AJIYA A DUHU BOOK1 BY BILLYN ABDUL

Author :  Billyn Abdul Category :  Romance

Chapter   32 / 77

93K to 96K   out of 230.9K words

ɗauka, nacan sama ta zubama ido sai dai hannunta bazai kai ba. Ta gwada ɗauka da ɗiɗɗishe amma duk tsahonta hannunta bazai kai ba. Juyawa tai tana ɗan kallon office ɗin alamar neman abin takawa, sai ko idonta ya sauka akan wani ɗan glass table da aka ɗaura ƙyaƙyƙyawan flowers a samansa. Shiko ta nufa ta sauke flowers base ɗin ta ɗakkosa gaban fright ɗin ta ajiye. Da kallon mamaki kawai ya bita, sai da ta ɗakko yaga da gaske fright ɗin ta nufa ya ɗan waro oily luluu ayes ɗinsa dake cikin gilashi.
     Itako hajjajun babu ko ɗar ta taka ta haye samansa ta shiga jido kalolin lemukan tana tarawa a ɗayan hannunta. Ba ita zai rainama hankali ba. Bari ta kai masa duk kalolin taga iyakar rainin wayonsa. Tana gamawa ta juyo da nufin sauka sai kawai tai wani irin yin baya sakamakon kasancewarsa tsaye a bayanta hannayensa duk a cikin aljihun ya wani zuba mata mayatattun idanunsa kawai. Kaɗan ya rage ta faɗi, da ƙyar ta iya daidaita tsaiwarta tana tura baki batare data cigaba da iya kallonsa ba. Shi kam nasa idanun ƙyam a kanta ko ƙyaftawa bayayi. Kasa jurewa kallon nasa tayi, kasancewar ta a saman table tsahonsu ya dai-daita a yanzu harma ta ɗan zartashi kaɗan. Tun tana jin zata iya daurewa har jikinta ya fara rawa. Ga sanyin fright ɗin da bata rufeba na busota, ta gaba kuma ya tareta tako ina dan tsaye yake gab da ita sosai. Ga kuma drinks data tara a hannu suma sanyinsu na shigarta. Wani irin cikowa idanunta sukai da ƙwalla, cike da sarewa ta saki drinks ɗin suka tarwatse a ƙasa har wasu na faɗa masa a kan ƙafa amma bai motsa ba.
       Zarrrr hawaye suka fara gudu a ƙyaƙyƙyawar fuskar Maanal. Lips dinta na wani irin motsi na son yin magana amma kuma ta kasa. Karan farko ya ɗan lumshe gajiyayyun idanun nasa tare da taɓe baki kaɗan. Sai kuma ya kai hannu a hankali ya rufe fright ɗin, yaja jikinsa yabar wajen batare da yace mata komai ba. Sauka tayi itama jikinta na cigaba da rawa zuciyarta na mata wani irin zafafa mata jin zafisa. Ko kallon drinks ɗin data zubar batai ba ta nufi hanyar ƙofa tana share hawayenta. Sai dai koda taja handle ɗin domin buɗewa sai ta jita bam a rufe. Tsaye kawai tai jikinta na sake cigaba da rawa. Hawayenta na ƙara ƙarfin gudu. Ta ƙara kai hannu taja amma still dai. Ai bama tasan ta wani irin juyowa inda yake ba, sai kawai ganinta tai a gabansa.
       Cikin matuƙar ƙunar zuciya da raɗaɗi ta ce, “Mikake buƙata da ni ne wai? What is your business with me? ”.
    Idan office ɗin ya motsa to shima ya motsa. Nunama yasan da ita a gabansa baiyi ba, karatunsa kawai yake yi. Hannu tasa ta fisgi book ɗin tai wurgi da shi saman kujera, cikin matuƙar tsiwa da komawa ainahin Maanal data mutu (😂injita) ta sake matsosa a kausashe, cikin ƴar tsawa ta furta “Ajwaad!! Nace mi kake buƙata da ni? Kana min abubuwa ina ɗauke kai amma na kula kai ka kasa fahimtar karatun kurma. Dole ne sai ka kasance in to my life ne? Kasan dai ni ba shasha bace da zaka taka yanda kake so kamar yanda ka iya ko, kodan kaga nazo ina aiki ne a ƙarƙashin alfarmarka kake ɗaukata a ban san mi nake yi ba? To daga yau nabar aikin, na bari tunda dama ra'ayina ya sani jin zanyi bawai rasa tallafin rayuwane ba ko talaucin da da ake kallonmu a ciki....”
