai su kaɗai, Zak-Shadow ya sake fahimtar rayuwa ta canja ga mahaifiyarsa, ta tabbata dai bata tare da sabon mijinta. Sai dai yanzun ma bai tambaya ba saboda girmamawa har sai da Mammah ta sanar masa komai a wannan karon da bakinta. Tabbas zuciyarsa ta hasala matuƙa, amma bai ce komai ba dai a zahiri. Itama Mammah data fahimci yanayin nasa sai tai masa nasiha da gargaɗinsa akan kar taji wani abu daga garesa. An riga anyi ya wuce sai a tari gaba. Badan yaso ba yay shiru kamar yanda ta gargaɗe san.
      A cikin wannan hutu ya samu damar bibiyar karatun ƙanensa, har zuciyarsa kuwa ya gamsu da yanda komai ke tafiya Alhamdullah. Musamman ma su Ja'afar ƴan Secondary. Ya ji daɗin kuma ganin yanda kasuwar Mammah tai tasiri a gida. Ya ziyarci Malam Zayyanu da abokinsa Malam Datti. Sun masa addu'a sosai da nuna jin daɗin nasarar da ya samu a NDA.
     Duk da yana cikin hutu bai daina yin motsa jiki da safe da yamma ba, kamar yadda suke yi a NDA. Wani lokacin idan yana fama Mammah har faɗa take masa ya huta. Yakan yi murmurshi ne kawai ya ce, “Mammah idan banyi ba jikina zai yi ciwo ne”.
    Haka dole ta ƙyaleshi har hutunsu ya ƙare, kamar kuma yanda yay alƙawari yaje Bauchi tare da su Ma'aruff cikin weekend. Sun ziyarci kabarin mahaifinsu da Umma har ma da kakaninsu su Malam. Babu wanda yasan yaje a ƴan uwan mahaifinsu sai kawunsu Jamilu kawai, dan basu kwana ba a ranar suka juyo Kano.
       A watan Agusta ya koma Jaji, domin yin Young Officers Course, inda ya sake haɗewa da Imran, a wannan karon ma a ɗaki ɗaya suka zauna, dan sai da sukai duk yanda zasuyi aka haɗasu cikin amincewar UBANGIJI. Alhamdullahi sun kamalla course ɗin su a farkon shekarar 1999, daga nan kowa aka turashi inda zai fara aiki. sai dai an samu matsala dan anyi posting ɗinsu waje daban-daban shi da Imran, amma da yake suna da oganni tuni suka nema oga Adetunji suka sanar masa damuwarsu. Shine yay ta kai kawo har aka haɗasu waje ɗaya yanda suke fata, antura su aiki zuwa 82 Division Enugu, inda suka fara rayuwar soja ta zahiri. A can suka gane cewa aikin soja ba na jarumtaka kaɗai ba ne, aikin zuciya da sadaukarwa ne.

★Su Zak-Shadow na Enugu cikin sabuwar rayuwar aikin soja, anan rayuwar Mammah da marayun ƴaƴanta na neman canja salo da fuskantar sabuwar jarabawar rayuwa. Domin kuwa Zak-Shadow bai wuce watanni uku a Enugu ba Tasi'u ƙanin Mammah ya zo kwatsam. Zuwan daya saka Mammah a farin ciki dan tayi tsammanin har abada ta rasa dukkan ƴan uwa a duniya.
       Da farko dai kamar abin arziƙi tsakaninta da Tasi'u, dan harda zama ya bata labarin rayuwar da yake ciki ta tashin hankali. Yarinyar daya aura basu ko ƙulla shekara ɗaya ba a rayuwar aure suka rabu, ya shiga halin rayuwa mai tsanani a sabuwar ƙasar da bai san kowa ba, haka ya jure saboda karatun da yake yi. To zuwa yanzu ya kammala, acewarsa har ya samu aiki, yanzu ma yazo gida ne domin wani aiki da zai yi na wata uku ya koma. Mammah ta jajanta masa ta kuma tayashi farin ciki.
