Waye Shi Complete Hausa Novel

Author :  Billyn Abdul Category :  Romance

Chapter   26 / 58

75K to 78K   out of 171.2K words

Ya amsa sallamar na isa na ajiye akan center table na zuba acikin kananun cup sannan na nemi waje na zauna ina jira yadan huce na mika masa. Na zauna gefe ina fadin.

"Barka da hutawa Baba" ya amsa.

"Sannu Marmeeyy yaya gajiyar hanya?"

"Lafiya" kawai nace.

"Kunbar su mummyn naku lafiya?"

"Lpy kalau tama bada sako a baka yana wajan Mama"

"Toh madallah nagode" yafada sannan mukayi shru kamar wanda yake jira nafada masa wata aikar bayan wannann yaji shiru. Yayi yar gyaran murya.

"Marmeeyy bakuyi magana da Mummyki akan zancen dawowarta ba? Ko akwai abunda tace?"

"Batace komaiba Baba amma mai zai hana kairata ka tambayeta? May be jira takeyi ka tambaya shiyasa batace komaiba" jijjga kai kawai yayi yana mamakin halin marmeeyy da batajin kuiwar fadar magana koda tafi karfin shekarunta. Idan aka sanya maganganunta da shekarunta a mizani magnganun zasu rinjayi shekarun, bbu wanda zai yarda karamar yarinyace mai zaro maganganu haka. kuma gashi ta iya fahimtar mutannenda take tare dasu.

"Baba kaga wayarda Yaya Ahmad ya siyamin" na fada ina mika masa wayar. Ya rigada yasan zancen wayar Ya Ahmad ya gaya masa ammma saiya nuna baisani ba.

"Madallah Ahmad yayi kokari Allah yabiyashi"

"Amin Baba amma baka ganin wayar tayi tsada da yawa" ya jijjiga kai.

"Batayiba Allah yasaka masa da alkhairi" na amsa da amin sannann na tuna maganar wannan mutumin inaji kamar intambayi Baba ko yasanshi.
Nadade ina tunani Baba yana kallona kawai yasan akwai abunda nake nazari akai"

"Wani abunne Marmeeyy?"

"Uhmm dama Baba inaso na tambayeka akwai wani lokaci daka tabayin bakin kamar watannin baya wanda harn kasaka mukayi musu aiki. Daga ina suke Baba?" Yana kare min kallo yanason gano wani abun yabani amsa.

"Wani senate ne da mukyi school tare ya rako wani nrman alfarma wajena da izinin governor wani abunne?" Na zaro ido hadeda jijjiga kai.

"Babu komai kawai ma tambaya ne naga baka taba hirar ba. Lallai wannan Babbar alfrmace Baba governor fa kace kuma kayi musu?"

"Eh sosai Babba ce danshima da kansa ya kirani kuma yazo (governor). nayi musu alfarmar sboda naga dacewar hakn"

"Allah yataimaka"

"Amin" alokacin tunani yashiga raina abunda nake zato ashe n haka bane" Amma wace irin alfrma ce har governor zaizo dakansa?


Nayi masa sallma nafita dan nasan Hamma na jirana washe gari tashin sassafe zaiyi."


ZAINAB ALABURA
Wannan Littafin na kudine kibiya 300Naira ta asuusn bankina domin samun damar yin karatu cikin kwanciyar hankali. 0003075326 JAIZ BANK ZAINAB M BAWA


Bayan isata daki na iske Missed call dinsa guda biyu ban bata lokaci ba wajan maida masa da kira saida ta kuwa katsewa yadaga. Nayi sallama ya amsa sannan na daura da fadin.

"Sorry Hamma ina wajan Babane kakira bana kusa"

"Babu komai nima yanzu ina duba kayayyakin da zanyi tafiya dasu ne" mukaci gba da waya sai wajan 12:00am mukayi sallama washe gari sassafe ya dauki hanyar Abuja yana isa ya kirani kwanansa biyu acan yana jiran su ummi bayan saukowarsu ko kwana daya basu karaba suka kamo hanya cikin dare suka iso.

Washe gari sassafe Maryam ta shirya Babu yanda batayiba na shirya mutafi tare naki. Tun lokacin da wannan abun yafaru nayiwa kaina alkawarin bazan sake zuwa gidanba. Data matsa sai nace mata ni narigada nayi alkawari bazan sake zuwa gidanba sai amatsayin matar Hamma. Batayi fushi ba kamar yanda nayi tsammanin zatay ba itakuwa a wajanta dake zuwanmu wancan lokacin taso ta zargi wani abun yasa bata tsaurara akan sainaje ba. Baba shi da yaso yabari su Ummi suzo dakansu kamar yanda suka kawota kar suga kamar saurin maido musu da ita suke. Amma ganin yanda maryam ke daukin zuwa ganin iyayen nata yasa yace Mama tashirya ta kaita Mama ta shirya bayan ta shiryawa su Ummi abun trba wnda zata kai musu. Da Maryam zata tafi 2k Baba yabata yace su hau adaidaita.

