Waye Shi Complete Hausa Novel

Author :  Billyn Abdul Category :  Romance

Chapter   16 / 58

45K to 48K   out of 171.2K words

ya lumshe idanuwansa kawai yana hasasho yaushe zai shiga rayuwarda yafara mafarkinta a ɗan fara soyyayarsa wanda abaya bai taɓa mafarkin shigarsa wannan yanayinba."
Wayarshi dake kan ɗan table tafara ruri yasan dole na gidane yake kiransa. A kasalance ya buɗe idanuwansa ya kalli wayar yaga Nawrah. Maida kansa yayi batareda yayi picking ba ganin haka ya tabbatarwa  مساعد شخصي (P.A) bayason ɗaga kiran dan haka baiyi tunanin ɗauka ya miƙa masa ba.

Ba'a sake kiran wayar ba 5minute later yaji an buɗe ƙofar office ɗin yana buɗe idanuwansa a fili yace.

"Nawrah"  Ta ƙafaso ciki مساعد شخصي(P.A) yana ganin shigowarta yatashi yafice a office ɗin."


ZAYNAB ALABURA.

*BIBIYATA YAKEYI*
*(WAYE SHI?)*


Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya.



P.A yayi mata barka da zuwa ta amsa sannan ya fita itakuma ta ƙarasa ciki ta zauna. Kallo take masa mai cikeda tuhuma ya sakar mata murmushi haɗeda faɗin.

"مرحباً حبيتي "
"Welcome My love). ta ɓata rai sosai sannan tace.

"Kana kallon kirana kaƙi ɗagawa" ya girgza kai yace.

"Ina aikine shiyasa" cikeda Shagwaɓa irinta mai neman rikici tace.

"Mood Habibi wani aikine haka yafi kiranda nake maka? Kawai bakason muyi magana ne dan Mum takirani ta sanarda ni. inaso naji bayani daga bakinka shiyasa nazo. Wai dagaske tafiyarda kayi just recently shine kaje neman aure? Dan Allah kacemin da wasane please" ya furzarda iska sannan yace.

"Bada wasa bane"

"Amma mood Habibi tayaya zaka auri ƴar africa? Wacce bata sanu aduniya ba? Koda tasanu a duniya ita na sa'ar aurenka bace"


"Babu ruwanku da matarda zan aura ni zan zauna da ita dan tayimin hakan kuma inasonta babu wanda zai hanani aurenta" cikeda Mamaki tace.

"Ka manta mu suwaye? Ka manta danginda muka fito? And kai kanka kamanta kai waye? You're Hammood mansour Kaine Celebraty na ɗaya akaff duniya abun kunyarda zaka jamana kenan? Mutumci zaka zubar mana" Ya runtse idanuwansa Bayason mata tsawa amma tabbas tana shiga huruminda ba nata ba. Ya buɗe idanuwansa akanta. Kamanninsu ɗaya sak dashi ko ba'a faɗa ba ansan ƙanwarsa ce.

"Nawrah" ya kira sunanta. Da mamaki ta maimait.

"Nawrah? Nawrah fa kace?" ya ɓata rai yace.

"Ehem" cikeda ɓacin rai tace.

"Mood Habibi yanzu akan wata can zaka kira sunana? Ka zaɓi sonta fiyeda mu kenan? Asiri tayi maka?. Ya ɓata rai sosai yace.

"Stop it Nawrah karki aibantamin soyayya ta"


"Nawrah" tasake maimaitawa al'ajabi yaƙi barinta Mood mai masifar sanyin rai da tausasan kalamai yau shine yake kiran sunanta bada laffuza masu daɗi ba? Kuma adalilin mace wacce batada wani amfani a rayuwarsa gabaki ɗaya. Saida ya runtse idanuwansa ya furzarda iska ya buɗesu sannan yace.

