Author : Billyn Abdul Category : Romance
yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖5️⃣4️⃣
______________
......... “Maanal!”.
Ammie ta kira sunanta cikin rawar murya tana mai share mata hawaye da sakin murmushi mai ciwo. Da ƙyar ta sake ƙoƙarin yin magana amma ta kasa saboda muryarta dake neman sarƙewa. Sai kawai ta jawo Maanal ɗin jikinta ta rungumeta tsam-tsam. A tare suka saki kuka mai ƙarfi.
“Ammie kice su tafi, bana son ganinsu wlhy. Sam bana ƙaunar sake ganinsu a rayuwata. Ko tunasu nayi ƙara jin tsanarsu nakey.....” yanda take magana cikin kuka itama Ammien cikin kukan ta ce,
“Shiiiiii bana son irin wannan maganar sam Maanal. Shi ɗin mahaifinku ne. Ita ɗin kakarku ce. Sunada muhimmanci mai girma da hakki a kanku. Koma mi kike tunani ki bari kinji, wannan tsakanin ni da su ne. Kuma ai komai ya wuce ko”.
“Bai wuceba Ammie, bakuma zai wuce ba, har abada kuma bazai wuce ba. Ni dai kawai su tafi. Idan ba hakama zan bar musu gidan. Gara na wuce na koma Abujan. Idan sun wuce sai na dawo”.
“Babu inda zaki je Autana. Kin san yanda nayi kewarki kuwa. Wata nawa ban ganki ba sai video call da bai gamsar dani. cikin lallashi Ammie take maganar, tare da kama Maanal suka koma bakin gado. Sosai take matuƙar ƙaunar Autar ta, dan ita ta fuskanci jarabawa guda uku ne a lokaci ɗaya. Shiyyasa ta fisu jigata da galabaita. Ga babbar jarabawar ciwo mai haɗari da take tare da shi. ALLAH ma dai ya ƙaddara tana da sauran kwana da tuni ta zama tarihi a cikinsu. Shigowar Nene ya katse Ammie daga lallashin Maanal ɗin. Kofin hannunta ta miƙama Maanal ɗin da faɗin, “Ga masoyiyar taki tunda kun mamemu, muda ke muku shirin zuwa wani satin biki sai kawai ku diro mana yau babu notis ja'irai kawai”.
Hannu takai ta share hawayen da suka gagara tsaya mata. Fuskarta a ƙwaɓe ta ce, “Ni garin ya isheni Nene kuma ina kewarku sosai.”
Cike da dabara irin ta manya Nene ta sanya dariya da dungure kan Maanal. “Ja'ira baki son garin amma gaki nan kinyi ƙyau ai. Nifa har wani ɗan ƙiba naga kinyi ma, ji kumatu dan ALLAH ko Asiya?”. Ta ƙare maganar da kallon Ammie tana jan kumatun Maanal. Murmushi Ammie tayi cike da ƙara jin ƙaunar Nene dake tamkar mahaifiyarta a yanzu, ta matuƙar taka rawar gani akan lamarin Manaal musamman a sanda take a halin mutuwa da rayuwa. Ta jinjina kanta da share sauran hawayenta tana faɗin, “Sosai kuwa Nene. Autah tayi ƙiba ba kamar sanda ta dawo sarvese ɗin nan ba. Ga fatanta yay wani kwanciya luff abinta halan ma bata tunawa damu ne a can”.
Da sauri Maanal ta waro idanu akan Ammie, sai kuma ta shagwaɓe fuska da faɗin, “Kai Ammie kema kina biyema Nene ko?”.
Dariya Nene da Ammie sukayi a tare. Nan fa suka cigaba da tsokanar Maanal har sai da sukaga ta ɗan sake tasha kunun gyaɗar da Nene ta kawo matan. Ammie da kanta ta ɗakko mata kaya ta tashi ta shirya. Tana ƙoƙarin maida towel ɗin datai wankan cikin toilet Daddy yay sallama....
___________★
A bala'in hargitse Hajiya Basariyya ke kallon Huznah. Hakama sauran ƴan uwanta. Sai kuma duk suka zaburo kanta suka baibayeta suna tambayarta accident tayi?. Babu wanda ta iya amsawa a cikinsu, hakan yasa Hajiya Basariyya ta kama hannunta kawai suka shiga bedroom. Kamar jira take suna shiga ta rungume mahaifiyar tasu tana mai fashewa da kuka. Ƙanƙameta itama Hajiya Basariyyar tayi hankalinta na ƙara tashi. Sai dai bata iya cewa komai ba har sai da Huznah tai kuka sosai sannan. Ruwa ta bata tasha kafin ta tambayeta abinda ke faruwa.
Huznah bata ɓoyemata komai ba daya faru tun daga zuwanta Abuja har yau da suke tahowa. Shiru tayi tana nazarin komai daki-daki. Ta jima shiru kafin ta miƙe tana cema Huznah, “Tashi kije kiyi wanka zan saka Afrah ta kawo miki abinci da magani, sai kisha ki kwanta ki huta zamuyi magana anjima”.
Kai kawai Huznahr ta jinjina mata itama....
Ɗaki Hajiya Basariyya ta shiga tare da ɗaukar waya tayi kiran aminiyarta. Bugu biyu kuwa ta ɗaga, ko gaisawa basuyi ba ta ce, “Aminiya akwai matsala fa?”.
“Matsala kuma Aminiya! Tami?”.
Tsaf ta zayyane mata komai da Huznah ta sanar mata. Cikin jinjina al'amarin Maman Yaseerah ta ce, “Eh lallai akwai matsala. Dan kuwa Darma family da su Majdiya jini ɗaya ne, auren zuminci ne tsakanin Aliyu Darma da babbar yayarsu Fateema. Amma Aminiya miyyasa tun farko baku sanar min cikakken sunan yaron ba?”.
“Wlhy nima iyakar abinda na faɗa miki shi na sani, itama kuma Huznahr na tabbatar shi kaɗai ɗin ta sani”.
Ajiyar zuciya Maman Yaseerah ta saki, sai kuma ta jinjina kanta da faɗin, “Aminiya wannan maganar tafi ƙarfin waya kizo kawai”.
“Okay in sha ALLAHU cikin satin nan kafin a fara bikin nan zanzo. Ai dole ma na shigo dan na fahimci al'amarin nan shiri yake so na haƙiƙa. Babu ruwana da wata alaƙar yaron da Majdiya, koma ya suke sai Huznah ta mallakesa tunda tana sonshi kuma yana da kuɗi”.
Dariya Maman Yaseerah tayi daga can, sai kuma ta ce, “Ina bayanki wlhy. Ni kin ma tuna min miya faru ne wai naga jiya Alhaji ya dawo da dare, yau kuma da safe naji suna waya da Alhaji Usman akan zai zo kadunar”.
“Wlhy bamu san abinda ke faruwa ba muma. Tashi mukai kawai muka ganshi a gidan. Ina shirin naje na bincika da safe sai kuma ga baƙi anyi ban san daga ina ba, naga dai ya shiga dasu sashen Asiya, yanzu kuma sai ga ƴaƴanta da Huznah”.
“To aiko kiyi azamar bincikawa. Dan al'amarin kamar ba ƙarami bane, ina kuma ƙyautata zaton wannan baƙin sun fito ne daga zuri'ar ita Asiya da yaran nata ne”.
“Iye! Ya akai kika sani?”.
“Ba tabbatarwa nayi ba nima. Amma ga Alhaji nan na shirin tahowa Kaduna ɗin ma, amma lallai akwai abinda ake ɓoye muku”.
“Tab ɗin cakwakiya kenan, a lallai dole ne na bincika, ko dama shiyyasa naga tun jiya Uwar ɗan ke cika da batsewa, ban san miya faɗa mata ba mai gidan, haka itama Asiyan duk tayi sukuku”.
“Humm munafukai, wannan gida naku ai sai ku, na tabbatar akan auren ƴayan nasu ne”.
“Wlhy fa sai mu. Kinga bara naje kozan samesa a sashen nasa zan kiraki daga baya. Amma ki farama Malam bayani akan al'amarin dai kafin na shigo, dan ƙilama zuwa gobe zan shigo kawai in sha ALLAHU”.
“To shike nan hakan ma yayi, sai na jiki”.
Daga haka sukai sallama kowa ya ajiye wayar. Shiru Hajiya Basariyya tayi zuciyarta cike da tambayoyi fal. Sai dai rashin makamar riƙewa yasa ta tattara komai ta ajiye gefe. Fitowa tai ta shiga ɗakin Huznah. Sai ta sameta ta fito wanka tana shafa mai. Zama tai har sai da ta kammala ta shirya ta taimaka mata taci abincin tasha magani ta kwanta sannan ta tashi ta fito. Sashen Daddy ta nufa, amma sai ta samu yana tare da baƙi. Haka dole ta fito bayan ta gaidasu dan ya haɗe fuska ta yanda bataga wajen wargi ba balle samun damar yin halin nata na munafunci..
Shima Daddyn ɗan girgiza kansa kawai yay yana mai kai ɗauke idanunsa daga kallonta. Dan yaji a ransa wani tsegumin ne kawai ya kawota......
____________★
*_TUNA BAYA.._*
Sautin kukanta a maimakon sallama daya karaɗe gidan ne ya saka mahaifiyarta da ƴan uwanta fitowa kusan a lokaci guda. Sai dai babu wanda yay magana sai ido da suka zubama ɗan saurayin yaron dake goye da ita a bayansa da ita kanta mai kukan.
Kallo ɗaya yay musu batare da yayi magana ba ya ƙarasa ga tabarmar dake a jingine jikin bango ya ɗauka ya shimfiɗa. Kafin ya sauketa a hankali tamkar mai tsoron yaddata ƙasa. Ita kam kamar wadda ta ɗosana a kan wuta. Yana direta a saman tabarmar ta wani sake ƙwallarewa da ihun kukan nata. Cikin ɗan nuna rikicewa da sake bayyana damuwarsa akan fuska ƙarara ya juyo gareta. Ƙafar da take ɗangalewa ya riƙe. “Banace kiyi shiru zan rama miki ba. Na rantse miki daga nan gida kawai zan shiga na ɗauka kekena har gidansu sai naje na rama miki. Sannan na masa dukan tsiya”.
“To ni ka tashi kaje”. Ta faɗa cikin taɓara da ƙara ƙarfin ihun kukanta. Bama ta gama rufe bakin ba ya miƙe. Fisha ya kalla matar dake tabbatar da mahaifiyar yarinyar ce saboda kamanninsu. “Ammie dan ALLAH ki saka min ruwan zafi a ruwa yanzu zanje na dawo zan gasa mata ƙafar”.
Cikin sauri Ammie tai ƙoƙarin dakatar da shi ta hanyar kiran sunansa. Sai dai ina har ya fice da mugun hanzari da sassarfa. Kanta ta ɗan dafe tare da maida dubanta ga ƴar budurwar da zata iya kai shekaru goma sha ɗaya. “Amaal! Kinga maza bisa gida kicema Oum-Fadeel karta barsa ya fita”.
“To Ammie!”. Yarinyar ta faɗa cikin hanzari itama tana fisgar hijjab. Dai-dai nan Ammie ta dawo da kallonta kan yarinyar data sake wani ƙwallara uban ƙara tana tittirza ƙafafu da faɗin, “Ni dai kar a hanashi. Sai ya ramomini....”
Tsawa Ammie ta daka mata. Tare da nunata da yatsa. “Idan baki min shiru ba na rantse da ALLAH zan tsantsama miki jiki da magribar nan. Ai dama tunda naga kun jima baku dawo ba nasan kina can ɗaukar maganar da kika saba. Shima Ajwaad ɗin sakarai dake biye miki, kin tashi kin cire uniform ɗin ko sai na ci ƙaniyarki....”
Kuka ta sake fashewa da shi amma bamai sauti ba yanzu dan tana tsoron Ammie. Sai kuma ta nuna ƙafar tana faɗin, “Ammie nafa karye ne a ƙafar...”
“Karyewa?”.
Ɗayar yarinyar da zata kaiwa sa'an saurayin yaron, idan ma ta girmesa kaɗan ne dake tsaye tana kallonta ta faɗa kafin ma mahaifiyar tasu ta amsa.
“Eh wlhy Didi. Ba Najib ɗin gidan Maman Ayna bane ya bugeni da keke mun fito islamiyya. Kuma shine yaƙi tsayawa harda cema Besty wai in ya isa yazo ya rama min”.
Shigowar Amaal da wata ƙyaƙyƙyawar mata mai kama da yaron sosai yasa babu wanda ya tanka mata. Matar ta nufeta tana faɗin, “Subahanallahi Baby na miya faru?”.
Fuska ta taɓe tana satar kallon Ammie, sai kuma ta ɓarke da kuka tana nuna ƙafarta da shigewa jikin matar da takai kusa da ita zaune. “Oum ba Najib bane ya karyani a ƙafata. Kuma na kasa tafiya sai da Besty ya goyoni ma”.
Sosai Oum ta shiga faɗa tana dudduba ƙafar da faɗin in fa har taji ciwon da gaske bazasu yarda ba. Ammie da taga abin nasu bana ƙare bane ta katseta da faɗin, “Aunty ALLAH ki daina biyema iskancin Manaal. Ni yanzu ma sonake nasan baki dai bar Ajwaad ya fita ba ko?”.
Kafin Oum ta bata amsa Amaal ta ce, “Wlhy Ammie ya tafi, inata kiransa ko kallona baiyiba ma ya kwashi keke da gudu”.
“Innalillahi banga ta zama ba”. Ammie ta faɗa tana shiga ɗaki. Babu jimawa sai gata ta fito da hijjabi a hannu. Sai lokacin Oum ta dubeta tana dariya. “Wai ina zaki je?”.
“A binsa zan mana. Sai na bari a cutar min da yaro tunda ke naga kinama ɗaukar abun bada muhimmanci ba, in dai kika biye ta wannan yarinyar wataran sai ta saka har ke an kai station ɗin ƴan sanda” Bata jira amsar Oum ba ta fice abinta.
Fitowar Ammie a gidan dai-dai da isowar Ajwaad a kekensa rigarsa ta islamiyya a yage. Fuskar nan ciɗin-ciɗin ga goshinsa ya ɗan kumburo kaɗan, sai gefen lips ɗin da jini kaɗan shima. Da sauri ta nufesa tana riƙe keken da faɗin, “Innalillahi Ajwaad, yanzu faɗan kaje kayo saboda ALLAH. Anya wataran Manaal bazata saka a maka dukan da zaka kasa tashi ba a anguwar nan?”.
Cikin ɓacin ran da muryarsa dake fita can ƙasa-ƙasa ta kasa ɓoyewa ya ce, “Ammie ciwo fa yaji mata a ƙafa, sai na ƙyalesa yaci bulus? Ko yanzu ban ƙyalesa ba sai na jera sati ina masa duka”.
Ƙasa magana ma Ammie tayi ta zuba masa ido kawai. Har ya shige shi da keken gidan bata iya ta motsa ba. Wannan abota na bata mamaki tsakanin Manaal da Ajwaad. Wata irin abotace mai ban mamaki da tsayawa a zuciya. Basu kasance sa'anni ba dan ya girmeta sosai kusan shekara bakwai ne tsakaninsu ma, sannan basu kasance jinsi ɗaya ba. Amma akwai wata irin shaƙuwa a tsakaninsu da sam babu ita a tsakaninsu da ƴan uwansu na jini ma. Ita abun har tsoratata yake yi.........✍️
_Tofa wasa farin girki, 🥱🥱yanzu zamu koma tushe fa._
✨ZAFAFAN DAI ✨
1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)
Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000
0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070
Kati MTN:- 09032345899
Ƴan NIGER 🇮🇷
1000CF
89825722
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖5️⃣5️⃣
______________
.......Su ɗin ƴan asalin jihar Kebbi ne, a garin Giro dake ƙarƙashin Suru LG. Aiki ne ya kawo mijinta nan cikin Kano kasancewarsa jami'in ɗan sanda. Ba Kanon suka fara zama ba. Sun zauna jihohi kusan uku a tsahon shekarun aikinsa. Sai dai shekara biyu data wuce aka maidosu nan cikin Kano suke zaune a anguwar sharaɗa. Yaransu uku ne duk mata. Shahidah itace ta farko, sai Amaal. Sai Manaal. Lokacin da sukazo Kano shekarar Manaal huɗu kacal, amma sai baƙar fitina a cikinta da shegen surutu. Manaal irin yaran nan ne masu shegen wayon tsiya da ɗan karan surutu kamar an musu ƙauri da kan akku. Ga ɓarnar masifa da jan faɗan tsiya. Sam bata ragama ƴaƴan jama'a dan ko anfi ƙarfinta saita ƙwaci kanta da cizo da bula ƙasa ko jifa. Gata suke mata matuƙa kasancewar itace kamar auta a gidan yanzu. Kowa ya kwaso abunsa zai ce Maanal. Musamman ma mahaifinsu da suke kira Baabu.
Dawowarsu cikin Kano sun samu abubuwan cigaba da dama, ciki harda ƙarin girma da Baabu ya samu, ita kuma ta fara kasuwancin turarruka da gyaran jiki irin na mata. Inda suke sabon wajene da aketa gine-gine, dan ko gidan dake a jikin nasu ma ana kan gina shi ne ba'a kammala ba. Sai dai an kusa kammala aikin. Hakan yasa kusan kullum zakaga mai gidan yazo da yaransa maza uku musamman ma weekend. Jefi-jefi sukan ɗan gaisa da Baabu idan anyi sa'a yana gida ko ya dawo wajen aiki. A haka ranar wata asabar yana gida suka tashi da shirin yin alala da yace yana buƙatar ci. Ammie ta kammala gyara wake ita da Shahidah da zata kai markaɗe. Sai kawai Maanal ta sanya rigima itama zataje. Cikin haushi Shahidah ta ce, “Dama kin bar damun kanki dan babu inda zanje dake. Haka kawai muje kita jibgar yaran mutane a gidan markaɗen kamar ranar da kika fasama ƴar mai markaɗen kai”.
Ihu Maanal ta sake ƙwallarawa tare da zubewa ƙasa tana burgima akan ita wlhy sai taje fa. Dai-dai nan Ammie ta fito da bulala da nufin tsula mata amma sai Baabu ya hana ta hanyar amshe bulalar ya ɗaga Maanal daga ƙasan. Daga haka ya fita da ita a gidan yana lallashinta. A dai-dai lokacin motar makwafcin nan nasa ta iso anguwar. Baabu bai wani maida hankalinsa ba dan baima san shi bane kasancewar bawai ya wani riƙe motar tasa bane. Sai da yay parking a gaban gidan nasa ya fito tare da matasan samarin ƴaƴansa uku sannan Baabu ya maida hankalinsa kansa. Sun gaisa cikin mutunta juna, yayinda suma yaran suka gaida Baabu da girmamawa. Ya amsa musu da kulawa yana mai shafa kansu, yayinda shima babansu yakema Maanal wasa.
“Ƴan samari yaya sunanku?”.
Cewar Baabu yana shafa kan ƙaramin su. Babban ne ya bashi amsa da. “Ni Fadeel. Wannan Fawzan. Sai Auta Ajwaad.”
“Masha ALLAH, ALLAH ya albarkaci rayuwarku manyan gobe.”.
A tare suka amsa da Amin. Yayinda mahaifinsu keta faman murmushi saboda surutun da Maanal ke zuba masa. Sai kuma can ta kalla Ajwaad dake ta faman cin chocolate ɗinsa, cikin ɗan tura baki ta ce, “Kai yaron nan bazaka tsammin alawanka bane. Inata haɗiyan yawu amma sai sha kakeyi rowa haramun dai”.
Ba ƙaramin dariya ta basu ba. Banda Ajwaad ɗan kimanin shekaru goma sha ɗaya daya wani yamutsa fuska ya harareta ya ɗauke kansa. Sai Baabu da ya ɗan harareta shima. Amma ita ko'a jikinta ta maida kallonta ga Babansu ta na sake faɗin, “Abbansu kace masa ya tsammin raina ya biya”.
“Kinga manta da shi Babyna. Muje na baki ina da ita da yawa. Daga yau kuma kema ni Abbanki ne ba nasu su kaɗai ba.”
Cike da murna tace, “Eh”.
Gaba yay da ita zuwa motarsa. Ya fiddo chocolate uku ya bata biyu a hannu, tare da ɓare ɗaya ya sake miƙa mata. Cike da jin daɗi ta amsa. Tare da juyawa ta murguɗama Ajwaad baki da faɗin, “Mai rowa ɗan wuta. Nima kuma ga nawa”.
Harararta nan ma yayi. Yayinda su Fawzan sukayi dariya. Shiko Baabu duk kunya ta ishesa. Ƙarfin halin Maanal da banne a rayuwa. Shegen surutunta da wayonta da suka girmi shekarunta na tada masa da hankali. Duk inda ake neman fitinannen mutum aka samu Maanal an rufe littafi kawai. Sai dai yana mata fatan idan ta ƙara girma ta