      Sunyi sati kamar uku a wannan farin cikin kwatsam rana tsaka sai ga Tasi'u da lauyoyi har biyu da wasu mutane, wai yana son a raba gida a bashi nashi kaso. Mamaki ya kama Mammah, ta kalla gida ta sake kallo, tabbas gidansu babba ne, gashi a bakin titi, kusan a yanzu ma gidan yafi duk wani gida na layin ƙyau saboda gyaran da Alhaji Nura yay masa lokacin daya aureta. Da farko ta ɗan so tirzawa tai masa faɗa, ya nuna mata shifa ba yaro bane, sannan gidan nan dai yana da hakki ai kuma dolene a bashi nashi hakki. Ganin yana son su zubar da mutunci a anguwa tace ba damuwa yayi duk yanda yaso, ko ɗaki ɗaya ta samu ALLAH ya amfana zata zauna da yaranta. Haka kuwa akai yayta shiga da fita batare daya bari tasan yaya komai yake tafiya ba. Kwatsam a cikin wata na biyu da zuwansa ta nemeshi ta rasa. Duk inda ya kamata ta bincika kuma tayi amma babu shi. Hankalinta yaso tashi kawunsu yace karta damu kanta, ta barshi duk ma inda yaje zai dawo tunda ba yaro bane. Haka dole ta haƙura ta share. Abin mamaki cikar wata ɗaya saiga wasu mutane wai sunzo gidan nan da take ciki nasu ne an sayar musu, suka nuna mata takardu harma da shaidun gani da ido da akai ciniki da su. Hankalin Mammah ya tashi kwarai da gaske, sai ta rasa inama zata saka kanta dan tashin hankali, kawai ta yanke jiki ta faɗi sai da aka kaita asibiti. Kwananta biyu aka sallamota, abu dai kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba Tasi'u ya saida gida ya gudu. Masu gida kuwa sun bata wata ɗaya kacal suna buƙatar gidan akwai abinda zasuyi da shi.
     Wannan tashin hankali ya saka Ma'aruff da Ja'afar sulalewa suka tafi Enugu suka sanar ma Zak-Shadow. Kwatsam babu zato ya gansu, mamaki ya kama shi ya balbalesu da faɗa domin a ganinsa ai kasada ce zasu kamo hanya batare da sanin gari ba su taho. Su dai haƙuri suke ta bashi, Imran dai ya kwacesu da ƙar, shine ya basu abinci sukaci ya basu wajen kwanciya. Zak-Shadow bai saurarensu ba sai dare, anan ne suka sanar masa abinda ke faruwa da halin da Mammah ke ciki, suka tabbatar masa a yanzu ma sunzo ne bada saninta ba, dan sun tabbatar tana can tana nemansu ƙilama hankali a tashe..   
      Jin wannan zance ya sake ɗaga hankalin Zak-Shadow, haka ya samu da ƙyar da kamun ƙafa aka bashi damar zuwa gida kwana uku kawai. Ya taso ƙanensa gaba suka nufi Kano. Aiko hasashen su ya tabbata, dan sun sami Mammah cikin tashin hankalin rashin sanin ina su Ja'afar ɗin suke, sai kuma gashi ta gansu harda uban gayya Haysam. Kukan dake danƙare da ƙirjinta sai a lokacin ne ta samu ta yi shi. Wannan al'amari ya sosa zuciyar Zak-Shadow matuƙa. Wanda ma bai san fushinsa ba a wannan karon ya gani kwarai da gaske.
     Ɗan kuɗin albashinsa da yake faman ajiyar taro da kwabo a account ya kwashe domin sayen fili, sai dai a karo na farko Kano ta fita masa a rai gaba ɗaya, yana son yin nesa da ita nisa mai yawa ko mahaifiyarsa zata samu salama tamkar yanda ta baro Bauchi, amma kuma bai san ina zai maidasu ba, dan haka ya nema shawarar Imran ta hanyar kiranshi a wayar landline. Babu wani ja'in-ja Imran ya bashi shawarar zuwa Abuja kawai, ya kuma haɗashi da yayansa.