"Asif Habibty. but kidaina aibantata. Tanada hankali da nutsuwa sannan ina sonta sosai bazan lamunci ki aibantamin itaba bazan iya ɗauka ba"

"Wacece ita? Inaso nasan waccece let me talk to her ko nawa takeso zan bata saboda tarabu dakai. kai ba ajinta bane" ya jijjiga kai haɗeda faɗin.

"kuɗinki su huta She has a multi billionaire husband Therefore yours is nothing"

"Husband" tayi exclaiming.

"Uhum" yafaɗa cikeda jaddadawa.

"Kanabin bayan ta akan sistanka da mahaifiyarka."

"Ko ɗaya kawai ina ƙoƙarin ajiye kowa a mazauninsa ne"

"Okay toh inaso nasan waccece ita."

"لا (No) zaki santa alokacinda na kawota gidana" Yana magana cikeda rashin damuwa a fuskarsa amma can cikin ransa yanajin damuwar rashin karɓan zaɓinsa da ƴan uwan nasa sukayi"

"Mood Habibi" ta kirashi ya ɗago ya kalleta tace.

"bazaka janye maganar auren yarinyar nan ba?" Yayi noding head alamun tabbatarwa.

"Zan saka maka pressure da kai kanka sai kaji zaka janyewa maganar"

"Okay" kawai yace. Aransa yanaji ba pressure ba komai zaka saka sai dai tasaka amma bazai iya janyewa ba. Shi tun kafin ya tunkari wannan lamari saida yagama tsayarda zuciyarsa waje ɗaya yayi shirin tunkar koma menene zai biyo baya. Nawrah dama ya shiryawa rikicinta dan bayau Mum tasaba ba duk lokacinda takeso yayi wani abin kowa bar wani abun nawrah take aikowa ta saka masa pressure har saiya amince ko ya janye amma banda
Akan soyayyarsa sa sam bazai ɗauki hakanba daga wajan koma waye.

Cikeda baƙin cikin ƙin amince da ƙudirinta da yayi ta miƙe tace.

"I hate her " ya taɓe baki sannan yace.

"Dama dame soyayyarki zata amfanarda ita? Tunda ni ina sonta hakan yayi"

"Mooda Habibi ka sani zannemota kuma zansan waccece ita zatasan tashiga abunda yafi ƙarfinta" Ya haɗe rai sosai yace.

"Idan kika taɓata zakiga ɓacin raina kuma zan iya yanke alaƙarda take tsakaninmu" cikeda tsoro take kallonsa taga fuskarsa babu alamun wasa saima ɓacin rai kuma tasan halinsa tsaff zai iya yanketa. Muryatta na rawa na tsoron abunda yafaɗa tace.

"Mood Habibi nice fa 1 and only sisternka. Ya jijjiga mata kai alamun tabbatarwa yace.

"Itama itace kaɗai soyayyata, ki amince da ita idan kinso" Tajuya tafice cike da ɓacin rai. Tana tunani lallai wannan yarinya ba ƙaramin shiri tayi akan mood ba taji ta tsaneta tsana mai matuƙa bazata taɓa saurarawa duk wani wanda zai shiga tsakaninta da ɗan uwanta ba. Kuma dole saita rabasu ta nemo masa macenda tadace da ajinsa.

Ta fice tasamu P.A. Babu yanda batayi ba yafaɗa mata yanda yarinyar take amma yaƙi dan haka kai tsaye tawuce cikin gidan mood. Daga office bai dawo gida kai tsaye ba yafita yadawo bayan magrib ya sameta da mamaki yake tambayarta abunda tazauna yi danya ɗauka tatafi. Tace taɗauki hutu zata ƙwana masa biyu. ta nuna masa komai yawuce ta yarda da zaɓinsa ya yarda da ita sosai dan yasan halinta kamar yanda yakeyin abunda takeso haka itama takebin abunda yakeso abunda bai saniba shine ƙwantan ɓauna tayi masa. ta ɗaura niyyar rabashi da yarinyar nan takowani irin hali."

sai bayan 2week ya shirya tafiya ganin mahaifinsa yanada match in 2weeks time sai bayan ya bugata sannan zai tafi dan haka suka shirya cewa idan yatashi tafiya zasu tafi tare da Nawrah."