Bada kayanta suka tafiba saboda adaidaita zasu hau shiyasa tace daga baya zatazo tadauka. Warmers dinda Mama ta shirya musu abinci kawai suk dauk sai jakar Hannu.

Sun samu Ummi na baccin gajiya sai bayan zuwansu tatashi. Kai tsaye maryam tawuce dakinta da murna ta tasota. Itama Ummi tayi murnar ganin yartata gashi tayi kyau ta sake murjewa da alamu tasamu kula mai kyau. Ummi ta karaso ta zauna damurnarta tana fadin.

"Ashe kuna tafe? datsu nagama fadin idanna gama baccin gajiya zanzo na tafi wajannaku"

"Ayya da gajikam sosai mu Yakamata muzo muyi muku bangajiya ai kinga Maryam ma ta kagu taga Umminta"

"Ita ta tasoku kenan ja'ira, mungde sosai mamansu Marmeeyy da Maryam Allah yasaka da alkhairi yaba zumunci zamuzo har gida nida abbansu muyi godiya"

"Ah haba babu komai yaro aina kowa ne" Ummi ta danyi waige-waige sannan ta juya ta dubi Maryma tace ina marmeeyy? Bata kaiga bata amsa ba Hamma yashigo parlourn da Sallama. Maryam bata damu da shigowar Hamma ba tafara fadin.

"Ummi ai yanzu wasan buya zakunayi da Marmeeyy Saboda suna soyayya da Hamma" saida Hamma yayi turus yakasa karasowa ciki Maryam tacigaba da magana.

"Babu yanda banyi da itaba wallh Ummi taki zuwa kunyarki takeji" daga Mama har Ummi baki bude suke kallon Maryam Hamma najin haka duk gwarin guiwarsa saida yaii kunya dasauri yajuya zai fita Ummi ta Kirashi yadawo sai sunna kai yakeyi.

"Gaskiya ne abunda Maryam take fada?" Ya sauke ajiyar zuciya.

"Eh Ummi dam ko Maryam bata fada ba kuna dawowa nayi niyyar samunku da Maganar"

"Toh madallah Alhamdulillhi abu yayi kyau dama abbanku ya fahimci wani abun tun ranarda zamu tafi ya fadamin inata addu'a Allah yasa zarginsa yazamo gaskiya nayi murna sosai Allah ya tabbatar muku da alkhairi. Kaji tsoron Allah ka rikemin diyata tsakani da Allah wallh nayi farin ciki nadade ina maka sha'awar auren Marmeeyy yarinyace mai hankali amma fahimtar hankalinku kamar baya kan juna yasa ban daga zancenba Allah yamuku albarka. Kansa akasa ya amsa da Amin cikin jin dadi.

"Bakice komai ba" Ummi tafada tana kallon Mama. Mama wacce ke murmushi tun lokacin da aka fara magana tasake fadada murmushin.

"Ai kince komai Ummi Allah ya tabbatar da Alkhairi yasa muna cikin rayayyu za'ayi" su duka suka amsa da Amin. Hamma ya saci kallon mama dukda wancan ranar bai daga ido ya kalleta yanda zai ganeta ba amma kamanninta daya kalla yau ya tabbatar masa da cewa itace mahaifiyar Marmeeyy duk da a haka baza'a taba zaton ta ajiye yarinya kamar Marmeeyy ba balle Yaya Habibu. Kamanni suke sosai da Marmeeyy kamar an tsaga kara. Yayi saurin mikewa ya fice dan baisan tana wajanba."

Mama tabawa Ummi warmers dinda tazo dasu Ummi nata godiya sannan tayi mata Sallama tafita.

Adaki tasameni nayi mata sannu da dawowa ta amsa sannan ta zauna fuskarta babu dadi.

"Marmeeyy zo zauna magana zamuyi" nazauna ganin babu fara'a afuskarta yasa nasha jinin jikina.

"Ashe akwai abunda Zaki boyemin matsayina na mahaifiyar ki Marmeeyy? Nadauka kowani hali kike ciki ni zaki fara sanarwa" kaina yadaure sosai narasa yanda maganar Mama ta dosa. Nayi tunani dayawa abubuwa dayawa sunzo raina amma banda zancena da Hamma.