    A ranar Haysam ya bar Kano zuwa Abuja. Inda da taimakon yayan Imran suka samu fili suka saya. Sauran kuɗin daya rage ya sayi siminti da bulo aka fara ginin ɗakuna ƙwara biyu kacal. Kwana uku aka bashi kawai a wajen aiki, dan haka dole ya koma Kano yabar sauran aikin wajen yayan Imran. Yana zuwa Kano ya sanar ma Mammah komai, mamaki ya kamata sai kuma ta shiga yi masa faɗa akan dammi zai yi hakan. Shi dai kansa a ƙasa kawai yana bata haƙuri ne. Sai da ta kammala yace su fara shiri kawai, nan da kwanaki kamar goma zasu koma can shi kuma ya shirya ya koma Enugu.
      Haka kuwa akayi, kwanaki goma bayan komawar Zak-Shadow yayan Imran yazo har Kano da mota ya kwashi su Mammah da yaranta. Tafiyar data sakata kuka sosai, jikin ƴan uwanta yay sanyi da rashin taimakonta da basuyi yunƙurin yi ba har Haysam ɗin ya yanke hukunci. Dan sun so hanata da nuna mata zasu ɗauki mataki tace ba komai zata koma Abujan kawai dan itama bata son zaman Kanon a yanzu.
    Wannan shine sanadi kuma mafarin barin Kano dasu Mammah sukai suka dawo Abuja. Ɗaki ne guda biyu kawai, sai aka zagaye gidan da kwanon langa-langa. Dan Zak-Shadow ya nuna baya son taimakon komai daga wani saboda Yayan Imran yaso yin hakan. Shima kuma Imran ɗin yaso yin hakan amma ya haƙura dan yasan wanene Zak-Shadow, idan yace baya son abu to kawai baya so ɗin da gaske.
     Yana sake ɗaukar albashin watan ya nufo Abuja, kuɗin yay amfani da su wajen maida ƙannensa duk makaranta, su Ammar ma da ba'a saka ba ya sanya su. Dama Mammah tunda suka dawo bata zauna ba, haka ta dinga shiga tana fita wajen nunama mutane kayan sana'arta ta koli. Sannu a hankali aka fara ganewa, kasancewar sabuwar anguwa ce kafin mutum yaje kasuwa sai yafi ganewa zuwa wajenta sayen abu a sauƙaƙe. Ganin haka ta fara haɗawa da kayan miya, da wannan sana'ar da albashin Zak-Shadow suka cigaba da rike rayuwarsu, idan an samu ɗan rarar kuɗi a sai siminti a ɗan ɗora gini. Kwatsam sai kuma ga wata ƙaddarar ta sake afkawa Zak-Shadow lokacin da yake shekara biyu da fara aikinsu, wai ya buɗe wata gaskiya wani ogansu yayi kutun-kutun an saka shi a prison. ALLAH sarki rayuwa, a wannan gaɓar ALLAH dai ya ƙaddara Mammah kam bazata rasa ranta ba. Dan bama ita kawai ba hatta su Ma'aruff sun shiga wata irin gigitar rayuwa.
    Haka Mammah ta dinga bin duk wanda ta sani cikin roƙo da magiya don ganin Haysam ya kuɓuta. Amma ina, Imran ma iya bakin ƙoƙarinsa yake amma al'amarin kamar da wani babban shiri a cikinsa. Hatta su Adetunji sunyi iya yinsu Zak-Shadow bai fito ba. Ga baƙar wahala suna bashi ta tashin hankali kamar sun sami criminal, duk mai hankali yaga wannan al'amari yasan akwai lauje cikin naɗi a ciki, sai dai kai tsaye basu san wa zasu fuskanta suce yayi ɗin ba..........✍🏼


_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000

23 / 49