Waye Shi Complete Hausa Novel

Author :  Billyn Abdul Category :  Romance

Chapter   37 / 58

108K to 111K   out of 171.2K words

relieve"

"Go home and get some rest we'll meet tomorrow"

"No I've been resting tun safiya now is your time sai dai if you want me to go and then saina tafi" Dasauri na girgiza kai.

"Bakiso natafi? Na jijjiga kai yayi murmushi.

"Okay I'll stay"

Muna zaune a wajan Har dare yafara yi sannan nace Mishi zai gaisa da sisters ɗina nafita na kirasu Anty fadeelah da Maryam. Suma sunyi kurnar ganinsa mun daɗe sosai suna hira dashi har selfie suka ɗauka sannan suka suka fita. Suna fita raudha tasake dawowa still tasake taɓashi raina yayi matuƙar ɓaci dole na tsayar mata idan yatafi.


Bayan fitarsu bamu daɗe muna hira ba shima ya shirya tafiya saboda dare yayi.

Nafita cikin gida haɗa masa tea ɗin da na zuba a flask dan naga yaji daɗinsa tun bai jima da shaba naga fuskarsa da hancinsa sun fara canja kala zuwa normal.
nasamu Mama hartayi ta juye tea ɗin ginger and cloves. Da na'a-na'a da sauran tea spices masu amfani. Ina shiga palourn ya miƙe ta Babban ƙofar palourn yanda muke shigowa yafita nabishi a hankali muke hira har muka kusan zuwa wajan motocinsa kafin mu ƙarasa anbuɗe masa ƙofa ya ja yatsaya yana kallona. Alokacin Yaya habibu da suke hira da maryam yataso yazo suka gaisa sannan yakoma wajan maryam. Hammood ya juyo da hankalinsa kaina.

"I'll miss you" yafaɗa na sunkuyarda kaina ina murmushi. Sannan na miƙa masa ɗan madaidaicin silver flask dake hannuna yasa hannu ya karɓa yana kallona.

"It's ginger and cloves tea drink it when you get home zai sauƙar maka da cold ɗin in sha Allah"

"شكران "
(Thank you) I love you nasake murmushi ya sanya hannunsa yakoma nawa yana murzawa a hankali sannan ya matso yayimin peck a goshi. Batareda ya damu da mutannen da suke wajan ba bayan su Yaya habibu akwai ma'aikatansa masu tsaronsa hardasu P.A.


"مساءل اخير قلبي."
(Goodnight my heart)

"Okay good night" na faɗa sannan yajuya yashiga mota saida naga fitarsu sannan na juya wajan Maryam dana hangesu suna hira da Yaya habibu.

"Babe zo mushiga" nafaɗa danna ƙagu nabata labarin.

"Oh kingama soyewarki ni bazaki barni nayiba?" dan Allah maryam kizo wallh abune mai muhimmanci" na faɗa.

"Tashi kije nasan akwai abunda takeso ta faɗa miki" Yaya habibu yafaɗa danya fahimci abunda nakeson faɗa mata.

Tun kafin mukai cikin gida harna gama zayyana mata komai tayi ihu tafi sau uku kamar wacce tafini murna.

"Babe amma wallh sai nabi na tsayarwa waccar raudan dan bazan ɗauki iskanci ba"

"Muje da gudu babe wallh muci ƙaniyarta" kai tsaye ɗakinda suke muka wuce dan tunda aka gama biki suke zaune a ɗakinmu nada da Baba yace mudawo ɗakin Mama. Anty fadeelah bata ciki muka shiga rai aɓace.

"Wai ke raudan nan bakida hankaline? Bayan kinzo ɗatsu kinyi masa rashin hankali shine bai isheki ba saida kika sake dawowa?" Cikin rashin damuwa da maganganunda na yaɓa mata tace.

"Toh ya zanyi? I really couldn't help it. I jusy wanted to see his face thats all i wanted. Ka wallh nakamu da sonsa kinsan I have such a great taste in men yanzu gobe dole ma nemeshi na bayyana masa abunda yake zuciyata kuma nasan zai soni tunda dole ne naganshi gobe I wanted to see him at any cost"
Naja tsakin baƙin ciki

"Amma kedai bakida hankaki no one in the right mind would do this Tayay kike tunanin zai soki?"

"Ta yanda kike naki tunanin?" tabani amsa. Wacce keson Yaya Habibu sai alokacin tayi magana.

"tried hard not to do it but he kept pupping in my head. Wallh nima sonsa nake raudha babu yanda za'ayi nabarki ki mallakeshi ni kaɗai zaiso kinsam yanda naji a zuciyata dana ganshi?" Do you know how sexy his voice is. It's not too high or too low it sounds so sweet He make my heart flatter.

