Author : Billyn Abdul Category : Romance
zuwannasa haka muka shiga gari hankalinmu ƙwance muka har cikin gida gabaki ɗaya motocinsa suka shiga ban jira ya buɗemin ƙofa kamar yanda yasababa muka fito mukayi ciki saida nayi masa iso wajan Baba sannan yashiga muka zaune gaisawa mukayi da Baba nabarsu suna magana nashig ciki. A ɗakin Mama ma samu su Maryam ina shiga suka sake ihu nashiga nazauna Cikinsu amma hankalina baya garesu tunda nashiga palourn Baba naji ƙamshin kayan soye-soye naso naci banbari mun gaisa ba nace ina zuwa na cire Hijabin jikina na fice, ƙaton tray na ɗauka zan wuce muka haɗu da Mummy da alamu tafita yanzu shugowarta danna ganta da Mayafi da jaka, Muna gaisawa ina tafiya.
"A'a Marmeeyy ina zakije ne haka sai sauri kike" ta faɗi tana tahowa yanda nake.
"Mummy Cin-cin zani ɗeba Wallh ina shiga palourn naji kamar zanji babu duk abincin dayake cikina naji kamar banci komaiba shine zanje na ɗebo" Mummy ta jijjiga kai.
"Eh lallai Toh Allah ya kyauta inaga idan zaki tafi za'ayi miki kitafi dashi saboda zaki iya hana bawan Allah zama kice sai yazo nan ya amsa miki ko ya kawoki kaɗan daga aikinki shiyasa gara atari lamarin kitafi dashi tun kafin ki aika ɗanyen kai" ko kulawa banyiba nawuce ciki na sameshi suna hira Jifa-Jifa da Baba, Ina shiga Baba ya waigo zuwa gareni.
"Marmeeyy inasu maman naki? Ai ki kirasu Su gaisa koh? Mummynku kam tafita duk da tace ba daɗewa zatayi ba"
"Toh ina zuwa" shine abunda nafaɗa nayi can ɗakin ina murɗawa naji a kulle na juyo,"Baba bani key ɗin can ɗakin zan ɗebi abune"
"Yana wajan Mummynku kuma tafita" najuya nafice na amso key ɗin nazo na buɗe" na ciko trays Damm da Dublan da tayota dama nafi sonsu daga yanda yake zaune ya hangi yanda na ciko abu tamm yatashi dasauri ya ƙaraso gareni ya amsa, turo baki nayi "Babu nauyi fa" Baba ya kauda kansa gefe kamar baya wajan nasa Hannu na ashe kayana ina faɗin "Zakaci?" ya girgiza min ka Banacin zaƙi ai kinsani, da hausa nace "Kabar daɗi" nasa kai nafice, Mummy ta fahimci cewa yana ɗakin Baba yasa bata ƙarasa ba. A corridor na wuceta nace. "Wai kije ku gaisa inji Baba". "Toh marmeeyy kiyiwa su Mamanki magana saimu shiga gabaki ɗaya" na gyada kaina nawuce saboda bakina yacika da Dublan bazan iya magana ba. Kaiwa palourn Mama nayi na dire maryam ta fara saka Hannu.
"Babe idan kikacimin kin shiga hakkina dan ban bayarba" ko takaina batabi ba taɗauka tana faɗin idan akayi na aurena ki faɗamin zan biyaki kayanki" su duka suka saka Hannu suna maimaita abunda tafaɗa, Mama ce tafito daga ɗaki ni sai alokacinma na ganta.
"Marmeeyy kinzo shine koki leƙani ki duba yaya nake anya kuwa marmeeyy yaushe zakiyi hankali?" na curo baki. "Mama ko mutum ya gwada yayi kewarki shareshi kikeyi ko awaya na kiraki saiki ƙi ɗauka ko muna gaisawa kice kina wani aiki jiyafa kiga watanmu nawa ban ganki ba amma ina zuwa jikinki kika tureni shiyasa nima yau ina zuwa na nemi Mummy saboda itake nunamin soyayya" Hannu Mama takai ta ƙwaɗe bakina tana faɗin "maras kunya" tawuce cikin gida anan tasamu Mummy, Mummy ta shaida mata zancen Baba. Mama tace ban faɗa mataba ta sanarwa Anty suka shiga. Bayan Mama tafita Maryam ta dubeni.
