Author : Billyn Abdul Category : Adventure
da ita, amma tare da rakkiyar danginta itama.
Bayan A'isha ta dawo gidan aurenta sun sake gina sabuwar rayuwa da mijinta Abdul-rasheed da ɗansu. Ya ɗauketa zuwa Maiduguri dangin mahaifiyarsa a karo na farko, sun yo musu sati har biyu. A kuma wannan zuwa ne shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakanin A'isha da Yakura, idan bamu manta ba Yakura dai itace akama Abdul-rasheed tayin aurenta a lokacin bikin ƙanwarsa Khadijah. Yarinya ce mai natsuwa da hankali, ga haƙuri da ilimin addini, ga ƙalubalen rayuwa da take fuskanta hannun mijin mamanta saboda marainiya ce babanta ya rasu. A wannan zuwa ma su Baba Kalla sun sake kwaɗaitama Abdul-rasheed auren Yakura, halin daya sake ganinta a ciki kuma yasa ya amsa babu wani jayayya, koda ya tunkari A'isha da maganar tun a can sai yaga tanata farin ciki. Hakan ne ya saka masa nutsuwa yana dawowa ya sanar ma Baba. Baba yayi murna sosai kuwa shima, ya kuma saka masa albarka. Daga haka aka shiga kai-kawon maganar aure.
Mata nada ba kishi ne basu da shi ba, zata iya yiwuwa ma sunfi matan yanzu kishi sosai. Sai dai akwai dattaku da kamun kai da sauƙaƙawa zuciya damuwa dama ɗaukar rayuwar aba komai ba. Dan haka A'isha koda ta nuna murnarta a fili a ɓoye tasha kuka, dan kuwa tana son mijinta sosai, amma son da take masa bazai saka ta tauyesa akan ƙarin aurensa ko bijire masa ba, ita dai aljannarta take nema da burin samu a wajen UBANGIJIN da yace ai aure kuma ayi biyayya ga maza, suma kuma su sauke haƙƙokinmu, wanda bai sauke ba kuma zaiga sakamakonsa. Iya ƙoƙari mijinta nayi akan ƙyautata mata da sauƙe hakkokinta dake kansa, ya ɗauki ɗawainiyar Innarta da karatun ƙannenta su Bashir, ga kulawar da Haysam ke samu ta musamman irin ta ɗan gatan ɗa, to mi zaisa kuma ta butulcema ALLAH. Yayta aurensa zata bishi da addu'a da kuma fatan zaman lafiya ita da amaryar. Dan a wajenta Yakura abar a tausayama ce ga duk mai imani. Gefe ɗaya kuma har cikin ranta son Yakura take ji, dan haka kawai ALLAH ya haɗa jininsu....
Haysam nada shekara ɗaya da wata ɗaya akasha bikin Abdul-rasheed da amarya Yakura, itama dai an kawota nan gidan kusa da A'isha, Alhmdllh kuma A'isha tasha yabo ga dangin mahaifin Abdul-rasheed dama na mahaifiyarsa saboda dattakon data nuna ƙwarai da gaske akan auren nan kamar ba ƙaramar yarinya ba. Babu wanda zai ce yaga fushinta ko ɓacin ranta koda a fuska ne, balle wata magana mara daɗi, hatta shi kansa ango Abdul-rasheed ma da take kwana take tashi da shi zakuma ayi kishin a kansa babu wani abun ALLAH wadai da zai ce ya gani daga A'isha, hasalima wani abun ita take dagewa akan ayi. Haka dai akai biki aka tashi lafiya kowa na san barka da sanya alkairi da addu'ar zaman lafiya na har abada.
Tsabar kunyar A'isha da nauyinta da Abdul-rasheed keji bai bar aboki ko ɗaya ya masa rakkiya gidan da nufin sayen bakin amarya ba, hatta kuwa da Nasiru. Haka ya shigo shi kaɗai. Kai tsaye kuma ɗakin A'isha ya nufa, abin mamaki sai ya samu ita harma tayi barcinta, Haysam na jikinta shima yana nashi. Ya jima a kanta tsaye yana kallonta da mamaki, har zuciyarsa na masa tambayar wai kuwa anya A'isha na sonsa? To dole yace hakan, yasha jin tarihin matan abokansa idan zasu ƙara aure akan kishi, amma ita ko da wasa babu abinda ta nuna masa mara daɗi, kuma dai ance kishi nan na mata shike nuna tsantsar soyayyarsu gareka. Haka dai yayta saƙawa da kwancewarsa, daga ƙarshe yay musu addu'a ita da Haysam ɗin ya kashe mata fitila ya fito tare da karo ɗakin ya nufi ɗakin amarya.
