Author : Billyn Abdul Category : Romance
take burinta yacika dan bazanje gidan wani ina tunanin mijinta ba koma wanene na aura its yanzu bai dameta ba. Nayi murmushi mai ƙayatarwa sannan nace.
"Nagode Amin"
"kinga nacewa Baba yabamu ke mutafi ashe kinyi aure kodan yanzu ma ai bata ɓaci ba ta'iya yiwuwa mijin ba'a kusa yake ba sai yabamu aronki"
" dayake yace miki ya gaji da ita zakice yawani baki aronta" kefa aysha kina bani haushi wallh feleƙenki yawa gareshi barinma yanzu da kikayi aurenann wani rawae kai kikeji dashi Allah yaso bake kaɗai bace mai auren itama Marmeeyyn tana dashi" Anty fadeelah tafaɗa rai aɓace. Baba kallonsu kawai yakeyi baisan akwai rashin jituwa haka tsakanin Fadeela da Aysha ba.
"Kema sai kiyiwa naki manemin magana yafito a aurar daku gabaki ɗaya yazama saura ƴan ƙananun kawai a gabanmu" Anty tafaɗa cikin zolaya. Anty fadeelah najin Haka tayi shiru.
"Wayar Ya Ahmad tayi ƙara ya amsa sannan yatashi yafice. tun kafin wayar Ya Ahmad tayi ƙara naji ƙamshinsa a cikin hancina dukda dama tun fitarsa jiya palourn bai saki ƙamshinsa ba na lumshe idanuwa na ina shaƙar ƙamshin, Ya Ahmad yadawo yace.
"Baba Hammood zai shigo ku gaisa saboda gobe sassafe zai tafi kamar ma yafaɗa maka koh?"
"Eh munyi magana dashi ya sanar dani hakan" Mama, Mummy, anty, suka miƙe zasubar palourn Baba yace su tsaya su gaisa da Hammood tukunna. Aysha ta zauna dirshan zuciyarta tana faɗin yau dai zataga ƙaryar da ake musu ta iya yiwuwa wanine mai suna Hammood ya auri Marmeeyyn Suna zaune a palourn Ya Ahmad yashigo tareda Hammond biye dashi akan ƙofar na buɗe idona ya sauƙa akan kykkyawar fuskars ajiyar zuciya nayi a hankali yanda Babu wanda zai jiyoni. Galala Aysha tasake baki tana kallon Hammood dagaske fa Hammood ɗinne wai dama dagaske suke? Kodai mafarki takeyi? Tanjin su Mama sun fara gaisawa dashi ta miƙe tabar ɗakin wani iri takeji aranta. Wato dagaske da suketa faɗin Hammood Hammood, Hammood ɗinne yawani ba? Dagaske Baba aurawa Marmeeyy Hammood yayi ita kuma ya bata Hamma, wannan ai ba dai-dai bane waraki ne ƙiri-ƙiri tunda babu abunda batafi Marmeeyy ba dahar zai zaɓi ya inganta rayuwar Marmeeyy akanta saida ta zubda ƙwalla tana yiwa Marmeeyy dariyar mugunta ashe itace abun dariya ba Marmeeyy ba. Jikinta har rawa yakeyi ta kira Hamma tace yazo sutafi shikan harya koma ya ƙwanta yaji wayarta.
"Dare yayi ki ƙwana a gidan kawai narigada nashiga na ƙwanta idan Allah yakaimu gobe sai nazo na ɗaukeku da narmeeyn gabaki ɗaya" takaici ya hanata sanar dashi abunda kunnuwanta da Idonta suka gani kuma sukaji mata. Ta datse wayar. Idan Ya Ahmad zai tafi yazo ya maidata kawai bazata iya zama a cikin gidan tana kallon wannan kayan baƙin cikin ba. Tana tunanin ko idonta bai gane mata dai-dai ba ta miƙe tasake komawa dan tabbatarwa daga fitarta har dawowarta babu wanda ya lura.