"Ashe soyayya kuke da yayan Maryam ni uwarki sai dai naji agari? Haka kikag ya dace?" Na dukarda kaina kasa.

" Dan Allah Mama kiyi hakuri wallh bawai naki fada miki bane da wata namufa kawai banason asanine saboda kar manya su shiga zancen"

"Bakya son manya su shiga bakya sonsa ne?" Na girgiza kai da sauri.

"Kina sonsa kenan?" Nayi shiru ban bata amsaba tafahimci abunda nake nufi dan haka ta canja tambayar.

"Bangane abunda kikac bafa Marmeeyy mr kike nufi da bakyaso manya su shiga zancen?"

"Naga Baba baida kudi kar suzo suce zasu turo n sanyashi a wahala shiyasa"

"Wannan ba dalili bane da zakiki sanar dani wannan zancen. Nadauka kinada wayo da idan lamari irin haka tataso ni zaki fara tunkara ashe babu. Yanzu haka kin sakani a kokonto bansan abubuwa nawa kike boyemin ba ta iya yiwuwa akwai wani abun. Idan akwai gra ki sanar dani tun yanzu idanna sani daga baya abun bazaiyi mana kyau ba. akwai wani abun?" Nayi kasa da kaina ina wasa da yatsuna.

"Menenne ina jinki"

"Zan fada miki amma Mama dan Allah kimin alkawari bazakiyi fushi ba" saida ta karemin kallo sosai.

"Nayi ima jinki"

"Shekara biyu baya harda watanni akwai wata number da take damuna da message ko ankira bata shiga kuma ko nayi blocking zatayi unblock da kanta message yashigo. Sannan duk wani abunda layina yake ciki Whatsapp ko kira ko Instagram wannan lamba tanada masaniya akai. Ko pics na daura a Instagram saukesu akeyi ayi delete a page dina gabaki daya harna hakura na daina. Duk wani labarin daya kamata nabata gameda numbern saida na bta har zuwa da akyi ofishin layi suka kulle." Tsoro karara nagani a fuskar mama abunda banaso kenan yasa tun baya ban gaya mata ba.


"Mama dan Allah kiyi hakuri wallh ban fada muku bane saboda banaso na daga muku hankali" shafo fuskata tayi cikeda tausyawa.

"Marmeeyy duk ke kadai kika shanye wannan abun?daga yau karki sake haka duk wani halinda kike ciki ki fadawa mamanki. Kikace kina zargin ba Bahaushe bane?" Na jijjiga kai.

"Ciro zoben ki bani babu musu na cire ma mika mata. Zanyi magana da Babanku amma sai bayan iyayen su Hamma sunzo dan yanda mukayi magana da ita tacemin cikin wanan satin kafinnan banaso adago komai har bayan sunzo anyi magana. Hamma ya kwantamin arai sosai kuma naji dadi daya kasance shine wanda kik zab daga yanyinsa yanada nutsuwa sosai Allah ya sanya alkhairi a lamarin. Na sunkuita kaina kasa ina murmushin jin dadi.


"Sannan zanbawa Habibu zoben nan yaje yaji kudinsa dan tun lokacin dana gani jikina yabani ba karamin zobe bane sai dai sanin babu yanda zaki samu diamond ring yasa nayi tunanin imitation ne kawai kika saya" tana gama magana ta ta dauki wayarta ta danna numbern Yaya Habibu minti biyar ya shigo ta mika masa zoben tace yaje yaji kudinsa."


Har Bayan magrib Yaya habibu bai dawoba sai can ya dawo a gajiya kai tsaye dakin Mama yashige muna ganin Haka muka bishi.

"Mama a'ina kuka samu zobenann anya bana sata bane?" Zaro ido dukanmu mukayi araina in fadin nashiga uku. Wata zuciyar tana fadin maganina kenan da aka kawomin abu babu bincikr nakama nasaka a Hannuna"

"Kai yimin bayani mana menene yafarau?"

"Kinga mama Wallh kaff garinnan yanda nasan ana saida zinare saida naje wasu wajan kanma ce suke cewa basuda na'urar da zata iya gane mai kyau ne ko fake daga karshe wani yabani shawara akan na aika abuja anan zasu iya ganewa shime naduki pics dins na turawa frnd dina dayake can yaje wajan da kansa ya hadani da branch dinsu nanan bincike yayi bincike hr wajan Police yanzu haka sun rike zoben sai anyi bincike akansa campanyn dake abuja zasu tuarawa dubai companyn da suka kera zoben asamu bayani akansa. ko harma sun turane oho su ayanda can Abuja suke bayani wai suna tunani a kasarnan abune mawuyaci asamu wanda zai iya affording zoben bawai dan babu masu kudinda zasu saya ba sai dan babu wanda zai iya kashe mukudan kudaden nan kawai akan zobe" Yanzu sun karbi details dina da komai nanda 3days zamuji bayani dan zasu aika dashi abuja idn bayani yafito idanma ma kamawane zasuzo su tafi dani ya wurgamin Harara bayan karasa maganar.