    A karo na farko da tun isowarta wajen ya ɗago mayatattun idanunsa dake cikin gilashi, gently hankali kwance ya zuba mata su. Sake hayayyaƙo masa tai har tana nunashi da ɗan yatsarta manuniya tamkar zata tsokale masa ido. Idanunsa da yake ɗan ƙyaƙyƙyaftawa ya ɗan ja kamar zai lumshe sai kuma ya sake buɗesu warrr a kanta. Cigaba take da nunasa tana masifarta har baya ma fahimtar abinda take faɗa, tsabar yanda ta birkice tuni veil ɗinta datai rolling ya warware hakama ɗan kwalin ya zame dogon gashinta baƙi siɗik dake ɗaure a tsakkiya cikin ƙyaƙyƙyawan ribbon ya bayyana sai lilo yake. Sosai ya maida idanunsa ya zuba akan gashin yana masa wani irin kallo.
      Ina Maanal bata san yana yi ba, masifarta kawai take tana kuka. “Na tsaneka, wlhy na tsaneka Ajwaad. Bana son ganin ko fuskarka, da nasan ƙaddara zata sake haɗamu a duniyar nan dana roƙa ALLAH mutuwata kafin hakan. Na cigaba da yin aikin nan ne dan kawai baka isa hanani yin abinda raina keso ba a duniyata a duk inda naso hakan koda kuwa wajen mallakinka ne......”
      Duk da wani irin saukar aradu da kalamanta ke masa a cikin kunne a bazata, matuƙar bazata taji tattausan hannunsa ya sauka akan yatsar ta dake neman cokale masa ido. Fisgar hannunta tayi tana sake birkice masa. Sai dai riƙon da yayma yatsar bana wasan yara bane ba. Dan fisga ɗaya ya mata bama wani da ƙarfi ba sai gata a gabansa a zube. Biyota yay da kallo har lokacin ɗan yatsar nata dai na riƙe a hannunsa.
       “Wlhy koka sakeni kona maka ihu”.
    Karo na farko ya saki wani ɗan iskan murmushi yana ɗan ɗage girarsa ɗaya, sai kuma ya sauke ƙafarsa duka ya ajiye a ƙasan carpet ɗin da take zaune tare da duƙowa sosai kusa da ita gab har tana jin numfashinsa da ƙarfin turarensa sosai a cikin hancinta. Jikinta taso ja baya sai dai sam yaƙi bata damar haka. Cikin sake lumshe idanu da buɗesu a lokaci guda ya motsa laɓɓansa ƙasa-ƙasa ya furta, “Bismillah yi, ba ihu ba? Maza kiyi, ai bana yau ne farko ba daman”.
Cusa kanta tayi cikin ƙafafunta ta dunƙule a waje ɗaya tana mai fashewa da kuka. Ga jikinta na matuƙar rawa. Tabbas komai dawo mata yake. Ta ƙarfin tsiya da tsiya-tsiya brain dinta da zuciyarta keson tilastata tuna baya. Bayan data jima da shafewa a tarihin rayuwarta. Bayan da bata fatan koda wata alama ta tuna shi, bayan da take kallo tamkar RAYUWA A BAYAN MUTUWA. Bayan data jima da tattarashi ta tura can bayan bayanta ta yanda bazata sake tunawaba har gaban abada. Miyyasa yake son tilastata ne? Miyyasa bazai mata adalci bane? miyasa yake son sake cuta mata da wannan DAFIN da yay ajalin ainahin Maanal. Miyyasa bazai gane komai ya canja bane, canjawa irin wadda ke shafe ƙarnuka da zamanoni tamkar ba'a yisu ba. Kaicon samuwar wannan aiki nata, kaicon amincewarta da yinsa. Ita da kanta ji take ma ta tsani kanta da kanta a wannan gaɓar.........✍️