Washe gari ma Abdul-rasheed yata zuba ido yaga canji ga A'isha ko'a fuska amma shiru, sai ma wani annuri data tashi da shi da farin ciki. Wanda ya sashi kasa gane daga ina ta samosa. (Bai san daga sallar dare bane. Dan cikin dare ta farka tai alwalarta a cikin ɗaki a botiki, ta shiga kaima UBANGIJI buƙatunta da addu'ar zaman lafiya da kwanciyar hankali ita da amarya da shi, Alhamdullahi kuma ta tashi ranta fes babu wani damuwa balle nauyin zuciya da take fama da shi a kwana biyun nan). Haka yay ta binta da kallo, musamman da zasuyi kari yaga ita da Yakura nata shan hirarsu hankali kwance kamar ma wasu ƙawaye. Kai daga ƙarshe ma sai bar musu gidan yayi, koda ya dawo samunsu yay suna aiki a tsakar gida suna hirarsu cike da nishaɗi da dariya. Ga Haysam a bayan Yakura a goye tana ƙulla aya da gyaɗar saidawa da A'isha keyi. Ita kuma tana girki. Harga ALLAH sai ya sake jin nutsuwar zuciya da kwanciyar hankali, harma da son A'isha yana sake nunkuwa a ransa. Dan haka da daddare ya sake haɗasu yay musu nasiha da roƙon su ɗore a yanda suka fara, su toshe kunnensu daga munafukai, su kauda idonsu daga azzalumai masu haddasa fitina a bayan fage. Sun tabbatar masa zai samesu fiye da yanda yake fata, suma kuma sun roƙeshi ya kasance adali a tsakaninsu mai tsayar da gaskiya. Shima ya amsa da tabbatarwa...
Tabbas Alhamdullah, babu abinda Abdul-rasheed da Ai'sha da Yakura zasu ce a wannan gaɓar sai tarin godiyar ALLAH. Dan kuwa gidan aurensu ya zama gidan farin ciki da ni'imarsu da kwanciyar hankali. Bawai basa kishin bane, sunayi, sai dai kowacce tana yin kishi mai amfani wajen ganin ta ƙyautata ma mijinta a ɓoye batare data sosa zuciyar ƴar uwarta ba. Haka shima mijin na ƙoƙarin yin adalci, wadda yafi so kuwa ya barma ransa ne.........✍🏼
_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._
*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*
*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*
_Shaidar biya👇_
*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*
*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*
*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*
*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull
*_WHATSAPP (500)_*
*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*
*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*
*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*
*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_Chapter 20_
__________________
_A KANO KI KE…? Kina neman inda zaki siyi abinci mai daɗi? Kina ƙiyar yin girki gashi zaki yi baƙi?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daɗi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daɗi akwai a lallaɓa. Kina son ki siyi abincin da zaki ɗauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daɗi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan ɓangare, tazo muku da nau’in abinci kala-kala na gargajiya da na ƙasar waje. Tana siyar da MANDI RICE, GRILL CHICKEN, CHICKEN BIRYANI, FUNKASO, ALELEN GWANGWANI, BREAD POCKET da sauran su. Fannin abin sha akwai natural ZOƁO mai zaƙi, wanda aka yi shi da ingantattun kayan marmari masu ƙara lafiya, akwai wanda bashi da zaƙi domin masu ciwon sugar da masu gudun ƙiba._