"A hannun wannan ja'irar nake ganin zoben zakiyi bayanin yanda kika samu idanna kamaki na kalada miki duka" dagani har Mama bmuce komaiba.
24hours kawai zoben yayi a wajansu yaya Habibu yasamu kira daga wajan police da campanyn da suka karbi zoben. Hakuri sosai suke bashi. Babban police dayake kan case din yafara magana.

"An tura dashi can abuja daganan suka tuntubi campanyn da suka kerashi sun tabbatar musu da guda biyu kawai suka kera kuma maishi yayi musu biya ya bukaci kar asake kera makamancinsu couples ring ne na mata da miji wannan shine na matar. Sun tuntubi wanda yasaka aka kera masa zobinan ya tabbatarda ba sacewa akayi ba zoben yana muhallinsa ne. Mun bukaci address da komai saboda binciike company sun bamu da yardar wanda yasa aka kera masa zoben. Address dai-dai yake da naka wanda kabamu sannan sunama surname yazo daya da naka Zainab Muhammad Dani. Kaga kenan bamuda wani dalili face mubaka kaynka amma a shawarce kusan yanda zaku killace zoben. Idan ku yan siyasa ne zaija muku Babbar matsala zai bata muku carrier naku sboda babu wanda zai yarda bada kudin government kukayi amfani wajan sayan zoben ya zame muku babbar kadara ba daganan jami'an tsoro na fanni daban-daban zasu shiga zancem daga karshema government zata karbi zoben. Abuna biyu idanku ba yan siyasa bane duk dai ido yahau kan zoben ba',asan abunda zai jawo ba dan mutane dayawa sunsan dazamansa mukanmu cikinmu bamusan ko akwai masu boyeyyen nufi da zasu iya neman mallakarsa ba. Abu mafi alkhairi shine kusan yanda zaku adana shi" Godiya sosai yayi masa sannan ya amshi zoben ya tafi.

Yadawo yayiwa Mama bayanin duk yanda sukayi.

"Mama dan Allah ki fadamin abunda yake faruwa har yanzu fa bakimin bayanin komaiba" cewar Yaya Habibu. Mama tayi masa bayani jikinsa yayi sanyi haka itama Jikinta yayi sanyi sosai dole Baba yashiga mganar amma sai zuwa jibi tunda gobe Maryam ta fadawa Marmeeyy akan taji iyayensu suna cewa zasuzo. Kuma har Mama ta sanar dashi amma cemasa kawai tayi zaiyi baki iyayen Maryam zasuzo. Shikanma yadauka cewa zasuzo ne suyi musu godiyar zaman Maryam kamar yanda Mama ta fada masa dawowarta tace sunata godiya sunce ma zasuzo suyi masa godiya."



ZAINAB ALABURA

Wannan Littafin na kudine kibiya 300Naira ta asuusn bankina domin samun damar yin karatu cikin kwanciyar hankali. 0003075326 JAIZ BANK ZAINAB M BAWA


Ranar aka sake mana result yayi kyau amma banci jarabawata guda daya danayi ta karshe ba lokacin da wannan abunn yafaru tsakanina da Hamma. Hamma gabaki daya ya dauki laifin ya alakantashi da kansa hakuri kawai yake bani. Banji dadin rashin cin jarabawarba amma haka na daure na nun babu wani abun kodan shima Hamma ya kwantarda hankalinsa. Har alkawarin fitar dani kasar waje karatu yayi saboda yayi silar faduwata a jarabawa yayi alkawarin rike hannuna zuwaga samun cikagaba yayi alkawarin sanyani a hanya har sai nacika mafarkina. Nidai kawai dariya nakeyi wannan abun kadai yasa naji zafin faduwa jarabawata ya ragu araina.


______________________

Mama batayi wani aiki ba kawai order snacks tayiwa masu zuwa dakin Baba kuma tasan akwai cartons na drinks da ruwa tun auren Ya Ahmad da sukaje aka cika musu butt din mota dashi Alhaji Habibu mahaifin Mama kawai iya wand . zaiyiwa iyalnsa tsaraba ya deba dake yanada ciwon sugar bayashan carbonated drinks sauran duka Baba yadawo dasu ya bawa matan ya ajiye saurn dake shima ba gwanin shan zaki bane.