"Kekam dai marmeeyy anyi banza wallh baka tauna magana idan zaki faɗeta jikifa abunda kika faɗawa Mama" na harareta ke ai kina tauna magana idan zaki faɗa tunda yanzu naji kina cewa Idan akayi cin-cin na aurenki zaki biyani wanda kikaci kokin manta cewa mama surukarkice saiki yita sakin baki ko tana wajan baki damu ba" "Kedai Marmeeyy bakida hankali wallhy amma kici gaba naga kafin nasan Yaya Habibun Mama nafara sani kedai ki gyara halinki in sha Allah ni zan sharewa Mama hawaye tunda ke baki tunani baka binta sau da ƙafa" na harareta "Sai ki share ai nima batace miki ina sakata Kuka ba ta'iya yiwuwa idan kece Hala mamanma tasake dake amma ni? Ko nice ƴar farinta iya kaci sai ta dinga shareni tana basarwa shiyasa na tarkata wajan Mummy nima" "Barka" Mukaci gaba da Hirarmu ƙawayena sunamin kallo kamar wata waliyyiya gani suke kaff cikinsu nafi kowa sa'a kuma a zahirin gaskiya hakanne. Muna zaune su Mama suka shigo harda Mummy. Mama ta dubeni Kijeki zai tafi Na miƙe ina shirin fita fadeelah ƙawarmu tace, "Marmeeyy rowarshi ake haka da baza'ace muzo mu gaisa ba?" na taɓe baki "Akanme zanyi rowarsa? Ashi ba irin mijinda sai mace tayi rowarsa bane shida kansa ke rowar kansa" "Uhmm Uhmm fa Marmeeyy ba'a shaidar maza wallh a idonki zai iya nuna Miki a duniya dagake babu kowa kuma ba hakan bane" "Au waike wannan shaidar da akayiwa maza ta zauna a ƙwaƙwalwar kanki kenan? Nikam zanyi shaidarsa kuma na yarda dashi sai kije can ke karkiyi naki idan kinyi auren, kuma ni mijina a duniya a nunawa dagani babu kowa ba a idona ya nunamim a duniya dagani babu kowa ba idan zakuje ku tashi please muna ɓata masa lokaci" "waike Marmeeyy mutumin da kikayi watanni jall dashi kikewa wannan shaidar?" "Ko kwana ɗaya mukayi ba watanni ba nayi masa" Maryam ta amshe "Faɗa musu dai wallh koni zanyi shaidar Yaya habib ɗari bisa ɗari" Dariya nasaka araina ina faɗin "lallai maryam baki kama dahir ba Yaya habibun? Wanda naga wani shaƙuwae da sukayi da Nawrah nidai nayi nauyin bakine amma nasan akwai wata aƙasa" mama da Mummy tsayawa kawai sukayi suna kallonmu baki sake suna kallon yaranda suka haifa a cikinsu suna zarar zancen da su kansu sai sunji nauyin sakewa a bakinsu. "Yau naga yara Marmeeyy zaki wucene kokuwa?" bansake magana ba na wuce abuna suna biye dani da Sallama nashiga yana zaune shi kaɗai yana kallonsa ya sakarmun murmushi nima na maida masa na ƙaraso na zauna daff dashi.
"Masoyi wai zaka tafi yanzu? I thougt sai zuwa dare jirginka zak tashi" "Yes zan tafi na yanke shawara idan na zauna ananma I'll just be missinh you bazan iya komai ba sai dai idan zaki biyoni mutafi idan zan tafi saiki dawo" ban kaiga bashi amsaba suka shugo ciki suka gaisheshi ya amsa idonsa yan kaina yana jiran amsata dama yasan bazan bishi ba" intafi?" na girgiza kai "Toh zamu tafi?" nanma na girgiza kai , yayi murmushi ya shafo kaina. Kiyi zamanki amma zanyi kewarki nayi murmushi inajin nima kaina zanyi kewar tasa. miƙewa yayi na rakashi har bakin mota ya rage tsayinsa ya sumbaci lips ɗina kawai naji hawaye yana gangara akan fuskata kamar wanda zamuyi shekara bamu haɗuba Jikinshi shima yayi sanyi ganin yanda nayi laƙwai ina son yin kuka ya jawoni jikinsa yafara shafa bayana bai iya furta kosa kalma ɗaya ba sannan daga bisani ya sakeni saida yaga nashiga gida sannan yatafi. Bayan nakoma saida naɗauki tsawon lokaci ban dawo dai-dai ba daga bisani na ware akaci gaba da hidimar biki. Tun amota muke waya dashi har zuwa da jirginsu zai tashi, bayan ya sauƙa ma haka Video call muka dingayi kusan ranar raba dare mukayi muna waya saida bacci ya ɗaukeni kafin ya kashe."
Bayan 2days ta tafiyarsa naje na zana Exam ɗina kai tsaye daga school ɗin gidansu Maryam na wuce tunda nazo dama inbanda gidan Hajiya sai gidan Baba Alhaji Habibu naje."
PAID BOOK
Littafin BIBIYATA YAKEYI (WAYE SHI) na kudine ki biya Naira Dari uku 300 Domin kisha karatunki hankaki kwance,
account 0003075326
Zainab m Bawa JAIZ BANK Ko katin MTN ta wannna lambar 08161146563 shaidar biya Ta 08161146563 da zarar kin biya Hankli kwance zaki samu damar karanta wannan labarin ku shigo daga ciki kar ayi babu ku domin wannan
tafiyace wanda salonta da tsarinta ya bambamta da ko wace irin tafiya karki bari ayi babu ke."
Idan Kuma kina bukatar Aringa tura miki pc kullum Dari hudu 400 kacal zaki biya batareda an Sanyaki cikin group ba zaizo ya sameki har yanda kike."
ZAYNAB ALABURA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun banking Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya.
Cike da gajiya da takecin jikina na shiga ciki inajin wayata tana ruri dake ina cikin yanayi na gajiya da jin yunwa yasa bazan iya amsawa ba bakina ɗauke da Sallama nashiga ciki a plaour na samu Ummi da Aysha suna suna zaune Aysha har tayi kumari akan lokacin tafiyata. Ummi ta washe baki tana faɗin.
"A'a Marmeeyy Ashe kina tafe?" na zauna kusada Aysha ina maida numfashi "Wallh Ummi tun jiya nakeso nazo nace barina bari idan naje exam sai nabiyo" Ummi fuskarta da fara'a sosai.
"Shiyasa naga mutuniyarki yau bata fita wajanki ba ashe kina hanya ne". "Munyi waya da ita na sanar mata ai tun sassafe" Ummi tana kallo na cikeda sha'awa She can't help it haka kawai Allah yasaka mata son Marmeeyy taso marmeeyy tazaka surukarta sai dai Allah baiyiba yanzu data zauna da Aysha itama har sunyi sabo ta fahimci itama batada matsala. "Ina wuni Ummi?" "Lafiya ƙalau Marmeeyy Ya hanya da mijinki?" cikeda kunya na ams ada faɗin "yana Lafiya" najuya ga Aysha "Matar Hamma Ina wuni" ta kalleni kerere "Marmeeyy banason rashin mutumci menene kuma wani matar Hamma bakisan sunana bane?" "Au sorry wai naga bai dace bakira sunan kai tsaye bane shine na miki inkiya Aysha ina wuni?" Ummi ta buɗe baki "Kai marmeeyy babu dama ayi hakuri ace mata Anty mana" saida na yatsina fuska "Ummi tsakanina da itafa Babu wani nisa shiyasa wai nabata karramawar matar Hamma" rangwashi Aysha ta sakemin akayi saida nayi ƙara afili nace. "Wallh Allah ya isa kuma bazan yafe ba haka kawai kinga jiki duk madara kikai Hannu ki wani zubamin duka" Ummi tace. "Toh kowa yayi haƙuri dama tsakanin mabiyi da mabiyi sai haƙuri" Aysha tayi ƙwafa "Ummi nifa ba ita take binaba Habib yake bina zallan rashin kunya ke damunta" maryam dake shigowa a lokacin tace.
"Yaya naji kuna ambatar Habibu? Ni banason rashin kunya" naja tsaki na kalli Ummi, "Ummi Yunwa nakeji" "Toh marmeeyy na ga alamun kin gajima shiga ciki ki huta za'a kawo miki abincin" na miƙe na zan shige tace. "Au na mantama Marmeeyy naga Aika Allah yasaka da alkhairi" nayi murmushi kawai na shige wajan maryam, miƙewa Maryam tayi tabi Bayana Ummi tadubi Aysha"Kema kibisu koh" Aysha ta miƙe ina zuwa na zube akan gadon Maryam "Wash Allah wallh nagaji" Maraym tashugo "Yaya Exam ɗin dai Babe?" "Alhamdulillhi Exam in sha Allah tatafi kenan" "Ai dolenta tafafi Babe kin manta yanzu ke wacece matar Hammood cefa ni nayi mamakin ma da baki yawa da Bodyguard" nayi murmushi gashican a waje shiba Bodyguard ba shiba Driver ba yabarshi wai duk yanda zanje muje tare, ina exam yana tsaye akaina kamar wani saƙago" Dariya maryam ta fashe dashi,"Babe bakida daɗi amma yaya zamanki acan? Hope komai yana tafiya normal" "Eh amma kinsan kwanakin nan wani abu yafaru Har nayi miscarriage ban sanarwa kowa bane saboda bansan Hankalinku yatashi" Shigowar Aysha ya hanamu hirar da muke shirin yi, Tashigo ta zauna na dubeta."Matar Hamma ashe kina wajan Ummi" ta ɓata rai "kefa bakida daɗi ba yanzu nagama cemiki kidaina cemin Matar Hamma ba?" Nayi murmushi, "Na rantse da Allah bazan daina ba ƙarya keba matar Hamman bace? Ni kicemin matar Hammood kigani idan banyi miki kyauta ba, kowa yan..., shigowar Mummy ya sanyani yin shiru na miƙe dasauri na amshi plate A hannunta adaidai lokacin kira yashugo wayata na ajiye plate ɗin gefe dani ina mata sannu sannan nabuɗe buɗe gamida zaunawa ina amsa kiran na saitata akan table tayi facing ɗina.