_me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram ko TikTok domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ƙasan rubutun nan._
INSTAGRAM
👇🏻👇🏻👇🏻
https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr
CALL/WHATSAPP
👇🏻👇🏻
wa.me/2349030398006
TIKTOK
👇🏻
https://www.tiktok.com/@leemars_delicious?_t=ZS-90ZQJ2mNJKc&_r=1
Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuɗi gida.❤️❤️🫶🏻
__________________
*_TELEGRAM GROUP_*
https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk
*_WHATSAPP CHANNEL_*
https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F
*_TIKTOK_*
https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/
*_INSTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
______________________
........Sakanni sun zama mintuna, mintuna sun koma awoyi, awoyi sun rikiɗe zuwa kwanaki, kwanaki sun haɗu sun zama sati, satittika sun dunƙule zuwa wata, wattani suka haɗa shekara. Shekaru sun cigaba da shuɗawa. Har amarya Yakura ta cika shekara uku a gidan Abdul-rasheed. Bata samu ciki ba har yanzu, hakama A'isha tunda ta yaye Haysam shekara biyu kenan bata samu wani cikin ba. Abdul-rasheed kuwa nata sake samun ɗaukaka a wajen aiki da kasuwancinsa na ɗinki, dan zuwa yanzu ya koyar da yara da yawa aikin tela, kuma Alhamdullah suma suna cin gashin kansu, ga shagon saida kayan ɗinki ya buɗe duk sati Nasiru na aiko masa da kaya daga kano. Wani lokacin kuma yaje da kansa yayo daga nan yayo zumunci ya siyama Inna kayan abinci ya dawo. Zuwa yanzu kusan duk ɗawainiyar zuri'arsa ta dawo kansa ne. Yayima su Baba yayima yayunsa da ƙannensa, yayi ma dangin mahaifiyarsa, yayima dangin matansa. Sannan ya sauke hakkin gidansa. Haysam yaro ɗan shekaru huɗu a duniya, ya tasa abinsa masha ALLAH, kyakkyawa mai lafiyar jiki ga gatan iyaye dana kakanni, ya tashi yaro mai shiru, mai son karatu da tambaya. Wayonsa ya girmi shekarunsa, damma baida surutu ne. Yana da shekara biyar a duniya kwatsam a ɗan tsakanin sai ga A'isha da ciki, ya salam zo kaga murna wajen Abdul-rasheed da Yakura dama su Baba, cikin A'isha nada wata biyu itama Yakura ta fara nata laulayin, ya rabbi, rasa ina Abdul-rasheed zai saka kansa yayi dan farin ciki, dan harga ALLAH yana matuƙar son yara. Kamar yanda A'isha ta fara samun ciki itace ta fara haihuwa, santalelen yaro namiji a wannan karon ma, mai kammani da Abdul-rasheed shima. Ansha shagali yaro yaci suna Ja'afar. Ja'afar nada wata biyu da kwanaki itama Yakura ta sauka, itama dai ta santalo nata namijin mai kama da Abdul-rasheed, shima dai yaci suna Ma'aruff. Haysam cike yake da farin cikin samun ƙanne da suka tashi tamkar tagwaye, dan kuwa ma tagwayen ake kiransu. Su Ja'afar nada shekara ɗaɗɗaya aka saka Haysam makaranta, dan kuwa ya cika shekaru shida a duniya cif.