---------------


fitowarmu daga test kenan gabaki ɗayanmu muna zaune maryam tace.

"Babe har yanzu baki faɗawa baban bafa gashi time sai tafiya yakeyi"

"Bani nace miki zan faɗa masa ba? Kina zamanki zakiji abba yayi miki magana tace

"shikenan" fadeelah wacce yanzu ta maƙale mana ko ina zamu cikin school da ita sai taje tace.

"Me za'a faɗawa Baban? Maganar aurenku da Hamma ne?" Dan Allah karkuyi gaggawa har yanzu ban fidda ran cewa nice zan auri Hamma ba" naja tsaki sosai dan maganarta ta ɓatamin rai ban kulata ba tacigaba da faɗin.

" kece fa kikayimin shigar sauri yanda kika naniƙewa maryam har ta haɗaku da yayanta danni har yanzu ban yarda cewa ba ita haɗaku ba" Maryam ma ta ɓata rai tace.

"wani iskancine haka fadeelah? Toh banice na haɗasu ba kuma na faɗa miki tun ba yau ba sannan ba Marmeeyy ta naniƙemin ba nice na naniƙe mata saboda abubuwa da dama. Tsawon lokaci muka haɗuda ita kafin muka haɗu dake. Tun muna islamiyya tana A ina B har mukazo hadda tare anan muka sana daganan muka yanke shawarar shiga nursing school tare kowacce ta faɗawa iyayenta suka amince. Sannan ta daɗe sanin Hamma bata taɓa nuna interest ɗinta akansa ba har saida ya ganta yace yanaso dakansa sannan ta amince masa ina marta bata ta wannan fannin babu ruwanta da kowaye mutum ko gidan bukka kuke dashi wallh marmeeyy idan tana sonka tana sonka tsakani da Allah kuma yanzuma zancemda mukeyi inaso nakoma gidansu da zama har mugama exam ɗin wannan lokacin"

Ganin ran maryam ya ɓaci sosai ya sanya Fadeelah ta maida abun wasa tana faɗin.

"ke da'allah wasa nakeyi fa" Maryam tace.

"Nidai na faɗa miki" Inajinsu ko tankawa banyiba saboda banda abunda zance. Lacturer muke zaune muna jira har lokacin bai isoba dama shi kaɗai muke dashi ganin bai zoba ya sanya muka haɗa chapter munata hira acikin friends ɗinmu akwai maison wasan ƙwallo kamana dan haka muka ware mu biyu muna hirar ball muna zancen match ɗinda za'a fara bugawa next week. Tacemin.


"kinsan Hammood yazo ƙasarnan kwanaki?" Nace.

"Nasan zuwansa aiya haukata mana ƙasa gabaki ɗaya ya rikita gidan radio da gidajen TV" ina faɗi cikeda murna da nishaɗi.

"Hmm bawan Allahn nan yayi kinji. Wanda suka ganshi sunce Afili yafi komai yakafawa duniya tarihinda baza'a mance dashiba at his young age yakafa tarihi a wasan ƙwallo" taciro wayarta tana nunamim pics ɗinsa ina following ɗinsa amma bantaɓa ajiye pics ɗinsa ko ɗaya a wayata ba wani irin kyau yake dashi mai masifar hankali. Kyawunsa bai kama kainaba sam gani nake kamar wani aljani barni dai na kalli wasansa dan har shagala nakeyi
Idan ina kallon wasansa. Ɗaya daga cikin friends ɗinmu da muke zaune tana jiyomu tasako baki tace.

"Ƴan wahala wannan mutumin kuna ɓatawa kanku lokaci akansa wallh manya manyan celebraties sunyi sun gashi akwai wata mawaƙiya and tana film ɗin turawa ta mace a soyayyyarsa amma baisan tanayi ba million dollars take biya tashiga ganin wansansa kowani pics ta ɗaura sai tayi tagging ɗinsa. Ke kinsan celebreaties nawa suke hauka akansa?" nayi dariya nace.

ke da'allah ɗaiɗaiku cikin ƴan wasan ƙwallo ke auren celebraties Yawanci matansu basu sanu a duniya ba zakice na faɗa miki matarda zai aura babu wanda ya santa" tace.


"Da wuya fa ke Hmm ai ana show akan yagennan mukam ai sai ƴan kallo a insta muna dariya iya namu likes da comment comment ɗinma marassa amfani dan babu wanda zai dubasu" Nace.


ZAYNAB ALABURA


*BIBIYATA YAKEYI*
*(WAYE SHI?)*


Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya.

" kinganni banida lokacin comment akan abun celeberaties toh me yayi zafi? Iyakacina like idanba sa'a ba harna mutu bazanga ko ɗaya cikinsu ba"

"Haba zainab yada cire rai haka?" Nace.

"Ke rabani na riƙe Hamma na hannu bibbiyu shine babban celebrity na wanda banda kamarsa ke ni ko wannan Hammood da ake ganin kyawunsa kamar hauka ni awajena bai kaimin Hammana ba" Daga wajanda maryam take taja tsaki tace.

"Dama mana yaushe zai kai miki shi? Kowa yana amfani da abunda yake hannunsa kenan amma kika sake haɗasu Allah ya isama Hammood" Cikeda ɓacin rai nace.

"Kekam dai anyi banza wallh waya keƙin nasa?" Saida tayi dariya ganin ta cikani sosai tace.

"Ai gaskiya ce zaki haɗa ɗan larabawa da ɗan fulani" nace.

"Kaman a kunnen Hamma"

"Kifaɗa mana yau kika saba min sharri Shima kansa idan yaji zai yaji kunyar abunda kikayi" takaici yasa nadaina kulata kota sakoni cikin zance bazan mayar matada amsa ba.

Muna zaune kusan 2hours lacturer yayi waya akan bazai samu zuwa ba bamuji haushi ba danma mun zauna munyi hirarmu abunmu mungode Allah dan haka na miƙe nace.

"idan kinga dama kizo mutafi" tasan da ita nake tace

"bantashi sai Hamma yazo"

"aidai kya barshi yahuta ko? Tunda shi baɗan aiki bane" ta taɓe baki tace.

"Aishi ya maida kansa driver dan haka yacika ladansa" nace.

"ke dai na daɗe banga ƴar rainin hankali kamanki ba wai Hamma ne driver" Nakoma ma zauna ban kirashi amma Ita ta kirashi"

Kusan 40minute sai gashi ya iso.

Tare muka fita dukanmu kowa yakama gabansa maryam tace fadeela tazo mutafi saboda hanyarmu yazo ɗaya samu sauƙeta a hanya. hakan akayi fa biyomu muna tafiya muna hira ƙasa-ƙasa nida Hamma. Maryam tace.

"Hamma kaji babe wai kar akiraka yau abarka ka halan yau batason ganinka ne" Ya kalleni na ɓalla mata harara yace.

"Wai haka babynah bakyason ganina? Nayi narai-narai nace.

"Hamma ka yarda kenan? Yarinyar nan ƙarya takeyi cewa nayi fa banason ka walaha yau ka huta shine ta juya maganar"

"Baby wani hutu zan samu batareda na ganki ba? Ai ganinki shine samun hutuna karki damu koda yaushe kikeson samamin hutu ki kirani nazo naganki kawai wannan shine babban kwanciyar hankalina" Nace.