Ɗaya daga cikinsu wacce ita bata damuba kawai ita dai taga celebrity ta amshe.

"Ohh really ni kawai naga fuskarsa i ddint hear his voice"

"Amma kukam dai anyi jakkai wallhy to mijinta ne an ɗaura musu aure da marmeeyy sai naga ta yanda zai soku ai ce muku akayi kowani tarukuce zaiso?" sun jijjuga da kalmar auren amma basu ƙaryata ba dan sunsan dole akwai wani abun atsakaninmu dahar ya tako zuwa wajena. Ɗayar tace.

"to kunjj ba? Saiku hakura toh ai ganinsa ma ya isa ace a wadatr bazakuyi mafarkin mallakrsa ba Allah na tuba in banfa sanadi yaushe har zamu samu ganinsa kamar yanda muka samu ayau? Amma hakanma baiyi muku ba dayake zuciya akwaita da zari aduk lokacinda tasamu wani abun saita zarcewa wani dafa zance muke akan konawa zamu biya a haɗamu muganshi ko daga nesa zamu biya. Ku kanku kunsan har indai zai taso yazo gareta ya aureta a hakan aiba ƙaramar soyayya bace wallhy ku rufawa kanku asiri da aikin wahala" sannan ta juyo gareni

"By the way How did you guys meet?" na juya da baƙin ciki batareda na amsa question ɗinta ba kodan nima banda amsar ce oho?" har yanzu bansan yaya akayi wannan soyayya ta ƙullu ba. Koni kaina yanzu haka inajin alamun sonsa nakeyi bansan kuma yaushe nafara ko yaushe soyayayr tashiga ba. Ficewa mukayi aɗakin zuwa ɗakin Mama.

"Babe dare yayi gashi yanzu bazai yiwu kifita ba karfa muƙure Ummi kinga tana kawaici baki fito da shirin kwanan gidanna ba haka jiya kika kirata kika kwana gashi yauma baki komaba"

"Ai tunda Mama taga dare Yayi kuma tasan dole saina haɗuda Hammood kafin na tafi saita kira Ummi tayi mata bayani"

"Toh barka"

"Babe bazkai ƙirashi kiji koya isa ƙalau ba?"
"Na kirashi nace masa me toh babe?" haka Maryam tayi amma naƙi kira daga ƙarshe ta haƙura.
Mama tashigo ta samemu tana shirin tafiya ɗakin Baba tace.

"Marmeeyy kin kirashi kinji ya murar tasa kuwa?"

"A'a Mama"

"Toh kikira maza kiji Allah yasa tayi sauƙi na amsa da amin. Maryam tajiya tafara waya Anty fadeelah ma tunda akaji ta ɓata shiru to wayar takeyi.

Wayata na ɗauka na danna lambarsa tana fara ringing akayi picking. Nayi shiru nasaka cewa komai saida yayi magana Sannan nima nafara magana.

"Uhmm dama nakira nace how is your cold"

"i feel better now thanks to you"

"Do you? Thats good to hear"

"Kin damu dani kenan? You sound worried"

"Eh nadamu" nafaɗa da yaran hausa yayi murmushi daga yanda yake dan yasan nafaɗa ne san kar yasan abunda nafaɗa.

Hira kaɗan muka taɓa mukayi sallama dashi.

_______

Chief metron ɗin tadubi Hamma.

"Abubakar har indai bazaka bar yarinyar nan haka ba Allah zan kira Umminku ta ɗauketa kona satine haba she's suffering baka ganine?" sannan tajuya kan Aysha

"Sannu banason na sake riƙeki a asibitk saboda jiki baiyi tsamari ba kuma riƙewar asibiti a irin wanna lamari duk tonan asirinku ne amma inga zan yiwa Umminsu magana ta ɗaukeki kona 2weeks ne a wajanta saiki samu kema ki huta and ki ƙwana biyu bakisha wani maganin gyara namu na mata ba kodaga gida ankawo miki kiyi avoiding ɗinsu dan shima yana cousing irin waɗannan al'amuran" Aysha ta jijjiga kai dasauri tanaso ace tayiwa Ummi magana ko zata samu sauƙi dan Hamma niyyar kasheta yakeyi yaɗaura niyya idan bayaga ta mutuba bazai sauƙe ba.

Hamma jin abunda Cousin sis ɗinsa take faɗi kuma yasan zata aika ya sanya ya.