Duk da kuwa kafin ma sakashi makarantar tuni ya fara ɗaukar karatu a wajen mahaifinsa da ma A'isha da Yakura. Dan Abdul-rasheed tsaye yake akan tarbiyyar Haysam, sannan akwai shaƙuwa a tsakaninsu mai girman gaske. Akoda yaushe zaka sameshi zaune a gefen mahaifinsa yana sauraron karatun Alƙur’ani ko labaran tarihi na Annabawa da jarumai. Hakama sauran litattafai dai-dai fahimtar yaro mai irin shekarunsa. Duk lokacin da mahaifinsa ya karanta masa tarihin jarumtar Annabawa data sahabban MANZON ALLAH (S.A.W) irinsu Abubakar As-Siddiq (RA). Abokin ANNABI mafi kusa kuma khalifa na farko, mai haƙuri da sanyin hali Umar Ibn Khattab (RA). Khalifa na biyu, adalin shugaba jarumi kaifi ɗaya. Usman ibn Affan (RA). Khalifa na uku, ya tattara Al-Qur’ani cikin littafi, mai yawan ƙyauta kuma mai sadaukarwa ga bayin ALLAH mabuƙata. Aliyu ibn Abi Talib (RA). Khalifa na huɗu, kuma ɗan’uwan ANNABI, jarumi da baya tsoro sai dai kafirai suji tsoronsa, dan ya basu wuta iya wuta a filin daga, Mijin Nana Fateema ƴar MANZON ALLAH (S.A.W). Ga su Abdulr-rahaman ibn Awf (RA). Irinsu Sa'ad ibn Abi Waqqas (RA). Talha ibn Ubaidullah (RA). Zubair ibn Al-Awwam (RA) ɗan uwan Ummul Muminin Khadija. Bilal ibn Rabah (RA), mai kiran salla na farko jarumi na gaske. Salmanul-farisi (RA) da ire-iren su da yawa da in lissafosu zamuyi da irin rawar da suka taka a musulunci da tsayawa kusa da MANZON ALLAH mu kammu mun san jarumai ne abin koyi da ba Haysam kawai ba ƴaƴanmu ma ya kamata ace muna basu tarihinsu domin su tashi da burin koyi da su ba zindiƙan wannan zamanin ba da yaranmu ke koyi da su koyi mara amfani da amfanarwa. A ɓangaren hikayoyi yana bashi irin nasu Iliya ɗan Mai Ƙarfi, Jatau Ɗan Mariya, Sarkin Zamani, da makamantansu. Dan a wancan lokacin, ana yaɗasu a gidajen rediyo kamar su rediyo Nigeria da jaridu irinsu Gaskiya tafi Kwabo da sauransu.
Irin waɗan nan tarihi da hikayoyi sunyi tasiri matuƙa a zuciyar Haysam, dan har yana ji a ransa yana son yayi koyi da su wajen hidimtawa addini. Sai dai abinda ke saka lissafinsa ruɗewa shine zamanin da yake saɓanin nasu ne, tunda shi bai zo zamanin yaƙe-yaƙe ba. Dan haka sai yayta jerama Babansa tambaya. Abdul-rasheed kuwa baya gajiya da bashi amsa, tare da kawo masa misalai akan idan su anyi yaƙe-yaƙe a zamaninsu shi kuma zai iya zama Ɗan sanda, ko SOJA ko wani dai aikin kaki domin bama ƙasarsa gudummawa. Ba wani fahimta Haysam yake da ƙyau ba, amma hakan na sashi jin eh lallai zai iya hakan. A haka ya fara makaranta sai abubuwansa suka sake faɗaɗa. Bayan yaye ƙannensa Ja'afar da Ma'aruff iyayensa sun sake samun ciki kusan a tare, amma Yakura ma ta riga A'isha a wannan karon, dan haka ta rigata haihuwar ɗa namiji mai kama da ƴan uwansa. Shima dai yaci suna Bilal, bayan wata uku da kwanaki itama A'isha ta haihu mace. A karo na farko Abdul-rasheed ya samu mace, dan haka taci suna Halimatu mahaifiyarsa Iya kenan suna mata alkunya da (Ummie). Itama dai akasha shagalin sunanta. A wannan lokacin ma Yakura ta sa sake yin gwanne kuma, dan Bilal nada shekara ɗaya ta sake samun ciki, dole A'isha ta cigaba da shayar da Bilal da Ummie a tare, aka bar Yakura da laulayin sabon cikinta har ALLAH ya kaishi haihuwa ta haifi mace itama da taci sunan Inna wato Karimatu suna mata alkunya da (Mommy).