"Toh in sha Allahu Hammana" maryam ta gefe ta kallon reaction na fadeelah dama ta jawota ne dan tasan dole Hamma zaiyi abunda zai ƙure mata tunani dataji muna hira ƙasa-ƙasa kawai saita sako wannan zancen dan tasan dole zai yi maganarda zata maido da fadeelah hankalinta. Kamar ƙwai haka yayita lallaɓina muna tafiya hankali har suka kawoni gida ahakanma Saida muka tsaya mukayi hira sannan nayi musu sallama nafice.

Ina shiga gida da kusan 30minute saiga kiran Maryam ina picking dariyarta nafara ji tana faɗin.

"Babe ya kikaga idon fadeelah nayi hakane kawai dan tasan matsayinta wallh yarinyar nan ƴar rainin hankali ce saita faɗi magana saita wani waske tace wai wasa takeyi kuma bafa wasan takeyi ba kawai dai taga rai yaɓacine Allah natuba mai Hamma zaiyi da ita?" Dariyar nima nakeyi nace.

" kedai bakida dama wallh da tasan waye Hamma dama bata fara wannan haukar ba na tabbata da Hamma yasam cewa yarinyar nan tafaɗi abunda tafaɗa da saiya tsayar mata Wallh Hamma baya ɗaukan rainin hankali" Maryame tace.

"Batta yanzu zata shiga hankalinta tasan sonki yake na gaskiya bawai cusa masa kai akeyi ba"
Mun daɗe muna waya da ita sannan Mukayi sallama."

Har tsawon sati biyu banyiwa Baba maganar maryam ba tayimin magana harta gaji tayi fushi ta sauƙo dan tace banida niyyar tambaya mata Baba ne taga alamun banaso tazo gidansu.

A yau na yanke shawarar samun Baba amma saina fara samun Mama nayi mata magana Anty fadeelah tana wajan aysha kuma ta school. Dana gma yiwa Mama bayani Anty fadeelah tafara amsawa.

"Lallai marmeeyy bakida kirki duk yanda maryam ke sonki kawai ta tambayeki ta zauna agidanku na ƴan satikai amma kiƙi? Ai ana rama hallaci da hallacine" mama tace.

"Barta ni banga abun tsayawa tunani ba dahar zataƙi tambaya ba yarintar nan dai iya kyautatawa tanayi miki amma" Nace.

"Mama dan Allah ki tambayeshi"

"A'a-A'a jeki tambayeshi da da kanki da kinso tazauna aida tun wuri kin faɗamin na tambaya miki shi amma yanzu da lokaci ya ƙure kejiyi da kanki" Nayi fuskar tausayi sannan nace.

"shikenan bayan isha'i zan shiga nafaɗa masa Allah yasa yayarda" mama tace.

'Amin" Bayan yadawo daga sallar isha'i nashiga wajansa nasamu alokacin za'a fara haska wasan ƙwallon ƙafa nazauna muma kallo cikeda sha'awa nake kallon yanda Hammood yake sarrafa ƙwallon Baba ma yazauna ya nutsu yana kallo kamar mai nazarin wani abu. Bantaɓa kallonsa ya nutsu haka wajan kallon ball ba kamar yanda yayi yanzu Muna zaune har aka gama sannan Baba yadawo da hankalinsa gareni dake mun kwana biyu bamu samu zama irin haka ba. Yace.


"Marmeeyy Ball tayi daɗi koh?" nace.

"tayi sosaima kuwa Baba Hammood kwarrarrene wajan sarrafa ƙwallo" Baba ya jijjiga kai cikeda gamsuwa da abunda na faɗa. yace.

"Tabbas yana da ƙwarewa. Yana burgeki kenan? Yayi maganar in a serious tone" na kalleshi nace.

"Sosaima Baba kaima ai yana birgeka"

"Yana burgeni kuma yanada nutsuwa"

"Uhmm, Uhmm, Uhmm ɗinda nake faɗi ya sanya Baba yace.

