Taki Zaman Aure Sirrin Zuciyar Mace by 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Author :  𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 Category :  Romance

Chapter   50 / 72

147K to 150K   out of 215.5K words

bakinciki da na haram, na san Baba kashe ni zai yi idan ya sani, buri na yadda za a zubar da ciki ne ba tare da kowa ya ji ba. Kullum maganar da nake masa kenan kuma saboda haka nake amincewa da shi, shi kuma yana ga jan lokaci saboda biyan bukatarsa. Amman ni ba zan iya cin amanarki ba Noor zuciyata ba haka take ba, ba a mana wannan tarbiyarba, tsorona na lalacewar aurenki ne da na Mama, ba ki tsaya kin saurare ni ba, ban san ya zan miki bayani ba_

Na mike tsaye da sauri a lokacin da nake karanta sakonta na karshe.

_A lokacin da zaki samu sakon nan ki karanta bana gidanki, na bar gidanki Noor, kuma ba gida zan tafi ba, ba zan kaiwa Mama abun kunya ba, ba zan tafi da cikin shege gidan Baba ba, na san zaki fada musu dukan abun da ya faru a lokacin da zaki koma gida ko kuma aka neme ni aka rasa. Dan Allah ki fada musu gaskiya Wallahi ba da son na aikata ba, kaddara ce ta riga fata, zan tafi inda ban san kowa ba kuma kowa be san ni ba, na bar ku Noor ku yafe ni, musamman ke...!_

Na jefar da takardar na nufi dakinta da sauri ina kiranta.

“Hana Hana Hana...”

Na tura sai na samu dakin babu kowa, na fada bandaki nan ma bata nan, na fito da gudu na nufo gate ina tambayar mai gadi ko ya ga fitarta.

“Hana ai tun jiya da dare ta fita, misalin sha daya na dare”

Na fashe da kuka na bude gate din na fita da gudu kamar ance zan ganta. Na yi dama na kalli karshen Titi da babu mutane na juyo na yi hagu nan ma babu alamar sawunta. A gurin na zube na kwarara wani irin ihu da dukan karfina ina kuka har sai da abun da ke cikina na motsa....



Duk wanda ta karanta min littafi bata biya ba na barta da ALLAH. duk wanda ta yi min sharing paid pages na barta da ALLAH.


It's 500
Zenith Bank
Hadiza Abubakar
2451879008

And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660

“Lafiya Hajiya Lafiya?”

Ban kula mai gadin ba na dago da guduna na dawo cikin gidan na nufi jakata na bude na kira number wayarta. Na yi sa'a ta shiga kamin ta amsa har wani jiri nake ganin tsabar bugun da zuciyata yake yi. Ringing tayi ta katse bata daga ba, ina sake kira sai na ji wayar a kashe. Faduwa na yi zaune kan kujerar, ban san abun da zan yi ba, ban san ta ina zan fara nemanta ba. Ban san kowa cikin kawayenta ba. Hana bata da kawaye a garin nan sai yan makaranta kuma ban san waye zan fara bincika ba, ni ban ma san ina makarantarsu yake ba.

Takardar na dauka na saka a jakata na koma dakin na dauko babban akwatina na zuba iya kayan da nake iya gani na rufe na janyo akwati na fito ina kuka. Bana son na kira Mama na fada mata domin bana son su san abun da yake faruwa da Hana, musamman Baba da ba fahimta zai yi ba. Idan kuma na koma me zan fada musu? Miye silar mutuwar aurena? Kuma ina zan ce na bar Hana. Ban amsa tambaya ko daya da mai gadin date din yake min ba. Na mike hanya na fara tafiya ina hawaye har na isa babban titi na tari okada na fada masa tashar da zan hau motar Kano zai kai ni.

Ya charje ni dubu biyu daga unguwar da nake zuwa unguwar da ya kai na hau mota. Na taki sa'a na isar tashar a lokacin da ake neman mutum daya motar Kano ta tashi na mika duka kudin da nake da su na shiga motar na zauna bayan sun karbi information dina. Tafiyar ta min nisa sosai wata kila saboda mota na hau, domin ban tana zuwa ko dawowa a mota ba sai wannan karon, wata kila kuma saboda abubuwan da suka saka ni gaba ne. Dan carjin da ya rage min na siye ruwa da shi su nayi ta sha, har muka isa Kano.