Hammood bai zauna a palournba bayan gaisawarsu yafice Ya Ahmad ya kalli Marmeeyy.
"Marmeeyy ko zo kije mana, da asubahi zasu wuce abuja daga nan kuma zasu wuce can ƙasar. Na miƙe a kunyace na bi Ya Ahmad. A jikin motar Yaya Ahamd ya tsaya.
Baba yace zaki bishi kutafi saiya dawo dake ya lura baya samun sake idan ana gidan yake dan jiya bai wani daɗe ba gashi kuma Baba yacemin yana jiyo ihu da hauka da akayita yimasa a palourn wabda ina tunanin su rauda ne dan tun safiya suka fice neman yanda yake zaune ina tunanin har yanzu basu samu bane yasa basu dawo ba ni kaina sun kirani sunata roƙo akan ne faɗa musu masauƙinsa bama faɗa musu masauƙnsan bane ko sunje bazasu taɓa samun shiga wajansa har su ganshi ba. Babu wanda yasan Hammood yana bauchi shiyasa kikaga baya yawo da dare. Kuma koda ansan yana Bauchi bazaiyiwu yayi yawo da rana ba sai lokacin da babu ido ko a ƙasashen waje baya yawo da rana idan bada wani dalili mak ƙarfi ba saboda su kansu garuruwa dokarda suka saka akansa kenan har indai zaiyi yawa da rana toh akan samu cinkoso na a layukanda zaibi gabaki ɗaya. Ina faɗa miki wannan a matsayinki na ƴar uwata ki riƙe Hammood dakayu Marmreyy a ganin idonki kinga yanda ake haukace masa duk da su waɗannan basu kai matsayin ya tsaya ya kulasu ba shiyasa kikaga wunin rana guda location ɗinsa ya gagaresu samu.
Basu bane matsalar Marmeeyy akwai lokacin da zaizo zakiga isassu wanda suka kai su bibiyeshi suna bibiyarsa bance ki bawa ko wace mace damar raɓarsa ba idan kin mallakeshi yazamana kin mallakeshi ne ke ɗaya. So sone amma sonkai yafi ke kaɗai nakeso kiyi rayuwa da Hammood har iya ƙarshen rayuwa inaso ki gwadawa duniya Kyau. Shahara dukiya basu namiji yake dubawa jikin mace ba. Inaso ki gwadawa duniya cewa mu baƙaƙen fata akwai rawarda zamu iya takawa a rayuwa ki gwada musu cewa you can keep your man for only You. Ke kaɗai ce a ransa rayuwarsa suda sukeda duk wani abu najin daɗin rayuwar duniya bai ishesu gani ba yasamu duk wani abunda yakeso a wajanki kuma hakan ya ishesh Marmeeyy hold your man very tight Allah ya kashe ya baki. Kuma ina faɗa miki ba ƙaramin so Hammood yake miki ba ke dai karki bamu kunya" tunda yafara magana nake murmushi kalamansa suna zama daram a ƙwaƙwalwata. Bayan yagama nace.
"In sha Allah yaya"
"Yawwa toh jeki Allah yayi miki albarka yana jiranki" yashige mota nikuma na nufi wajan motocinda nagani. Kafin na ƙarasa naga ya zagayo daga bayan motar ashe bai shiga ciki ba buɗemin yayi na sakar masa murmushi sannan nashiga nazauna ya rufe kafin ya zagaya an buɗe masa ƙofa. Ba masauƙinsa mukaje ba yawo muke tayi a cikin gari sai daga baya naga motocin sun rarrabu yazama saura tamu kaɗai akan titin shima ana zuwa wani waje mai yalwar bishiyoyi Sannan kuma babu kowa drivern yaja ya tsaya ya saida ya sanya mask da facing cap sannan ya fita yazo ya buɗemin na fito. Sai kallona yakeyi dan nayi masa kyau a cikin Hijab ɗin sosai. Ahankali muke tafiya muna shawagi a wajan iska mai sanyi da daɗi tana haɗuwa da turarensa tana kaɗawa. Ya juyo ya dubeni.