     _Hummm ni Balki, wai shin...🤔 To bara dai nayi shiru kada ace na cika takale-takale 🥱😌😩🏃_



✨ZAFAFAN DAI ✨

1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)


Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000

0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070

Kati MTN:- 09032345899

Ƴan NIGER 🇮🇷
1000CF
89825722
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_💞AJIYA A DUHU....💞_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_


🅿️➖4️⃣3️⃣


______________


........Shima da gaba ɗaya kansa ke juya masa, al'amura masu nauyi da suke lulluɓe a zuciyarsa na sake zaburowa, a hankali ya saki mata yatsan yana rumtse idanunsa da ƙarfi. Wani irin ratsa zuciyarsa da ɓargo kukan nata yake yi. Sai dai bazaka taɓa fahimtar hakan a fuskarsa ba idan ka cire idanunsa da sukai matuƙar kaɗawa. Tawani fannin kuma zai iya cewa kukan yake so tayi, dan zai rage mata nauyin zuciya dana zafinsa da yasan take ji. Fin mintuna biyar suna a haka kafin ya miƙe a wajen, veil ɗinta dake yashe a ƙasa ya ɗauka, ƙamshinsa na sake ratsa hancinsa, kanta ya ɗan rankwafo ya yafa mata veil ɗin a saman kanta batare da yace komai ba ya wuce ainahin office chair ɗinsa, batare daya zauna ba ya ciri ƙaramar pepper yay ɗan rubutu, sai kuma ya ɗauka shopping bag ƙarama dake a saman desk ɗin. Rigar suit ɗinsa dake a hanger ya cire itama tare da tattare wayoyinsa. Gabanta yaje ya ajiye shopping bag ɗin nan da shot note ɗin da yayi batare da yace mata komai ba ya nufi ƙofa. Sai da ya kai hannu zai danna maɓallin buɗe ƙofar batare daya jiyo ba ya furta, “Ki tabbatar kin shiga restroom kin gyara fuskarki”. Daga haka yay ficewarsa cike da takunsa na nutsuwa da ƙasaita.
     Da wani irin sauri Huznah dake zaune cikin takaici da damuwa ta miƙe. Hakama AS ɗinsa daya san wannan ba lokacin fitowarsa bane miƙewa yayi. Baiko kalla inda Huznah take ba, sai Assistant ɗin nasa ya kalla. “Zanje airport ɗaukar su Mamy. Take care of everything”.
     “Okay Sir ALLAH ya tsare”.
Kansa kawai ya jinjina masa yay wucewarsa. Har kuma yayi taku uku sai ya tsaya cak jin ana binsa a baya. Ɗan waiwayowa yay tamkar mai jin ciwon wuya ya zuba mata ƙasaitattun idanunsa da gaba ɗaya suka sauya kala da launinsu. Dan farin gilashin fuskarsa bai zam ya ɓoye komai ba daga garesu. Kasa jure kallonsa Huznah tayi, sai ma jikinta dake neman fara rawa. Amma tai ƙoƙarin riƙe kanta da tsiya, sai dai muryarta na ɗan rawa ta ce, “A zahiri bakayi kama da mai wulaƙanta mutane ba, why ni nake neman zama ƙasƙantacciya a yayin zuwa ganinka? Please ka duba ni, ka bani dama muyi magana dan ALLAH”..
         Karo na farko ya lumshe idanun nasa da buɗesu. Hakan tuni ya zame masa ɗabi'a musamman a yayin son yin magana. Cikin cool voice ɗinsa mai fidda ƙaramin amo da kasancewa ƙasa-ƙasa tamkar ba namiji ba ya furta, “Mi kike buƙata?”.
      “Kai! Kai nake buƙata AA. Ina son yin magana da kai Please”.
Lips ɗinsa ya ɗan ciza sai kuma ya janye idanunsa daga kanta. Ƙoƙarin wucewa yay batare daya tanka mata ba yana kallon Designer agogonsa da sai ka gama karaɗewa baka samo sa ba, dan shi duk wani agogon sakawarsa ana masa shi a companynsa kuma shi kaɗai, sai idan wani ne yace yana so ayi irinsa daga nan shi kuma yabar saka Design ɗin sai kuma wani. Da sauri ta bi bayansa suka shige cikin elevator daya buɗe. Anan ɗin ma dubansa tayi da son yin magana sai dai ta gagara sakamakon ganin fuskarsa babu alamun wasa. A haka suka fito tanata ƙoƙarin ganin ta daidaita tafiyarsu. Aiko hakan yaja hankalin ma'aikatansa matuƙa. Dan duk inda suka gitta idanu yuuu akansu. Masu ƙus-ƙus nayi masu jinjina kai nayi. Yayinda zukatan mafi yawansu suka sake yarda da eh lallai da gaske itace boss ɗin nasu zai aura kuwa. Dan abune da basu taɓa gani ba boss da mace kamar haka. Ina dai ka gansu da wata to lallai abokiyar kasuwanci ce, dan shi hatta a cikin family baya kula ƴar kowa, in dai kina sama da shi zai yi respecting ɗinki. Suna gama ficewa sai ƙus-ƙus ɗin ya ƙaru, yayinda wasu suka maida hankalinsu ga hotunan dake akowacce kusurwa ta Company ɗin na mace mai niƙab da hijjab. Wadda da yawansu sun gagara tantance hoto ne ko zane ne. So suke su tantance ko wadda suka fita taren ce. Sai dai sam babu wani alamu ko kamanni daya nuna hakan. Dan baka isa tantance ainahin wacece a hoton ba tako ina....