Bayan haihuwar Mommy babu jimawa UBANGIJI ya amshi ran Baba, jiyyar kwanaki biyu rak. Wannan rasuwa ta girgiza wannan zuri'a, barema Inna data koma kamar ta ruɗe. Haka dai akasha kuka da kai-kawo kowa ya haƙura a ƙarshe. Ashe wata na tafe, dan Inna na cikin takaba itama dai ciwo yay mata tsanani, ta matuƙar sakama kanta damuwar rashin baba, ashe itama ciwo ne na tafiya, itama dai a cikar wata na shida da rasa baba tabi bayansa. Su Abdul-rasheed suka sake gigicewa da ƴaƴanta. Nan ma akasha kuka kowa kuma ya haƙura, shike nan gida ya faɗi, an bar su Abdul-rasheed daga su sai dangi. A lokacin Haysam nada shekara goma sha ɗaya a duniya. Yana primary 5, yana shirin gamawa kenan ma, tunda aji 5 ce a lokacin 1983. An gama kukan rasuwar su Baba da Inna babu jimawa itama mahaifiyar Yakura ta rasu, haka suka kwasa sai Maiduguri. Satinsu guda suka dawo ko muce A'isha da Abdul-rasheed suka dawo tare da yara. Yakura sai data ƙara kusan sati biyu ma sannan ya dawo. A lokacin A'isha ta sake samun ciki, cikin daya dinga bata matuƙar wahala, daga ƙarshe ma ta haifeshi a bakwaini, har sai da aka sakashi cikin kwalba na wasu watanni, ita kuma tasha jiyya tamkar bazata rayu ba, mafi yawan mutane idan suka je dubata gani suke kafin su ƙaraso gida za'ace A'isha ta rasu. Abin birgewa kuma Yakura ke jiyyarta kai bakace kishi bace ba sam. Haka dai tasha fama tsahon watanni kafin ALLAH ya bata lafiya ta miƙe tamkar ba'ayi ba, dan kafin cikar wata biyu jikinta ya murje sarai harta fara dawo da ƙibarta. Kamar jira sai ita kuma Yakura ta shiga nata sabon laulayin cikin.
A yanzu dai Abdul-rasheed nada ƴaƴa bakwai a duniya. Haysam, Ja'afar, Ma'aruff, Bilal, Ummie, Mommy, sai autan A'isha Ammar. Family ya haɗu sai dai Alhamdullah. Ga kuɗaɗe Abdul-rasheed na samu na ban mamaki, sai dai baya tarawa kullum cikin hidimar ƴan uwa yake da ƴaƴansu, kai hatta maƙwafta da abokai cin arziƙinsa suke yi, dan mutum ne mai ƙyauta da hidima. Ga dai kuɗi ana wasa da su, amma idan ka cire gidan da yake rayuwa bai ajiye kaddarar komai ba. Hakan kuma bai taɓa damunsa ba bai taɓa kuma damun matansa ba. Ba shi kawai ba su kansu sun koya daga alkairinsa, ko baya kusa sukan yi a madadinsa da ɗan abinda yake basu da sana'o'in su duk da kuwa ƙananu ne. Abdul-rasheed bai taɓa sayen kaddara koda ta fili ya ajiye ba balle gona idan ka cire ta mahaifinsu da yake nomawa, bayan rasuwarsa kuma aka raba musu gado, daya tashi sai ya barma ƙannensa da suke ɗaki ɗaya ma kason sa. Dan a lokacin ne autan ɗakinsu ke shirin yin aure, shima dai ya gado Abdul-rasheed duk tsawon lokacin nan yana yawon karatu ne, daga ƙarshe dai zaiyi aure a yanzu cikin wannan satin. Auren daya taka rawar gani mai ban tsoro da razanin zuciya a zukatan zuri'ar Abdul-rasheed Shehu Isa Kobi dama al'ummar anguwa, kai harma duk wanda yasan wannan sunan wannan aure ya kawo masa tarihin da bazai manta da shi ba.........✍🏼
Shin miya faru ne a wannan aure daya zame ma wannan zuri'a tambari da bazasu manta ba? Wane ajiyayyen tarihi wannan aure zai bari haka?🥲. Kudai kumuje zuwa dan har yanzu a shinfiɗa muke. Cakwakiyar da shagulgula na gaba🏃🏼♀️.
_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._
*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*
*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*
_Shaidar biya👇_
*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*
*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*
*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*
*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull
*_WHATSAPP (500)_*
*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*
*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*
*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*
*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_Chapter 21_
__________________
https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt
Link na grp
07077532253
https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm
https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok
IMZEEDVENTURE
Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu.
Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa?
Kayan yara masu kyau unique na yan gayu?
To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo!
Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳.
IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu.
Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga