AJIYA A DUHU BOOK1 BY BILLYN ABDUL

Author :  Billyn Abdul Category :  Romance

Chapter   33 / 77

96K to 99K   out of 230.9K words

biyun daya rage shi da Nazeefa. Gyaran murya yay da gyara zamansa. Hakan yasa Yazeed ɗagowa ya ɗan kallesa.
        “Yazeed kasan dai ina bayanka nima ɗari bisa ɗari akan zancenka da Maanal. Sai dai ina son kamar yanda su Baba Kalla suka faɗa wannan karon naje da kaina da baba nema maka aurenta ga mahaifinta. Hakan shine zai bada salama game da tujarar mahaifiyarka akan al'amarin”.
     “Daddy nima na yarda da hakan, amma dan ALLAH ina sake neman alfarmar haɗewar gaba ɗaya. Nasan ko'a cikin satin nan zaku iya zuwa ga mahaifin nata, idan kuma ka amince min ni saina fara zuwa na ganshi”.
    Ɗan jimmm Daddy yayi, sai kuma ya shiga jinjina kansa. “Shike nan na yarda da zancen naka in sha ALLAHU za'a haɗe bikin nan da sati biyun, zan samu Baba da batun shima sai mu saka ranar zuwa muga mahaifin nata, kai ka tsahirta sai bayan mun dawo ɗin. Kadai je ka cigaba da shirinka na zama angon mata biyu a rana ɗaya”.
      Ƙasa Yazeed yay da idanunsa wani murmushi na suɓuce masa. Yayinda zuciyarsa ke wani irin washewa da farin ciki mara misaltawa. Ji yake kamar an masa gafarar zunubansa. Yana fitowa ya shiga neman layin Maanal dan yay mata albishir, sai dai bata shiga ba. Duk da yasan yanzu tana office kasa haƙuri yayi ya shiga neman Shahidah. Bayan sun gaisa yake tambayarta Maanal fa. Cikin girmamawa ta sanar masa har yau ba'a dawo mata da wayarta data samu matsala ba ne, amma tana ƙyautata zaton yau za'a kawo mata, sai dai idan ta tashi zata haɗasu.....

___________★

       Shiru kawai Ammie tai tana kallo Daddy dake mata bayanin sabon hukuncin daya sake yankewa akan dawo da zancen bikin Maanal da Yazeed anan da sati uku. Za'a haɗe ɗaurin auren kawai idan ma bikin Maanal ɗin ne za'a ɗaga nan da zuwa ko wata ɗaya ne idan ita bata shirya ba to. Sai kuma batun zuwa ga dangin mahaifinta kamar yanda sukai alƙawari tun farko. A yanzu haka ma yana shirin zuwa su tattauna da baba ne. Ya sanar mata ne koda sun gama yanke hukunci shi da baban basai sannan taji ba.
         Zuciyar Ammie kaikawo kawai take a cikin ƙirjinta, sai dai kamar yanda ta saba dannewa yanzun ma saita danne ta amsa masa da girmamawa tare da jera addu'ar fatan alkairi. Wannan halayyar nata ke ƙara masa jin sonta da ƙaunarta. Bayan ya wuce hawaye cike da idanunta tayi kiran Nene, ko gaisawa basuyi ba ta sanya mata kuka. Sosai hankalin Nenen ya tashi, ta shiga tambayarta abinda ke faruwa a rikice. Sosai Ammie tayi kuka kafin ta zayyanema Nene komai. Itama hankalin nata tashi yay, harma taji ta gagara furta komai..

___________★

       “Aunty Babba nifa ina son ku haɗu ke da Aunty Majdiya da Aunty Khaleesat kuyi magana da Baffah akan batun nan. ina so a cikin watan nan iyaye suyi magana, kuma wata biyu kawai nake so a saka, itama Maanal yau zanyi magana da ita”.
        Baki Oum ta buɗe kamar a ɗan firgice zata bama RK amsa idanunta suka sauka akan AA dake kokarin shigowa, sai dai furucin RK ya sashi tsayawa cak shima..........✍️


_Wannan fa shine cakwakiya, tako ina kowa ya zaburo. Manaal akwai white blood kam🤣. Dangin AA wai mike damun Yayanku ne?🥱🏃_






✨ZAFAFAN DAI ✨

1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)


Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000

0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070

Kati MTN:- 09032345899

Ƴan NIGER 🇮🇷
1000CF
89825722
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_💞AJIYA A DUHU....💞_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_


🅿️➖4️⃣4️⃣


______________


.......Kallonsa kawai Oum take yi zuciyarta na motsawa da bugawa da sauri-sauri, yayinda shima ya zuba mata gajiyayyun idanunsa da suka sake kaɗewa. A hankali ya ɗaga ƙafarsa zai juya ya fita ta kira sunansa a hankali.
       “Ajwaad!”.
  Cak ya tsaya batare daya juyo ba. Yayinda RK da bai lura da shigowar AA ɗin ba ya juya shima yana kallonsa. Cikin rashin fahimtar abinda ke faruwa ya saki murmushi da faɗin, “Ni dai ban more ɗa ba. Malam dawo bafa wata magana bace daban kaima ayi dakai batun son zuwa a nema min auren ƙanwarka Maanal mukeyi kawai”.
     Da wani irin ƙarfi AA ya rumtse idanunsa jikinsa na wata irin tsuma. Da sassarfa ya nufi ƙofa murya a shaƙe ya furta, “Oum na ɗakko su Mamy” daga haka yay ficewarsa.
      Da mamaki RK ya dubi Oum shima, “Aunty mike damun ɗanki?”.
Murmushin yake Oum tayi kawai. Zuciyarta na ƙara raunana da mata nauyi. Cikin son danne komai ta ce, “Maybe aiki ne ko kuma an kunnosa daga waje. Kaga ka bari zamu tattauna anjima su Aban sun iso”....


___________★


       Kamar yanda Sen Bukar ya faɗa zuwa dare ya sake sabon zama da Rabilu. Sun sake tattaunawa sosai tare da tsaida ranar zuwa Giro domin ganawa da mahaifin Maanal. Yayinda tun a ranar ya sanarma uwargidansa shifa zai ƙara aure. Dan yau a gidanta yake. Kamar yanda ta saba cikin nuna rashin damuwa tai masa addu'a da fatan alheri. Sai da ta fito daga ɗakin nasa ta koma nata taci kuka. Ita kaɗai tasan yanda take matuƙar takaicin aure-auren nan na mijinta. Dan ita macece mai tsananin kishi. Shiyyasa a dukansu daya auro kowacce jinta take a sabuwar kishiya. A gareta bata yarda da zancen hausawa da kance kishiya ta biyu ita kaɗai ce kishiyar uwargida ba. Ita duk kishiya sunanta kishiya a wajenta. Sai dai irin matan nan ne ita masu ƙullata da shanye abu a cikinsu bazaka taɓa jin sun furta da baki ba. Shiyyasa ake mata kallon mai haƙuri. Amma sam ba haka bane ba, domin kuwa tana nan tana tara abubuwan a rai suna mata nauyi...
      Shiko Sen.. Bukar ko'a kwalar rigarsa, dan tun a daren yama gama tsara komai. A gefe kuma ya saka babban yaronsa Oler yo shopping na garari zuwa gobe domin yin tsaraba kaikace ganin danginsa zaije ƙauye ba neman iznin neman auren ba......

    _________

          Tunda ya baro sashen Oum kulle kansa yay a bedroom ɗinsa. Wani irin ciwo kansa ke masa, ga sanyi na ratsa masa ɓargon jiki da ƙashi, bai ko iya cire takalman ƙafarsa ba ya faɗa saman gado tare da jan duvet ya ƙudundune kansa. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa zazzaɓi ya rufesa gaba ɗaya. _(Na tsaneka, wlhy na tsaneka Ajwaad. Bana son ganin ko fuskarka, da nasan ƙaddara zata sake haɗamu a duniyar nan dana roƙa ALLAH mutuwata kafin hakan. Na cigaba da yin aikin nan ne dan kawai baka isa hanani yin abinda raina keso ba a duniyata a duk inda naso hakan koda kuwa wajen ya kasance mallakinka ne.....”)_ wani irin sara masa kan nasa yayi sakamakon kalamanta da suke maimaita kansu a cikin kunnensa tamkar yanzu ne take ambatosu, ko a ɗazun ma dakewa kawai yake yi a gabanta. Ji yake tamkar yayta fasa ihu, ihu irin wanda sai ya janyo girgizar ƙasar da kaf gidajen duniya zasu narke cikin ƙasa. Sai dai ba zaiyi hakan ba, sai ma ambaton ALLAH da ya dingayi a zuciyarsa...
      Dai-dai nan Oum da hankalinta ya kasa kwanciya ta iso sashen nasa. Dan har ta nufi sashen mahaifinsu ta fasa tayo nan. Ganin babu shi a main falo yasata haurawa sama da sassarfa. Nan ma babu kowa komai ma a kashe yake tamkar ƙasa. Bedroom ɗinsa ta nufa, tai nocking da kiran sunansa amma shiru. Handle ɗin ta kama zata buɗe dan zuciyarta na sake tabbatar mata babu lafiya amma sai taji gam. Sosai hankalinta ya sake tashi ta shiga kiran sunansa cikin damuwa da lallashi. Amma fin mintuna biyar baida alamar amsawa. Hawaye suka fara ziraro mata cikin rawar murya ta ce, “Haba sweetheart sokake na maka kuka. Ka buɗe naga halin da kake a ciki Please Autan Oum”.
    Nan ɗin ma babu alamar motsinsa, hankalinta ne ya sake tashi, cikin sassarfa ta juya ta fita. Sashen Abah ta nufa, sallama kawai tayi batare da jiran amsa ba ta danna kai cikin bedroom ɗinsa. Dai-dai ya fito a wanka, batare da ya kalleta ba cikin barkwancinsa da Fawzan ya gada ya ce, “Ai ni da na cika fam saura kaɗan na fashe ganin matar gidan yau bata ɗokin dawowata kamar yanda shima ɗanta baiyi.....”
       Jin tayi shiru sai ma kamar tana kuka ya sashi fasa nufar mirror da yay niyya ya juyo yana kallonta. Tsamm yayi sai kuma ya tako a hankali zuwa inda take cike da nutsuwarsa da cikar kamala. “Fateema miya faru?”. Ya tambaya hankali tashe. Idanunta dake zirar da hawaye ta zuba masa. Da ƙyar ta iya motsa lips ɗinta ta furta, “Ajwaad. Ya rufe kansa a ɗaki nayi kiran duniya bai amsa ba. Ina jin tsoro, tsoro nake ji Zaki na, kada yanayinsa na bayane ke son dawowa”.
     Ɗan lumshe idanu Abah yay ya sake buɗewa a kanta (Sak ɗabi'ar AA da alama a wajensa ya gada rufe ido da buɗewa yayin magana😂👌🏃). Hannunsa yasa ya riƙo nata, cikin yanayin tashin hankalin shima ya ce, “Oh kenan akwai abinda ke damunsa? Dan a haka yaje ɗakkomu airport fuska kicin-kicin, daga gaisuwa ko bai sake kulamu ba har muka shigo gidan nan. Wani abu ya faru ne?”.
        “Ni dai a sani na babu abinda ya faru a yau ɗin, duk da dai satittikan nan gaba ɗaya gashi nan dai tunda ya tashi daga zazzaɓin nan na gab da tafiyarku, yau kuma daga office ya wuce ɗaukanku dan da Fawzan ne zai je sai ya kirani akan akwai meeting na gaggawa da zai shiga dan ALLAH nama Auta magana yaje ɗaukanku ko Babban yaya. Shi kuma Fadeel ya tara aiki a office saboda zuwa Kanon nan da yay shiyyasa na turama Autan text akan shi yaje, ya kuma kirani a waya babu wani damuwa a tare da shi yace min zaije ɗin dan bashi da wani abu mai muhimmanci a lokacin, sai kuma gashi ya dawo yanzu a birkice.”
      Cikin furzar da iska mai nauyi Dad ya ce, “It's okay ina zuwa.” closet ɗinsa ya nufa ya saka kaya tare da buɗe wata loka ya dudduba keys, ɗakko na sashen AA yayi yazo ya kama hannunta suka fito. Suna ƙoƙarin shiga sashen motar Fadeel da kowa ke kira babban Yaya a gidan ta shigo. Ganin yanda suka nufi sashen Auta kamar hankali a tashe ya sashi fitowa da sauri shima yabi bayansu ko rufe motar ma bai gama yi ba. Matarsa data fito daga flat ɗinsu domin tarbarsa ganin inda ya nufa ta ɓata fuska da binsa da harara, har zata juya a fusace sai kuma ta fasa itama ta nufi sashen AA ɗin dan son ganin mi mijin nata kema gudun zuwa yi sashen ƙanin nasa mai shegen girman kai.
     Lokacin da suka iso su biyun Abah nata ƙoƙarin gwada key a ƙofar bedroom ɗin AA ɗin, yayinda Oum ke duba sauran bedrooms ɗin da ɗazun rikicewa ta mantar da ita dubawa. Dama bedrooms uku ne a saman, ƙasa ma uku. Ɗaya a main falo biyu a ɗayan falon.
      “Abah lafiya kuwa?”.
  Fadeel daya iso ya faɗa a rikice. Batare da Abah ya dubesa ba ya amsa masa da, “Ban san mike faruwa ba nima Fadeel. Oum ɗinku ce tazo hankali tashe tana sanar min Ajwaad ya kulle kansa a ɗaki”.
      Kafin Babban yaya ya samu damar cewa wani abu ƙofar ya buɗe. Su duka afkawa sukai ciki har Oum da matar babban yaya data iso yanzun nan. Aiko tuni hankalinsu ya sake tashi dan ganinsa a bargo, yayinda tuni Oum da babban yaya sun haura saman katafaren gadon nasa dake a dunƙule kamar zero. Oum ce ta yaye bargon dan har fuskarsa ya rufe, hucin zafin zazzaɓinsa ne ya bugeta, sai kuma rawar sanyin da yake faman yi. Cikin fashewa da kuka Oum ta kamo hannunsa ta damƙe cikin nata tana kiran sunansa......

      ________★

      Kusan zamu iya cewa a position ɗaya AA da Maanal suke a ciki. Dan itama bama ta san a yanayin data iso gidan ba. Sai maigadi ne ya biya taxi drivern daya kawota. Itako tuni ta shige ciki tana layi saboda nauyin da ƙirjinta yay mata har numfashinta na seizing. Batama ko ƙarasa shiga cikin ainahin falon ba ta zube a ƙofa tana ƙoƙarin kiran sunan Shahidah sai dai muryarta sam bata fita. ALLAH ne ya taimaka Linda ta fito dan tana ƙoƙarin jera abincin su Barrah a d/table kasancewar suna gab da dawowa daga school. Idanu ta zaro tare da dangwarar da abinda ta ɗakko ɗin ta nufi Maanal da gudu. Ganin numfashinta na neman barin gangar jikin ta yasa Linda kwara ihu. Ai a guje baba magajiya ta fito daga kitchen tana tambayar Linda mike faruwa?. Ganin Maanal dake kakarin mutuwa yasa itama ta fasa ƙarar. Sai kuma ta runtuma waje a guje tana kiran maigadi. Cikin sa'a ta samesa tare da drivern yara da yazo ɗaukar mota zai tafi ɗakkosu. A guje suka koma ciki su ukun, Linda da Baba magajiya suka cicciɓi Maanal suka fito, a mota aka sakata, baba magajiya ta shiga itama driver yaja suka fice aka bar maigadi da Linda dan bazai yiwu subar gidan babu kowa ba kuma.
        Maigadi ne ya tunatar da Linda cewar ya kamata ta kira Hajiya ta sanar mata. Sai yanzu itama ta farga da haka. Lokacin da ta kira Shahidah tana tsaka da aiki, amma haka ta wancakalar da komai cikin tashin hankali ta fice zuwa asibiti bayan ta kira RK. Cikin tashin hankali ya sanar mata isowar su Maanal ɗin a yanzu haka. Kana jin muryarsa kasan shima ya gama gigicewa, sai Shahidah ta ƙara ruɗewa itama.

     ★ A wannan karon ma dai ansha matuƙar wahala kafin ceto numfashin Maanal, sai dai sam babu aman jini idan ka cire wanda ya ɗan ziraro mata ta hanci kamar haɓo. Shima kuma basuyi wahala wajen tsaidashi ba. Su Dr Ranjet basu samu nitsuwa ba sai bayan isha'i, dama shi RK wannan karon ma kasa komai yayi bakamar wancan karon da akai komai da shi ba. Sai dai yana a bakin ƙofar tare da Shahidah da mijinta da shima ya iso suna zaman jiran tsammani. Fitowar su Dr Ranjet ya saka su dukansu miƙewa. RK kamar ba likita ba ya nufesa da sassarfa yana tambayarsa yaya take?. Cike da kulawa Dr Ranjet ya dafa shi yana faɗin, “Calm down doctor, everything is fine”. Kusan su ukun a tare suka sauke ajiyar zuciya mai matuƙar nauyi. Yayinda Dr Ranjet ya sake kwantar musu da hankali.....

__________★

       A ruɗe Oum tacema Babban yaya yay mata kiran Uncle ɗinsu yana sashenta. Fita yay kuwa da sauri, sai dai yana fitowa motar RK na fita a gidan da gudu. Dan dai-dai ya nufo sashen AA da nufin jin damuwarsa saboda tunaninsa Oum na wajen mijinta kamar yanda tace masa zataje, sai dai yana gab da shiga sashen ne Dr Ranjet yay kiransa cewar gafa Maanal an kawo asibiti. Shine ya juya a guje ya faɗa mota ya fice. Fitar tasa dai-dai da shigowar motar Fawzan shima daga wajen aiki. Matarsa na a gefensa dan itama tana fita aikin, motarta ta samu matsala ne ta barta a office tai kiransa ya biya ya ɗakkota suka nufo gida. Ganin babban yaya ya sasu fitowa da sauri Fawzan na tambayar ko lafiya yaga Uncle Rafeeq ya fita a guje?.
         “I don't know why! Na fito kiransa ne nima fa”.
     “A da alama gaskiya babu lafiya, dan kamarma waya yake hankali tashe. Maybe asibitine suka kirashi kasan Uncle da patient ɗin nan nashi. Amma lafiya kuwa?”.
      “Auta ne babu lafiya”.
   Ai Fawzan ma bai samu damar sake cewa komai ba suka nufi sashen AA su duka ukun. Sai dai Babban Yaya na ƙoƙarin kiran layin family doctor ɗinsu a waya da shima ke aiki a KK HOSPITAL ɗin. Kafin doctor ya iso su duka sun rufu a kansa hankalinsu duk a tashe. Kallo ɗaya zakaima wannan taron kasan AA ɗin ɗan gatan dangi ne. Dan amaryar Abah ce kawai babu a wajen. Sai da matar babban yaya ta ɗaga waya tai kiranta sannan sai gata ta iso. Kusan tare suka shigo da doctor. Itama dai macece ƙyaƙyƙyawa, tana da ɗan jiki na ƙiba dan har tafi Oum ma. Sai dai Oum ta fita tsayi da haske dan ita fara ce kamar yanda Abah ke fari tas. Kai hasalima suna kama sosai da Abah ɗin tabbacin auren zuminci ne a tsakaninsu. Hakama duk yaran kama suke dasu, idan ka cire AA da yake da duhun fata sai dai kamanin fuskar Oum da Abah ɗin na tare da shi shima.
       Duk fitowa sukai aka bar Oum da Doctor yana duba shi. Duk da cikin faɗa yake mitar shi abarsa kar doctor ɗin ya taɓasa. A barshi haka baya buƙatar kowane magani. Hawaye Oum take tana ƙoƙarin tausarsa da shafa lallausar sumarsa daya tara take cin kuɗaɗe. Yayinda idanunta ke zubar da hawayen tausayin yaron nata dan gaba ɗaya yanayinsa ya nuna alamomin tashin ciwonsa. Sam bata fatan hakan, bata son abinda ya shuɗe suke murna ya dawo. Sun azabtu matuƙar azabtuwa da halin da AA ya shiga a shekarun baya. Da ƙyar da addu'oi abubuwa suka sassauta. Sai tabon dake zuciyarsa da sun san har ya koma ga ALLAH bazai warke ba kamar yanda suma nasun yake zaune daram. Sai kuma gashi ƙaddara na neman sabunta abubuwa cike da ban al'ajabi da mamaki a duka ɓangarorin biyu.........✍️






✨ZAFAFAN DAI ✨

1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)


Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000

0022419171
Access

33 / 77