PAID BOOK

Littafin BIBIYATA YAKEYI (WAYE SHI) na kudine ki biya Naira Dari uku 300 Domin kisha karatunki hankaki kwance,
account 0003075326
Zainab  m Bawa JAIZ BANK Ko katin MTN ta wannna lambar 08161146563 shaidar biya Ta 08161146563 da zarar kin biya Hankli kwance  zaki samu damar karanta wannan labarin ku shigo daga ciki kar ayi babu ku domin wannan
tafiyace wanda salonta da tsarinta ya bambamta da ko wace irin tafiya karki bari ayi babu ke."
Idan Kuma kina bukatar Aringa tura miki pc kullum Dari hudu 400 kacal zaki biya batareda an Sanyaki cikin group ba zaizo ya sameki har yanda kike."


ZAYNAB ALABURA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya


"Kai Haba A'a bama sai anyi hakanba zan barta bazan sake kusantarta ba tayaya za'a ɗauketa kawai da sunan ankaita gidan Ummi dan wannan dalilin? Dawani ido kikeso na kalli Ummin? Kawai abarta anan basai an kaita ni zan barta ta ko Maryam taxo ta zauna damu ko sistanta idan takama nabar gidanne ma saina bar musu gidan du zauna"

"A'a toh Abubakar ba dole ayi hakanba? Aidole ce tasaka na fahimci halinda kake ciki kai kanka amma har indai takama abarta a wajan Ummin haka za'ayi kokuma ka kaita gidansu Amma shawararda ka bada na ƙannenka ko nata su zauna daku hakanma yayi idonsu zaii rage wani abun yanzu dai kuje gida tukunna sai ku yanke shawara idan ƙanwarce idan kuma ƴan uwantanne toh. Amma tasamu hutu kodan gudun samun matsala ma dan ana samun matsala sosai a irin waɗannan lamarin matsala baga lafiyar jikinta ba kai kanka naka lafiyar jikinba sannan zan baku magani tashashi na wani lokaci in sha Allahu babu komai. Godiya sukayi mata suka koma gida. a hanya tunanine fall cike a ransa yarasa yaya zaiyi? Maryam zaice tazo ta zauna da ita? idan Maryam ce da yasan tanajin tsoronsa zai iya korarta ta fita ko taje wani waje zai iya hakura da matarsa kuwa? Toh Kokuma ita ƴar uwarta zatazo? Toh amma ai ita Marmeeyy ce kaɗai ƙanwarta da zata iya zama da ita ɗayar yayarta ce sannan kuma tayaya ma zasu iya zama da Marmeeyy? Ajiyar zuciya kawai yake sauƙewa yana tunanin yanda zai ɗauki lokaci batareda matarsa ba. Ajiyeta kawai yayi ya juya itakuwa tana shiga ta zube taso yashugo suyi magana yaɗauko mata Maryam amma ita a ranta ta yanke gara Marmeeyy tazo idan Marmeeyy tazo gidan ta tabbata duk wani abunda takeji akan Hamma saita cire mata shi. sai dai shi Hamma ne bata tunanin zai yarda Marmeeyy tazo, ita bata tunanin ita kanta marmeeyn zatazo ko bazata zoba. Ajiyar zuciya tasauƙe ta rigada ta yanke shawarar faɗa masa hakan kawai.

Bai dawo gidanba Har tayi Bacci taso yazo suyi magana haka ta haƙura da jiransa tashiga ta ƙwanta shima yana dawowa yashige ɗakinsa dan yaji tsit bai nemeta ba ya ƙwanta washe gari da safe Saida suka gama breakfast ta dubeshi.

"Uhmm Hamma dama gameda maganar jiyanne nace mai zai hana Marmeeyy tazo tazauna damu har in warware?" saida yaji wani iri.

"Marmeeyy kuma meyasa Marmeeyy bayan akwai maryam?"

"Saboda idan tana gidan bazaka iya aikamain komai ba dan nasan har yanzu kana sonta Maryam kuwa ƴar uwaka ce zamanta da babu kusan ɗaya" ya kalleta da Mamaki. Ta jijjga masa kai alamun tabbatarwa.

"Eh ai nasani har yanzu kana sonta Dan haka zamanta shine zaisa ka gujewa wasu abubuwan dan Allah kar kace A'a dan hakan shine maslaha". Shiru yayi baice mata komaiba. Taji haushin hakan kuwa taso ya musa yace A'a banason Marmeeyy a yanzu ke nakeso. tayi zaton auratayya dake shiga tsakaninsu yanzu sun wuce batun soyayya ya mance da Marmeeyy ita kaɗai ce aransa ashe bata saniba da sauranta toh lallai ba Marmeeyy kaɗai ke buƙatar acire Mata Hamma a zuciya ba har shi Hamman yana buƙatar acire masa Marmeeyy a zuciya. Haushi ya hanata cemasa komai harya shirya ya fice.