        Yana fitowa drivern sa dake can wajen securitys suna hira ya miƙe da sauri. Sai dai koda ya iso garesa sai ya miƙa masa hannu murya ƙasa-ƙasa yana faɗin, “Don't worry, give me the key, I want to drive myself”.
      Babu musu driver ya rissina ya miƙa masa key ɗin. Sai kuma ya buɗe masa motar da sauri.
      “Ka sama mata taxi”.
Ya sake faɗa yana ƙoƙarin shiga motar, kallon Huznah driver yayi, sai kuma ya amsa da sauri cike da girmamawa. Huznah kam dake tsaye kamar zata saki kuka kallonsu kawai takeyi, tana ji tana gani a gabanta ya birka motarsa ya fice cike da ƙwarewar iya tuƙi na nutsuwa da cikar kamala....
       Lallai yau taga madarar wulaƙanci da babu ko gauraye a cikinta, wato mutumin nan cikin ruwan sanyi yake tsula maka tsiya babu hayaniya babu hargowa ko yawan magana. Dole ne ta koma Kaduna su sake shiri kam, amma zata fara bari ta haɗu da mahaifiyar tasa dan taga yaya nata takun itama, hakan zai sa susan irin shirin da zasu musu su duka.. da wannan tunanin ta ballama drivern harara ta fice da ƙafarta.....

     ★★★

  Maanal ta jima a wajen tana kuka, sai da ta fara jin zuciyarta na mata nauyi a cikin ƙirjinta kafin ta ɗago kanta da ƙyar, office chair ɗinsa ta zubama ido sosai tamkar shine a wajen, har yanzu hawayen na cigaba da ziraro mata. Tunanin dake neman tasiri a ranta ta ture da ƙarfin tsiya tare da miƙewa ta nufi restroom ɗin kamar yanda ya faɗa, dan itama tasan ko giyar wake tasha bazata fita a haka ba ai. Sosai restroom ɗin ya haɗu, gashi ƙal-ƙal sai ƙamshi yake zubawa kamar ba toilet ba. Ta jima tsaye tana kallon kanta a mirror ɗin bayin tana hawaye kafin ta wanke fuskar tata ta fito bayan ta gogeta da ƙaramin towel fari tas dake a bayin. Harta nufi ƙofa ta koma da baya, shopping bag ɗin daya ajiye a gabanta ta ɗauka kasancewar ganin abinda ya rubuta a takardar daya ajiye a sama, sai kuma ta maida ta ajiye. Nan ma ta juya zata tafi idonta suka sake sauka a novel ɗin nan nasa. Baki ta tura gaba sannan ta ɗauka shi dai ta ficewarta..
      Koda ta fito bata kula kowa ba a wajen ta shiga haɗa ƴan tarkacen kayanta, kallonta kawai su Zaharadeen suke cike da gulma. Sai Yaqub ne daya miƙe tsaye yana kallonta tun shigowarta ya furta, “Sister Maanal are you okay?”.
      Kanta kawai ta jinjina masa batare da dace komai ba. Kafin ya samu damar sake magana ta kwashi kayanta zata wuce. Cikin sauri ya bita yana faɗin, “Ina zaki je?”.
    “Gida”.
Ta bashi amsa a takaice. Cikin tashin hankali ya buɗe baki zai sake magana a fusace ta ce, “Please Yakub! Nace ba komai. Leave me alone”. Daga haka tai gaba abinta fuuuu. Shiru yay kawai yana kallonta, gaba ɗaya fuskarsa ta nuna tsantsar damuwa da tashin hankali. Shin mike faruwa? Mi akai mata? A office na CEO fa aka kirata! Miya faru acan ɗin?”. Rashin mai bashi amsa ya sashi juyawa jiki a sanyaye ya koma ciki. Sai kuma ya sake tadda wani abun takaicin, su Zaharadeen ne suke buɗe babin gulmar Maanal ɗin. Wai maybe ta faɗama CEO tana sonshi ne shine ya koreta a aiki, sai ALLAH ya ƙara suke mata da kiranta mai girman kai da faɗin rai. Takaicinsu ya saka Yakub ko kulasu baiyi ba......
      