Karfe shida muka sauka garin Kano, domin Tafiyar awa tara ne daga Kano to Lagos a babbar mota. Na fito motar aka cire min akwatina na karba na fara ja zuwa gate din tashar. Napep na shiga na fada masa kasuwar da zai ni, wato kasuwar yan waya.

“Dan Allah ka dan jira ni sako kawai zai karbo”

“Okay amman Karki dade”

“Ba zan dade ba”

Na bar akwatina a ciki na shiga cikin kasuwar a lokacin da wasu suke ta hada hadar tashi saboda yamma ta yi. Wani shagon na nufa na nuna masa wayar hannuna.

“Malam kuna siyen irin wannan wayar?”

Ya kalleni irin duban nan na rashin yarda. Sannan ya karbi wayar ya duba waje da ciki.

“Wayar waye?”

“Tawa ce siyarwa zan yi”

“Saboda me zaki siyar?”

“Ina cikin matsalane ina bukatar kudi”

“Ina receipt da kwalin wayar”

“Suna gida”

“To kije ki dauko waya a hannuna haka ai ta sata ce”

“Wallahi tawa ce, ka duba ciki akwai hotuna na a ciki, kawai ina cikin matsala ne ina bukatar kudi”

Na fada hawaye na jika fuskata. Dayan dake gefensa ya taso ya karbi wayar ya duba.

“Nawa zaki siyar”

“Ni ban san kudinta ba ku siya kawai”

“Iphone 14pro max mu baki 305k kin ga ta dan ji jiki”

Na zaro ido ashe babbar waya nake riko ban sani ba. A zatona wayar ba zata wuce 50k ba idan ma ta yi tsada.

“Ka dai kara, dan Allah matsala ce ta saka zan siyar Wallahi”

Sai ya miko min wayar.

“Ba zan iya siyenta fiye da haka ba, siyen waya haka ma ai it's risk kawai dan na ga kina cikin damuwa ne zan siya, kin ga ma yanzu tashi zamu yi”

“To kawo kudi”

Ya cire min layina ya miko min sannan ya kirgo kudin ya miko min ba tare da na kirga ba na karba ina masa godiya. Na fito da sauri na samu mai napep din nan a inda na bar shi ina shiga ciki ya rufe ni da fada wai na bar shi yana ta jira.

“Yi hakuri”

“Ina zan kaiki?”

“Hotel”

Na fada kai tsaye domin kudirin da ya saka na siyar da wayar kenan domin babu sauran kudi a hannuna.

“Wace hotel”

“Ko wace ma wacce dai mutane ba su cika yawan cikawa ba”

Ya fara lissafa min sunayen hotel yana tambayar wacce za zai kai ni. Zuciyata kuma taya raya me kamata na tafi can ba, gida ya kamata na tafi, amman idan na tafi gida me zan fada.

“Kai ni ko wace ma”

“Okay”

Na share hawaye ina jin bakinciki a zuciyata, yau ga ni a garin Kano amman ba damar tafiya gidanmu. Ina yar'uwata take a wane hali take yanzu? Me ye makomar cikin dake jikinta? Me yasa ban saurareta ba wata kila da bata gudu ba. Ya sauke ni a gaban wata katafariyar hotel mai girma da haske ko'ina.

“Mu shiga ciki ko na sauke ki a nan?”

“Nan ma ya isa”

Na fito na dauko akwaiti na bude jakata na dauko 3k cikin kudin wayar na mika masa, sai ya karba yana min godiya. Na juya na hotel din sai kuma na ji bana ra'ayin shiga ciki. Dan haka na tari wata Napep din na shiga domin aiwatar da kudirina.
A kofar gidan Kareem mai napep din ya sauke ni, na sallame shi na nufi flowers din da suke gefen gidan na daga akwaitina na jefa a ciki sannan na nufi gate din. Na kwankwasa na san by that time yana gida ko hanyar gida, domin muna hanya aka yi sallah Magariba.
Mai gadin ya bude ya leko.

“Mai gidan yana nan?”

Ina magana numfashi daker domin karfina ya gama karewa ga bakina ya bushe, har lokacin kuma ban ji ina sha'awar komai ba duk da kasancewar ina jin yunwa.

“Eh yana nan”

“Dan Allah ka ce mishi yana da bako a waje dan Allah ya fito abu ne mai muhimmanci”

“Wa zan ce masa?”

“Kawai ka fadi haka dai”

“Tohm”

Ya juya ya koma ya rufe gate din. Ni kuma na kai hannuna na dafa ginin ina jin zuciyata kamar zata fashe. Tun a lagos na kudurtawa zuciyata zuwa na fada masa damuwa ba, da na yi nufin na fara sauka hotel ne washe gari na je na same shi a restaurant ko asibitinsa na fada masa, amman burin ceton yar'uwata ya saka na ji kamar idan ta kai gobe zan iya rasa rayuwarta. Na kwashe minti talatin tsaye a gurin sannan ya sake bude gate din.

“Yace a shigo da bakon”

Na cira kafa na shiga cikin gidan na fara takawa sai na hango shi tsaye a entrance yana kallona har na karaso. Ya kalli daga kasa har zuwa sama.

“Noor”

Na kalleshi ba tare da na amsa ba.

“Minene kuma wannan karon?”

“Kareem na san ina damunka ina shiga rayuwarka da yawa, amman dan Allah karka ce min aa na maka alkawari daga wannan ba za sake ba, dan Allah ka taimaka min dan girman Allah”

Na kai kasa ina rokonsa sai kallona yake ya kasa cewa komai. Na nufo shi ne saboda ina jin yana karfi na dukiya wata kila har da hanyar da zai taimaka min.

“Shigo ciki”

Ya juya.

“Matarka za....”

“Bata nan”

Na mike tsaye na bi bayansa na shiga cikin falon sai na zauna a kujera shi ma ya zauna nesa da ni yana kallona.

“Me ya faru?”

Na bude jakata na dauko takardar sakin zan tashi na kai masa sai ya taso ya karba ya zauna a dayar kujerar dake kusa da tawa. Yana gama karanta takardar ya kalleni

“Innalillahi Wa'inna Illaihirraji'un, Saki Noor mi ya faru?”

Na ciro dayar takardar da Hana ta aje min na mika masa ina hawaye. Ya karba ya fara karantawa mikewa yayi tsaye ya girgiza kai ya runtse ido, can kuma ya bude idon ya kalleni.

“Da gaske?”

Na daga mishi kai har sau uku, ya koma ya zauna na dafe kansa.

“Ko da yaushe idan ina cikin damuwa, na kan zo gareka saboda ina samun mafita kuma kana taimaka min, dan Allah ka taimaka min ta dawo, bana son Mama ta sani ko Baba domin idan Baba ya ji zai Fadawa Umma ita kuma zata yada a cikin unguwa, Mama kuma idan ta ji wata kila ba zata iya hakuri zata janyo mutuwar aurenta, bana son daya daga ciki ya faru?”

“Na ji zan taimaka miki amman dole ne iyayenki su sani Noor, me zaki fada musu a mutuwar aurenki? Kuma yanzu kamin a gano yar'uwarki me zaki fada? And idan ma an ganta amman ba a cikin hali mai kyau ba dole za su ji ba zaki iya boye wannan ba, yanzu idan kin tafi gida me zaki fada?”

“Ba gida zan tafi ba Hotel zan zauna, har sai an gane Hana sai mu tafi gida tare, na Fadawa Baba kawai mun yi fada ne ya sake ni”

“Noor yanzu kurciyata tana damunki, matsala irin wannan iyaye kadai suke iya tsayawa mutum, dole ne ki fada musu gaskiya, gidan ba zaki iya Fadawa Baba ba, to ki fadawa Mahaifiyarki, kaddara ce babu wanda ya wuce kaddara”

“Kaddarar ita ce kullum a biye da ni, aure na biyu kenan ina yi babu dadi, gashi yanzu har na janyo Hana ta gudu ta shiga duniya”

Na fada ina kuka. Mikewa yayi tsaye ya haura sama ya bar ni a falon ina ta kuka ni kadai gaba daya ma duniyar ta isheni. Be dade ba ya sauko da waya a kunnensa.

“Yeah let me ask her”

Ya kalleni.

“Ina kika saka ran zata tafi?”

“Ni da ita ba mu san kowa a Lagos ba, ban san inda zata tafi ba, bata da kawaye sai yan karantarsu ban san gurin waye zata tafi ba”

“Wai bata san kowa a lagos ba”

Can kuma na ji ya amsa da

“Okay Thank you”

Ya zauna sannan ya amsa kiran da ya shigo.

“Aaryam na kira baka daga ba”

Ya kalli agogo.