"كيف كان امتحانك" (How was your exam)
"Alhamdulillhi"
"Rouhi please kidawo tunda kingama exam kinji? I missed you gidan kaman Babu kowa haka nakejinsa" na haɗe girar sama da ƙasa.
"Masoyi kwana goman saika rage wasu aciki? Ni gaskiya bazan dawo ba sai lokacin daka ɗaukamin ahakanma ina roƙonka ka ƙaramin zakace wani nadawo lallaima" duk maganar danayi da hausa nayita cikin sigar shagwaɓa.
"Rouhi nifa banji abunda kikace ba amma nasan kina nufin bazaki dawo ba Koh? Shikenan duk ranarda kika dawo zanyi tafiya nabarki ke kaɗai kiji yanda nakeji" na ɓata rai.
"Wane mutum Masoyi ai bazan yardaba" yayi dariya "Toh zamu gani ai" muna hira harna cinye abincin kafin mukayi sallama da zummar da dare zamuyi waya. Najuya wajansu mukaci gaba da hira, har Aysha ma hira muka ske munayi sosai sai dai magana ɗaya biyi sai anyi faɗa, sallama Hamma yayi yashigo ciki bai zauna ba ya dubi Aysha.
"Yaya jikin naki?" "Dasauki sosai" "Allah yabaki lafiya" ta amsa da Amin, Cikin yanayin walwala na gaisheshi ya amsa cikeda kulawa.
"Marmeeyy Yagd ya kwana biyu?" "Alhamdulillahi komai lafiya" sannan yajuya ga Aysha "Kince zakije wajan biki koh?" Ta gyaɗa masa kai "Toh kunyi maganar da Ummi?" "Eh tarema da ita zamu tafi event ɗin yau" "Toh ko zaki zauna acan kawai saboda zirga-zirga idan angama bikin saiki dawo?" Yafaɗa yana shafa zajen fuskarsa haɗeda yi mata wani mayen kallo, daga kallo akwai abunda yake nufi da zuwanta gidannan" ita kuwa da batasan akwai wata a ƙasa ba ta washe baki. "Hakan yayi Hamma nima nayi tunanin hakan amma da bakayi magana ba shiyasa banyiba" "Shikenan kije ɗin kawai saiki sanar da Ummi" tayi godiya ya ciro kyɗi yabata ko akwai abunda zata buƙata sannan yafice.
Bayan azahar muka shirya muka fice, Ummi sai daga baya zatazo dagani sai Aysha sai Maryam. Gabaki ɗayanmu anko muka saka nima ina zuwa dama aka saya duka aka ɗinkamin. Sai dai nayafa ƙaton gyale saboda nasan halin Hammood."
Cikin 3days akayi biki gabaki ɗaya aka gama aka kai amarya ɗakinta duk kayan dana saka a biki saina ɗauki pictures masu yawa na turawa Hammood, wani lokacinma jaa gefe nake daga wajan bikin nayita waya dashi." Bayan biki da ƙwana ɗaya Hamma yazo ɗaukan Aysha amma maimakob ya maida ita gidan Ummi sai yawuce can gidansu da ita. Aysha har kuka saida tayi yace bazai maidata ba.
Nima cikin kwanakin nagama shirin tafiya saboda Hammood ya matsa kusan kullum sai yayi magana aranar dana cika 10days kuwa yace aranar zan koma akwai abunda ya tsareshi amma zan tafi aranar" daƙyar na roƙeshi ya ƙaramin 4days Zan cika 2weeks kenan ganin ta iya yiwuwa yasamu time yazo ɗaukana a lokacin yasa yayi haƙuri yabarni. ana gobe zai iso.na shirya zuwa gidan Anty fadeelah Maryam ta rakani mukaje tun 12am sai wajan la'asar Mukabar gidan zuwa gidan Aysha.
akwance muka sameta itaba zazzaɓiba amma wai batajin daɗi anan mukayi la'asar Maryam tashiga kitchen tayi mana girki Hamma daya shigo ya samemu sake fita ma yayi. Asyah taci abinci firr taƙi wai bazataci ba na dubeta.