"You look good in Hijab" nayi murmushi bance komaiba tun kafin yatafi naji nafara missing ɗinsa.
Mun daɗe a wajan saida dare yakusa rabawa sannan muka ɗauki hanya naɗauka gida zamu wuce sai naga munwuce masauƙinsa. A hanya motocin sukazo muka haɗe muka ƙarasa a tare.
"Daga wani waje suka tsaya muka ƙarasa ciki ranar nashiga ɗakin na yaba ƙyawunsa amma yauma saida nasake yaba ƙyawunsa. Bamu daɗe da shiga ba room service suka danna belt na ƙofar ya tashi buɗe musu bayan yayi confirming wanda suke ƙofar suka shigo da trays ana trollyn ɗinsu a table suna zuwa suja ajiye abincin ya buƙaci nazo naci kaɗan na taɓa natashi da ake cewa larabawa basuda ci nikam yau naga saɓanin hakan har mamakin abincin dayaci nake saida na buɗe baki ina kallonsa yagane mai nake nufi yayi dariya.
"I know i eat alot. I'm a footballer dole naci" na jijjiga kai alamun gamsuwa. Saida yagama sannan yatashi ya nufi sirf ɗin kayansa wani akwati maj masifar kyau ya ɗauko ban luarda abunda yakeyi ba yazo dai-dai kunne na ya raɗamin.
"Take up your hijab" saida gaban yafaɗi nakasa cirewa a hankali ya taimakamin na cire wata sarƙa yaciro sakamin a wuyana har ɗan kunne da zobenta ya sakamin sai sirirn bracelet ya ɗaura ya juyo tagaba duk ina kallon abunda yakeyi ya kamo ƙafata zai ɗauramin leg chain mai hawa-hawa mai masifar kyau banga ɗan kunne da sarƙan wuyana ba amma ganin bracelet da leg chain kawai ya tabbatarmin da kyauwnta. Natsaya ina ƙare masa kallo a yayinda yake ɗaura chain ɗin a ƙafata tun daga sumar kansa har kan hancinsa. natuno wani abun nayi saurin ɗauke ƙafata bsi kaiga ɗaurawa ba ya jiyo ya kalleni na girgiza masa kai.
"No not this bandashi kabarshi"
لماذا"
(why)"
"Uhmm, Uhmm narasa yanda zanyi masa bayani ya tsraeni da ido yanason ƙarin bayani. Na dubirbice narasa yanda zan faɗo zancen gashi kuma ya tsareni da kyawawan idanuwansa yana kallona.
"Mufa ana duk mace mai saka anklets abunda ake mata zargi daban koda bada wata manufa tasaka ba" ya kalleni har alokacin baice komaiba yana neman ƙarin bayani.
"Mata masu saka sarƙan ƙafa ana musu kallon lesbians wani wajema masu neman maza" saida yayi dariya sannan ya miƙe daga kan guiwowinsa dayake ya zauna a kujera gefena.
"is okay now comply with ur culture amma zaki sakamin a gidana nagani kullum dan ina sonsu sosai" na sunkuyarda kaina ƙasa narasa eh zance ko A'a idan nace eh ina ban zaƙe ba? Hannuna yakama har gaban ya nunamin sarƙan tayi kyau sosai na saita ƙaramin kyau ni kaina.
Ya miƙomin box ɗinta da ring sai anklet dake ciki na amsa nayi godiya.
"I'll leave today duk ranarda nadawo zan tafi dake kisaka a ranki I'll never set my foot again a wannan ƙasar and leave without you. I'll be back when you've completed your school And thats amonth i think. Be ready to live with your husband. Idan nasake dawowa I'll tell you more about my self. Ina jinsa bance komai ba har yagama maganarsa ya ciro Atm ya damƙamin nabi Atm ɗin da kallo sunanane ajiki ya ɗauki phone ɗinsa ya danna wasu numbers nan take message ya shugomin anyi activating atm ɗin da layina ya buɗe kenan?.
"Kiyi amfani da wannan. A komai da zakiyi don't ask Baba kinji na gyaɗa masa kai. Yayimin peck a kumatu sai wajan 3am kafin ya maidani gida a ƙofa ya tsaya ya rakoni ya ciki ya sakemin peck a kumatu haɗeda faɗin.
"I'll miss you" nima inaso nace hakan amma nakasa dan haka kai tsaye nayi da yaranda bazaiji ba nima haka. Ya miƙamin waya ƴar jaka da safe nabawa Baba na amsa Mukayi sallama na shige gida shima yatafi."
Comment ɗinku yayi ƙasa wallh da wanne zanji da school koda rashin comment😩😩
PAID BOOK
Littafin BIBIYATA YAKEYI (WAYE SHI) na kudine ki biya Naira Dari uku 300 Domin kisha karatunki hankaki kwance,
account 0003075326
Zainab m Bawa JAIZ BANK Ko katin MTN ta wannna lambar 08161146563 shaidar biya Ta 08161146563 da zarar kin biya Hankli kwance zaki samu damar karanta wannan labarin ku shigo daga ciki kar ayi babu ku domin wannan
tafiyace wanda salonta da tsarinta ya bambamta da ko wace irin tafiya karki bari ayi babu ke."
Idan Kuma kina bukatar Aringa tura miki pc kullum Dari hudu 400 kacal zaki biya batareda an Sanyaki cikin group ba zaizo ya sameki har yanda kike."
ZAYNAB ALABURA
Wannan littafin na kuɗine kibiya ₦300 ta asusun banking Kamar haka 0003075326 Zainab M Bawa JAIZ BANK ko katin waya na MTN ta 08161146563 haɗeda shaidar biya
Da sanɗa nashige cikin gidan dan banaso kowa yaji shugowata lokacin ƙarfe 3:45am na murɗa ɗakin Mama naji a buɗe kai tsaye na shige ban shiga uwar ɗakinta kamar yanda nasababa yanzu na wuce cikin ɗakinmu. Anty fadeeala nagani tana sharar baccinta na shiga a ahankali na cire hijabin jikina dayake ƙamshin turarensa na ajiye gefe na rage kayana na na cire sarƙar na zubata cikin box ɗinta na ajiye sannan na ƙwanta cikeda tunaninsa bankaiga samun runtsawaba aka kira sallar aubahi. Natashi nayi raka'atanil fijr sannan najira aka shiga na gabatar da Da sallah.
Mama tatashi tayi sallah tashugo zata tashemu ta sameni zaune akan sallaya batayi zaton na dawo ba san batasan shugowata ba.
"Kuntashi kenan?"
"Eh natashi" baki tashi fadeelah ba tukunna Toh ki tasheta kuyi sallah" na amsa sannan tafice. Bantasheta ba dan nasan ba sallar zatayi ba ina zauna akan sallaya ina addu'oi naji bacci na ƙoƙarin ɗaukana na tashi na ƙwanta akan gado aƙanƙanin lokaci bacci ya ɗaukeni. 7:00am Mama tafita zuw akitchen dan tanadarda abun karyawa a gabaki ɗaya gidan. Dake gun ranarda suka san Mummy tadawo kenan Mama face mata ta ƙwana ɗakin Baba amma haka fire taƙi sai jiya da ƙwanan Mama ya ƙare sannan ta shiga ɗakin nasa. Kamar yanda suka saba 6:30am suke fitowa hura wuta a ɗaura abun karyawa saboda yara masu zuwa makaranta. Yau Mama ta mance shaff dake ba itace da girki ba saida ta tuna cewa Mummy ce saita tashi tafito dan tasan Mummy bazata taɓa zuwa kitchrn ta hura musu wuta da sunan zasuci abinci ba. Jin ɓuruntun Mama a cikin gida yasa Anty tafito tafara tayata aikin tana faɗin.
"Yaya naga fa ba kece kika ƙwana ɗakin Baba ba? Yau mummy ce kamar yanda tsarinmu yatafi amma meyasa kece a kitchen?"
"Babu ahunda yasa Mummy kam ai ita baƙuwace bazamu barta tayi aiki yanzu ba"
"Kinsan wacece Mummy fa ko ba baƙuwa bace bazatayi aikin kitchen ba kinsanta kuma ni bazan iya kallon kina aiki batareda na tayaki ba bazamu zaune kullum mune zamu ringa yimata girki tana ƙwana da miji ba zaman da akayi abaya a yanzu bazai maimaitu ba ko abaya ba'ayi irin wannan zamanba dan tanada ƴan aiki masu yimata aiki bamuba wallh idan muka sake zaman yanzu sai yafi na baya ƴan aiki zamu dawo cikin gidan" murmushi Mama tayi.
"A'a Habiba bazamu dawo ƴan aiki ba kuma yanzuma kyautatawa ce bai kamata mubarta tashiga kitchen ba dan yanzu ita baƙuwace a gidan sannan banaso ki sake irin wannan maganar kinga matsalarda aka samu wancan shekarun sai yanzu ake ƙoƙarin magance ta banaso asake samun makamanciyarta"
"Shikenan In sha Allahu bazan sake cewa komai ba"
"Hakan yayi Allah ya zaunar damu lafiya suka amsa da amin" Suka gama Aikin sannan suka sakawa ƴan makaranta sukaci Mama tace.
"Barina taso Marmeryy takaisu"
"A'a kibarsu kawai ni zan kaisu kokuma zasu iya zuwa dakansu kinga yanzu ai dakansu suke dawowa"
"Toh hakanma yayi sufara zuwa dakansu ɗin Mama tafaɗi". Sai 8:00am kafinnan Mummy tafito lokacin sun gama komai na gidan. Tayi musu sannu da aiki suka gaisa sannan takoma ɗakinta. 10am natashi dake nasan banda makaranta. Bayan nabi na gaishesu na zauna a palour ina tunanin Hammod ko yatafi? Ina zaune Aysha tafito daga uwar ɗakin Mama nabita da kallon Mamaki. Bansan nana ta kwana ba ko meyasa taƙwana agida? Ko wani abunne yafaru tsakaninta da Hamma tataho gida ta ƙwana? Banida amsar tambayoyina dan haka naja bakina nayi shiru bata kulani ba nima banbi takanta ba tayi waje ina jiyota tana tambayar Mama abinci.
mama tace yana kitchen kishiga ki ɗauka.
"Yanzu fisabilillhi abincin nawa aka barmin a kitchen Mama? Nazo gida bayan ƙwanaki ko tattalina ba'ayi? Toh ni wallh yanzu zan shirya na koma gidana tunda abun hakane"
"Shirya ki koma Aysha dama Babu wanda yace ki ƙwana anan sia taurin kanki"
"Wallh Mama acan ina zaune ake dafamin a kawomin sai dai natashi nasamu wani lokaci Hamma ya biyoni dashi har ɗaki"
"Aikuwa dai gata yakusa ƙarewa dan kin kusa fara shiga kitchen kina girki" miƙewa nayi nafito nima naɗauki nawa abincin nashiga naci sannan na fito tsakar gida Wajan Baba nawuce na gaisheshi yacemin na kira masa matan gidan na shiga ciki na sanarda aikar Baba sannan na dawo ɗaki.