Baba yana zaune Mama tashiga wajansa da mamaki take kallonsa yaya Baka shirya ba? Ya kalleta.

"Oh wai dawuri zasuzo?" Haka nake tunani dan Umminsu ta kirani ina tunanin tafiya biyu zasuso da neman iri" saida gaban Baba yafadi dan yanajin haka yasan Zaiyi wuya idanba Marmeeyy bace. Yadaure yace.

"Tofa wace kenan cikin yaran?" Sai sunzo dai maji dannima haka aka sanar dani" hmy

"Toh Allah yakawosu barina kira Baba (Alhaji Habibu) na sanar dashi bai kyautu suzo su sanemi ni kadai ba.

" Eh hakanma yayi Allah ya taimaka ya amsa da amin"
Alokacin yakira Alhaji Habibu ya sanar dashi. Yanata Allah-Allah Alhaji Habibu ya iso kafin isowarsu saboda idan ya kasance Auren Marmeeyy akazo nema zaifi kyau ace yana kusa danshi zaifi yimusu bayani yanda zasu fahimta sosai.

Kafin Alhaji Habibu ya iso su Abban Hamma da mahaifinsu dawasu daga cikin yan uwan Abbansu sun iso. Ana gaggaisawa Alhaji Habibu ya iso shima. Batareda bata lokaci b suka sanarda abunda yakawosu. Bayan shaida musu da akayi yara sunason junansu. Baba yaji Babu dadi matuka dayasan akwai wanda Marmeeyy takeso da bazai taba aurarada itaba shiru yayi yakasa magana.
Alhaji Habibu ne yayi musu bayani hadeda basu hakuri bai fito kai tsaye ya fada musu anyi mata aure ba amma ya fada musu da sadakin wani akanta ita kanta yarinyar bata saniba yakara basu Hakuri. Mahaifin Abbansu ne yafara magana.

"Babu damuwa Allah yasa hakan shine mafi alkhairi Amma kaya kam munzo dasu bazamu koma dasu ba mu a al'adarmu ba'a fita da kayan aure adawo dasu. Dan hakw idn kanada wata yarinya koda kanwarta ce sai abashi mu mika sadaki kamar yanda mukazo da niyya anyi niyyr kulla zumunci Allah har indai akwai yanda za'ayi toh kar afasa"

"Amma baka ganin su yaran bazasu so hakanba?" Cewar Alhaji Habibu.

" Ai tunda itama wannan an karbi sadakin ta batareda saninta b suma hakan za'ayi inada tabbacin yakini da kuke dashi akanta shiyasa suka yanke hukunci bada saninta ba. Suma wadannan ku sanya wannan yakinin akansu ina fata bazasu bamu kunya ba dan sun samu tarbiya. Inbanda yanzu zamani ma da yara suka kwallafa rai a soyayya ba dacan ina akasan wata soyayya aure akeyi batareda Sanin junaba kuma muyi hakuri mu zauna"Kowa a wajan ya aminta da shawarar da mahaifinsu Abba ya bayar na hada auren Hamma da Aysha Baba shikansa yaji dadin hakan amma jin dadinsa yana yankewa kasancewar baisan yanda yaran zasu dauki zancen ba." Dake Bbbane sosai dan har Alhaji Habibu ya girma ya sanya babu gardama duka mutanen wajan suka amince aka karbi sadaki na Aysha da Hamma. Dake azumi saura 2weeks hakan yasa aka saka auren sallah da sati biyu. Duk wani abun al'ada alokacin sukazo dashi. Dama sun gama shrinsu na komai dan haka aka saka rana bayan Sallah da sati biyu. Yara kuma zasuzo suga juna."

Anrabu cikin aminci da mutunta juna basu wuce gidansu Hamma ba gidan Mahaifinsu Abba suka wuce zasu tattauna. Mahaifinsu yaja musu kunne barinma Abba akan kar wanda yasake yafadawa iyalansa dalilin fasa auren har Ummi dashi kansa Hamman dan yasan iyayenta bazasu yanke hukunci su karbi kudin aurenta batareda saninta ba babu wani kwakwaran dalili. Dan haka kada ayi musu katsalandan abarsu su sanarda ita da kansu. Kowanne a cikinsu ya aminta da hakan.


Ummi kuwa batasan yanda abun ya kaya ba kawai wucowa tayi gidanmu.

Tunda naji muryarta na kule adaki dama tunda bakin suka

26 / 58