    ______________★

      “Alhamdullahi ranka ya daɗe aiki ya kammala. Wannan shine cikakken bayani akan ainahin mahaifinta dama zuri'arta baki ɗaya”. Rabilu ne mai maganar fuskarsa washe da murmushi yana miƙama Sen.. Bukar bayani akan Maanaal daya binciko kamar yanda ya buƙata. Sosai fuskar sa ta washe da murmushi. Dan shi kaɗai yasan yanda yake azabtuwa da so da ƙaunar yarinyar nan data mamaye dukkan illahirin jinin jikinsa. Yanzu haka yau har gaban Mawaad company yasa drivern sa yaje ya faka mota har Maanal ta iso. Fitarta a motar Shahidah da dukkan abinda ya faru a wajen kan idonsa ne. Ji ya dingayi kamar ya sato ta saboda yanda tai matuƙar ƙyawu a cikin kwalliyar ta yau.
       Rabilu ya cigaba da faɗin, “Su ɗin asalin su ƴan jihar Kebbi ne, ƙaramar hukumar suru a wani ƙauye da ake kira giro. Mahaifin nata ɗan sanda ne, dan har ya kai matakin DPO amma yanzu ya ajiye aiki sakamakon doguwar jiyyar da yayi. Ita kuma mahaifiyarta bata tare da shi a yanzu, dan sun rabu shekaru kusan takwas kenan, a yanzu haka tana auren wani Alhaji Usman Chalawa ne anan kaduna, yana riƙe da su kuma tamkar mahaifin nasu koma fiye da shi.”
     Cike da zumuɗi ya furta, “Rabilu kaje wajen Oler ka amshi key ɗin motar ka sabuwa dal, zuwa dare zan nemeka idan na koma gida”.
     Cikin matuƙar washe baki Rabilu ya shiga godiya harda ɗan zamowa daga visitors chair da yake zaune ta office ɗin Sen.. Aifa cike da zumuɗi ya bar office ɗin. Kai tsaye gidan Sen.. Bukar ya nufa domin amsar alƙawarinsa dan yasan baya magana biyu akan alkawari irin wannan daya shafi mata. Zai iya cewa dukan matan alhajin idan ka cire uwargidansa duk shine ya masa bincike akan sauran biyun. Ya kuma taka rawar gani akan samuwar auren fiye da zaton mai zato. Sai dai ya fahimci kamar Senator ɗin yafi sakin kuɗi da ɗoki akan wannan ƴar shilar. To ƴar shila mana. Akan matan Alhaji ai manaal ƴar shila ce. Dan ko jikansa na farko ya girmi Maanal sosai. Aiko ina sha ALLAHU zai yi iya ƙoƙarinsa dan ganin tako ina Alhaji bai samu matsala ba, ya kuma mallaki yarinyar da gaggawa. Dan yasan irin wannan kariɓujin arziƙin da ire-irensa sunta zuwa kenan. Zama kuwa ai ba nashi bane ba....

____________★

         Cike da nutsuwa Daddy ke kallon Yazeed. Yayinda shi kuma kansa ke duƙe a ƙasa rauninsa na sake bayyana akan fuskarsa. Karo na farko Daddy ya ɗan saki murmushi, yayinda tausayin yaron nasa ke ratsa masa zuciya. Ya jima da fahimtar tsananin so da Yazeed kema Maanal, sai dai bai sake tabbatarwa ba sai a ɗan tsakanin nan. Musamman yau da yazo masa da roƙo da magiyar janye batun sai nan da wata biyar ayi aurensa da Manaal. So yake a haɗesa gaba ɗaya anan da sati

32 / 77