Su duka suna zaune a palourn Baba yadubesu
" Ƴan sayyyar da za'ayi agida na kayan abinci su cefene nakeso kuyimin list sai Habiba su Fita da Habibu kasuwa suje su sayo da kuɗaɗen da suke hannuna dan nasan yanda akayi bikinnan komai yaɗauko ƙarewa. Sannan ga wannan ya miƙawa Mummy. Kuɗin cefene ne na yau nasan har baza'a samu sayowa ba kafin ayi sayyayar gida gabaki ɗaya. Mummy ta jujjuya kuɗin tausayin Baba ya kamata a rana takan kashe ninkin hakan yakai sau 4 a wasu ƴan hidimominta kawai da bata ɗaukesu a komai ba ashe quatern abunda take kashewa ƙananun matsalarta sune cefenan gidan mijinta"
"Kabarshi Kawai zanyi amfani da kuɗin wajena akwak kuɗi a wajena" Baba ya jijjiga kai.
"A'a hakkina nake sauƙewa ki karɓesu a nemi yara suyi cefane a ɗaura abinci dawuri. Sai yaranki su tayaki dan gidan yanzu babu mai aiki" Iya adalcin da Baba zai iya mata kenan yace yara suyi mata aiki dan yasan bazata iyaba kuma shi bayida halin ɗaukan mai aiki Idan yace zai ɗauka kuma bazai yiwu ya ɗauka mata mai aiki ita kaɗai ba"
"Mummy kam ai yanzu baƙuwa ce abari muyi mata ko na wani lokaci ne kafin ta karɓi aikin"
"A'a abunda bazai ɗaure ba gara kar afara shi tun yanzu. Kubari yaranta dai suyi mata zuwa wani lokaci muga abunda Allah zaiyi" Mummy tayi shiru ita dai batasan tayaya zata fara aikin gida ba tunda tun farkon aurensu bawai yi takeyi ba tazo takoma gidansu masu aikinta kaɗai su 3 ne yanzu tayaya zata fara aiki? Bari dai tajira tagani yanzu yaran su fara aikin kwana biyu zata ɗauki maiyi mata aiki.
Ɗaki nashiga na ɗauki wayata anan nayi arba da jakar da Hammod yabani nabawa Baba. Saida naganta kafin na tuna ta batareda ɓata lokaci ba naɗauki jakar na isa zuwa ɗakin Baba na manta da matansa na ciki saida naga takalmansu A ƙofar ɗakin har zan juya sai naji Baba yana faɗin.
"Waye a baƙin ƙofa?" dake yaji footsteps ɗina kuma baiji shigowata ba.
"Nice Baba aika na kawo maka amma tunda kuna magana zan dawo"
"Shigo ki kawomin ai mungama maganar" toh nafaɗa haɗeda yin sallama nashiga ciki.
Na isa zuwa wajansa na miƙa masa jakar ya miƙa hannu batareda yace komaiba saida ta isa gareshi ya ajiyeta a gabanshi sannan yace.
"Menene wannan marmeeyy?"
"Aikeane Jiya yabani nabaka"
"Waye kuma yabaki aika ki bani?" Baba yayi tambayar kansa tsaye dan tunaninsa bai kawo masa Hammood ba.
"Uhmmm Hammood ne jiya yace nabaka nafaɗa ina sunkuyarda kaina"
"Toh" kawai yafaɗa haɗeda buɗe jakar saida gabansa ya buga ganin abunda yake ciki"
"Marmeeyy kikace shi yabaki kuma kibani?"
"Eh Baba nikuma ya bani wannan na miƙa masa ATM daya bani jiya saida na tashi sannan naga abunda yake ciki zaro ido nayi na kalli Baba da yayi shiru bazaka iya gane yanayinsa ba. Ya sanya hannu ya karɓi ATM ɗin ya dubashi sannan ya dawomin dashi na tsaya ina kallonsa danna ɗauka zai riƙene.
"Karɓi Marmeeyy wannan nakine shi yabaki kiyi amfani dashi matsayinsa na mijinki yanada ikon yabaki kyauta yaɗauki