Sassafe natashi na shirya kayan makaranta muka fice da Maryam zamu bi gidan su ta saka uniform tukunna. yaya Habibu yakaimu bayan gaisawa da mukayi da Ummi Maryam ta shirya taɗauki Bag ɗinta muka wuce school. Gabaki ɗaya zaman school nayishine da tunanin Hammood cike araina inata duba wayata ko zai kira ko message amma babu ko ɗaya. Dake friday ne bamu daɗe a school ɗinba muka dawo gida. Maryam tawuce gidansu Nima nawuce gida. Mama tanata jira taji ko zanyi mata magana amma banyiba haka ta zubamin ido kawai.

ƙarfe biyu Aysha taji Hamma shiru Baizo ba baikuma ko yimata waya yace ya yarda a ɗauko Marmeeyn ba ko maryam ya kawo mata idan bai yarda da Marmeeyn ba dan tasan idan jiya ya iya yimata haƙuri to yau bazaiyiba. Tun kafin dare yayi gara ta sake masa tuni.
Ɗaukan wayarta tayi tashiga contact tayi dialing number ɗinsa bugu biyu ya ɗauka. Bayan tayi sallama ya amsa.

"Hamma najika shiru bakace komai akan ɗaukan Marmeeyyn ba"

"Kishirya zanzo muje gidan sai muyi musu magana" tayi murna sosai dan zata jefi tsuntsu uku da dutse ɗaya nafarko zata sanya Marmeeyy tasan irin muhimmanci da mace take dashi gun mijinta na biyu dole ta nemo hanyar cirewa Hamma shima Marmeeyyn aransa na uku zata samu sauƙi daga jarabar Hamma.

Alokacin tatashi ta shirya cikin doguwar rigar lace ta sanya turare da Humra ta ɗauko jaka da gyale harda takalmi ta kima ɗaurin ƙwali tazauna tana jiransa. Har tagaji ta sunce ɗaurin baizo ba aka kira la'asar tatashi tayi sallah tana zaune taji shugowarsa. Ta turo baki yana ganinta yagane abunda take nufi amma ya share yazo ya zauna ƙamshin turaren da ta sanya yana fisgarsa.

"Hamma amma fa cemin kayi na shirya gaka nan zuwa shine bakazoba sai yanzu?" tafaɗa a shagwaɓe. Ya dubeta da tana shagwaɓar tayi kyau amma sai dai ta nemi data zaune tsaye. Kawarda kansa yayi gefe bayaso daga yau yafara saɓawa maganarsa na cewar zai barta ta huta"

"Eh nace ki shirya amma ai bance miki yanzu zanzo ba. Kitashi ki canja kayan turaren jikinki yayi ƙamshi dayawa yana sauƙarmin da kasala karki saka turare" miƙewa tayi jin abunda yake faɗa da sauri tayi ɗaki saida tayi wanka ta wanke turaren sannan ta canja kayan ta saka sabo dall wanda sam babu ƙamshi a jikinsa saina sabuntar kaya. Ta shirya tafito tsaff da ita a yanda tabarshi ana ta sameshi ta ƙarasa kusa dashi.

"Hamma na fito muje" ya buɗe idanuwansa a kasalance ya dubeta harsun canja kala a hankali ya sanya hannu ya jawota tafaɗo jikinsa. Dasauri tafara ƙoƙarin ƙwacewa zuciyarta na bugu da ƙarfi.

"Menene hakan Hamma? Dan Allah kabari kaga fa banda lafiya" tafaɗa tana fashewa da kuka. Dan tuna irin azabarda takesha idan ya riƙeta.

"Shhhss is okay, ba wani da zafi zanyi miki ba kuma iya na yanzu ne kaɗai ba gashi zanje na ɗauko miki Marmeeyy ba sai kwana biyu kafin tatafi ke bazakiji tausayina ba tsawon lokacin da zan ɗauka batareda keba? Haka ya lallameta da baki da sakar masa jikinda saida ya sanyata danasanin tausaya masa da tayi. Yamma tayi liƙis amma haka ya ɗauketa ya kaita a ƙofar gida ya ajiye ta yace idan zai dawo ɗaukarta zai shiga tafara yimusu maganar amma kafin yazo. ɗaukin zuwa gidane kawai ya sanyata fita amma idanba haka ba babu abunda zaisa tafita a yanda takejin jikinta. Tunda tayi arba da gida taji shawararta ta canja yanzu zama zatayi agida har sai ta warke"

A hankali ta shiga har cikin gida tana zuwa tawuce ɗakin Mama kai tsaye ana shirin yin magrib Mama taji shigowar Aysha.