"Marmeeyy akwai magana ne?"

"uhmm dama Baba maryam ce Umminta da Abbanta zasu tafi Umrah kuma zasu ƙwana biyu shine tace na roƙeka ka tambayi abbanta tadawo nan gidan da zama saboda mu samu muyi karatu cikin ƙwanciyar hankali" Ga mamakina sai naji Baba yace.

"Shikenan ai babu damuwa zanyiwa mahaifinnata magana saiki bani numbernsa" nayi murna sosai alokacin nabawa Baba numbern Abba yacemin zai kirashi zuwa safiya suyi magana.

ina komawa ɗakin Mama kai tsaye ɗakinmu nawuce saboda exam ta gabato yanzu kusan koda yaushe karatu kawai nakeyi wanka nashiga saboda yanayin zafo dayake garin. Nafito daga wanka idona yakai kan zoben dake hannuna natsaya kallonsa inaso natunano yanda naga makamancin irinsa a ƙwanakinnan gabana yayi mummunan faɗuwa."


ZAYNAB ALABURA


Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun bankina Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya.

Duk yanda naso nayi tunani nakasa tunano yanda naga makamancin wannan zoben ajiyar zuciya na sauƙe kai tsaye nashiga tunani idan zan iya tunawa tsawon wata biyu kenan bansamu saƙo daga wannan number mai turamin saƙo ba, to ko lpy? Ko wani abunne yafaru? Kokuma ya haƙura ne? Rashin samun amshoshin tambayoyina yasanya naji gabaki ɗaya babu daɗi nayi tagumi ina tunanin to ko wani abunne ya sameshi? Na sake sauƙe ajiyar zuciya akaro na biyu shin to ko wani abunne ya sameshi? Nayi zaton ya haƙura ne ya daina amma alamu bai nunashi acikin mutane masu sarewa ba. Wannan yanda yakeda jarabar naci bazai taɓa jaa baya ya haƙura da abunda yakeso ba. to koma meyasa zan damu dashi? bayan abunda nake nema ne ya samu yadaina damuna kamar yanda nake buƙata, na sake sauƙe wata ajiyar zuciyar. Saina samu kaina dayin addu'ar Allah yasa  yana lpy. Uhmm koni maima ya dameni da zancen wannan mutumin?" na tambayi kaina. Ahaka anty fadeelah tashigo ta sameni ta zauna bakin bed sannan tace.

"Marmeeyy karatun kenan?" na ɗago na kalleta na zumɓuro baki bance komai ba tasake faɗin.

"Hamma ne ya sakaki tunani koh? Yasa kin kasa karatu toh aikuwa gara yabarki kiyi karatu" na yatsina fuska nace.

"Babu ruwan Hamma wani tunanin nakeyi can daban"

"Wani yashigo rayuwarki bayan Hamman kenan?" na zaro ido haɗeda faɗin.

"Rufamin asiri kar wani yaji labari" tayimin harara tana faɗin.

"ai gaskiya na faɗa dan duk wanda ya kalleki a lokacinda na ganki zai fahimci hankalinki yana wani wajan daban"

"kinganni ni tunanin exam ma nakeyi ko kaɗan hankalina bai kaiga Hamma ba" nafaɗi hakanne dan gujewa ta sake ɗauko wani abin. Ta jijjiga kai sannan tace.

"Bikin Ya Ahmad yanata ƙaratowa wai dagaske kike zakije?" Na jijjiga kai alamun tabbatarwa sannan nace.

" sosai ma kuwa"

"Marmeeyy baƙya tsoron mummynmu ba lallai ta ƙarɓeki ba kasancewarki ƴar babanmu abune maisauƙi tahuce haushin mahaifinmu akanki"

"Kuma ai ƴaƴan babanmu ne tunda ta amsheku nima zata amsheni sannan nifa bada niyyar zama

16 / 58