"Wai ke Aysha meyake damunki ne? Kince babu yanda yake miki ciwo amma bazakici abinci ba"
"Kamar zatayi kuka tace wallh ni Marmeeyy aurenne yafita akaina zan koma gida kawai abu yaƙici yaƙi ƙarewa kullum aiki guda ɗaya" nagane abunda take nufi sai tabani tausayi cikin sigar lallashi nafara bata shawara.
"Kiyi haƙuri amma ni inaga kamar harda tsanar abun da kika sakawa ranki kinƙi sake jikinki kullhm ciki tsoeo kike inaga wannan kaɗai zai sanya miki tsanar abun amma da zaki gwada daurewa kizama jaruma kuma kema kina bada gudumawarki zaki samu sauƙi sosai" hawayen kan fuskarta suka ƙarasa gangarowa, "Ke dai kawai Marmeeyy saboda naki mijin bahaka yake ba shiyasa kike maganar dauriya amma ina wani dauriya da zanyi fisabilillhahi?" cikin tausayawa nace toh mai zai hana ya yana yawan shan lemon ko lime ku ajiye drinks ɗinsu sa'i-sa'i zakiga yarage" abubuwan da Hammood yake sha a duk lokacin danaƙi bashi haɗin kai na faɗa mata shima yana rage zafi dasu da wasu ƴan dabarun da baza'a rasa ba. "Marmeeyy kina ganin isan nayi hakan ba wata jarabar zan ɗebowa kainaba", "Babu wata jaraba ki gwada ki gani" abubuwan danace mata yasha tun kafin mutafi ta kirashi ya sayo Maryam ita muna maganar ma jaa gefe tayi tana waya da Yaya habibu."
A daren ranar Hammood ya iso ƙwana 1kawai muka ƙara muka kama Hanya naci kuka kamar raina zai fita. Ba abu dhabi muka wuce ba kai tsaye kuwait muka sauƙa."
PAID BOOK
Littafin BIBIYATA YAKEYI (WAYE SHI) na kudine ki biya Naira Dari uku 300 Domin kisha karatunki hankaki kwance,
account 0003075326
Zainab m Bawa JAIZ BANK Ko katin MTN ta wannna lambar 08161146563 shaidar biya Ta 08161146563 da zarar kin biya Hankli kwance zaki samu damar karanta wannan labarin ku shigo daga ciki kar ayi babu ku domin wannan
tafiyace wanda salonta da tsarinta ya bambamta da ko wace irin tafiya karki bari ayi babu ke."
Idan Kuma kina bukatar Aringa tura miki pc kullum Dari hudu 400 kacal zaki biya batareda an Sanyaki cikin group ba zaizo ya sameki har yanda kike."
ZAYNAB ALABURA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun banking Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya.
Isar cikin dare mukayi amma duk da haka munsamu tarɓa sosai sai dai Hammood bai yarda mun gana da mutannen cikin gidanba yace sai zuwa safiya, duk da kasancewar gidan kamar safiya haka yake ko'ina tarr hasken fitulu ga sojoji sunata shawagi ko'ina tareda ɗai-ɗai kun mutannen gidan ina kallon gidan ina sauƙe ajiyar zuciya ina ganin gidan Hammood wata duniya amma ga duniya guda
anan ina tunani koshi kansa mai gidan baisan yawan al'umma da suke rayuwa a cikin gidanba, Kai tsaye Masauƙinmu muka nufa kamar yanda ya buƙata dake akwai gajiya a jikina muna isa na cire kayan jikina na shiga wanka ina fitowa nabi gado na ƙwanta. Kafin Hammood yayi nasa wankan ni har bacci ya ɗaukeni. Ya zauna gefen gadon da murmushi ɗauke a kyakkyawar fuskarsa ya dafa jikina yana kallona, a hankali ya motsa lips ɗinsa yafara magana.
"Rouhii هل أنت نائم?" (Are you sleeping?)" cikin bacci naji muryarsa yana magana a hankali na motsa batareda na farka ba nayi sounding "Uhmmm" "Rouhi tashi kiji wani abu" cikin baccin na maƙe kafaɗa saboda baccin baiyi nisa sosai ba, "Rouhi please mana wai haka