"A'a wa nake gani kamar Aysha? Ke waya faɗa miki ana fita aure sati guda? Matsashi kikayi kenan ya kawoki?" Aysha taturo baki.

"Mama ai dai zaki bari na zauna kafin kifara min faɗa natafi gida kwana 6 bananan amma bakuyi kewata ba ina zuwa za'a faramin faɗa" tafaɗa tana tura baki.

"Toh ai abunne aysha baiyi tsari ba sati ɗaya fa? Aidan kinsan Babanku bamai faɗa bane ba da sai yayi miki faɗa amma koshi yaji bazaiji daɗi ba"

"Nifa Mama banda lafiyane nazo gida"

"Subhanallahi toh Allah ya sauwake" Mama taja baki tayi shiru dan batason ƙarin wani zancen da za'a sakata jin kunya. Ta gaisheda Mama. mama ta amsa tana tambayar jiki tace.

"Dasauki Mama amma wallh ni kinganni yanzu nadawo gida kenan saina warke na koma"



"Zanga yanda za'ayi haka ta yiwu"

"Allah mama dagaske nake" toh kawai Mama tace ganin zancen bana masu hankali bane. Nikuwa bansan da zuwanta ba ina wajan Mummy muda Anty fadeelah acan mukayi sallah. Itama Aysha a ɗakin Mama tayi sallah saida Mama taga batada niyyar fita sannan tace.

"Aysha tashi kije ki gaida mutanen Sauran mutanne gidan"

"Nasan yanzu Baba bai dawo ba sai yayi isha'i Anty ce idan nafita gaida Baba saimu gaisa wallh banjin daɗine banso nayi tafiya biyu"

"Allah yasauwake amma ai Mummynku ma tananan sai kije ki gaisheta itama"

"Dama Mummy tana gari? Rabona da waya da ita tun washe garin ranarda aka ƙwantarda ni a asibiti ni naɗaukama tatafi dannasan bata wasa da business ɗinta dan yafi mata komai." Dan ƙwalo Mama tayi mata.

" ungo naki Mummyn naku kike faɗawa Haka? Toh ki tashi kije wajanta kuma Mummynku ta dawo nan da zama kenan" Zaro ido tayi da Mamaki abunda bata taɓa zato ba tayi murna sosai harta manta dawani rashin lafiya kai tsaye tatashi tayi ɗakin Mummy. Sallama kawai tayi tafaɗa ciki. Bulum kawai mukaji shigowarta kamar wata wlkiya.

"Mummy wai dagaske kin dawo kenan? Bazaki koma abuja ba?

"Waya faɗa miki haka?"

"Mama ce ta faɗamin"

"Mamarku ta faɗa miki bayan kinji bakinta shine kuma kike sake tambaya ta?"

"Uhmm mummy abunne wallh yabani Mamaki bantaɓa zaton zaki dawo nan ba naɗauka kin zauna a abuja kenan"

"Mamaki ma yabaki bakiji daɗi ba kenan? Tukunna ma waye ya kawoki? Waya ce miki ana zuwa gida daga aure biki ko sati baiyiba? Tsabar rashin hankali ki kamo hanya ki taho gida?" bata kaiga cewa akomai ba Yaya Ahmad yayi sallama. Muka amsa Mummy tabashi izinin shugowa. Da mamaki yake kallon Aysha.

"Kekuma me kikeyi a gida?"

"Banda lafiya nefa shine ya kawoni gida" tafaɗa tana tura baki.

"Allah ya kyauta" kawai mummy tace. Muka gaisarda Yaya Ahmad ya amsa sannan ya zauna.

"Mummy yaushe zaki tafi ne?" da mamaki na kalli Mummy ina mamakin ashe bata gayawa Ya Ahmad tadawo kenan ba.

"Ahmad korata ma kakeyi? Cikinku Marmeeyy ce kawai ta roƙi nazauna karna tafi. Fadeela kanma bansan stand ɗinta ba san bata taɓa cemin komai ba ga Aysha wai Mamaki takeyi Akan taji nazo kenan bazan tafi ba"

"Wai dagaske Mummy bazaki koma ba?"

"A'a ƙarya" tafaɗa a daƙile yaya Ahmad na ganin haka ya kama kansa dan yasan ba komai Mummy take ɗaukana ysnxu cemata zallan wai dagaske da yayi saita ɗauki hakan raini"

"Toh hakan yayi kyau Mummy Allah ya kaɗe fitina ya zaunar daku

37 / 58