“Okay, daman wani taimako nake so dan Allah, wata yarinya ce ta gudu a Lagos nale son a nemo ta, na san kana da friends yan Lagos sosai maybe you can help”

Ya mike tsaye ya nufi kitchen ya turo kofar, bana jin komai da yake fada har sai da ya gama wayar ya dawo ya zauna.

“Ina wayarki dole sai an tura hotonta”

“Na siyar na siyar da ita yanzu, suka ba ni 305”

“Wayar?”

“Eh”

“Saboda me?”

“Ba ni da kudi ne, kudin sun kare a hawan mota, shi ne na siyar da wayar saboda na yi amfani da kudin, irin wayarka ne”

Ya kalli wayar ya kalleni.

“15 pro max suka baki 305k?”

“Aa taka ta tsufe tawa da shekara daya, tawa 14pro max ce”

Na ciro kudin na zube duka a gurin.

“Wane barayo ya siye wayar?”

“Ba barawo ba ne shago ne”

“Saboda kawai sun ga baki san kan waya ba sai su siye a 305k? Dole sai an nemo hotonta da Yanzu ina layinki yake? Dole sai an nemo hotonta da sunan makaranta su”

Na yi shiru ina tunanin gurin da zamu hotonta domin ban zan tafi gida babu ita ba.

“A dp dinta na whatsapp akwai hotonta kuma sunan makarantar su Victory College Of Health”

“Yanzu ina line ki?”

Na saka hannu jaka na dauko layi na mika masa, sai ya karba ya haura sama sai gashi ya sauko rike da wata wayar touching amman ba iPhone ba. Ya saka line da na bashi ya dade yana taba wayar ban sa me yake dubawa ba kamin ya miko min wayar.

“Saka number ta”

Na karba sakon karta kwane ya rubuta a messager wayar.

“Dan Allah Hana ki dawo, tafiyarki ta haifar min da matsaloli da yawa, na bar Lagos na dawo Kano, amman na kasa tafiya gidanmu saboda ban san me zan fada musu ba, bana son na fadawa kowa matsalarki, na miki alkawari babu wanda zai ji, dan Allah ki dawo na yafe miki kuma na fahimce a yanzu, Abdull ya sake ni, Hana kuma kin sani ina da ciki zan iya rayuwa zan iya mutuwa, idan baki dawo gida ba, ni ma zan koma ba, zan tafi na bar garin Kano ne, domin rashin izurin da na yi miki ya hana ni sukuni, ina kaunarki yar'uwata dan Allaj ki dawo, na miki alkawarin babu wanda zai ji”

Na saka number ya na dago na mika masa wayar ina kallonsa. Kwarjinsa da kirmarsa sun cika min ido, Kareem mutum har da rabin mutum, shi din mai tsayawa ne akan damuwata mai kokarin ganin bayan abun da ya hana ni farinciki.

“Na gode...”

Na furta ina hawaye.

“kwashe kudin ki tafi gida”

“Toh”

Na kwashe kudin na saka a jaka sai ya miko min wayar.

“Indai yar'uwarki tana sonki da gaske zata dawo ko ta kira ki tsakanin yau zuwa gobe, idan kuma bata kira ba, zamu yi amfani da line mu gano inda take, amman dai zata dawo na miki wannan alkawari ki kwantar da hankalinki”

Na daga mishi kai sannan ya karbi wayar na mike tsaye da cikina.

“Noor Zauna"

Na koma na zauna sai ya tashi ya nufi kitchen be dade ba ya fito rike sandwich da lemu ya janyo karamin lebur ya dora min a kai.

“Zaki iya cin wannan? Ko wani abun kike so a kawo miki? Jikina na rawa akwai yunwa a tare da ke”

Ban tsaya ba shi amsar zan iya ci ko aa ba na dauka na fara ci.

“Kar matarka ta dawo ta same mu a nan”

“Ba zata dawo ba. Yaushe rabonki da abinci?”

“Rabona da abinci tun jiya bana iya cin komai sai ruwa, gaba daya maza ba su da kirki, Zafeer be fahimce ni yanzu yana can yana cewa na ci amanarsa, na auri Hafiz ban jidadi ba, yanzu kuma wannan”

Ajiyar zuciya ya sauke ya bata rai sosai yana kallona.

“Wannan duk ya fi su zama dan iska, ni mana ban so aurenki da shi ba, kawai babu yadda zaka hana abun da Allah ya tsara faruwarsa ne, taya zai aikata duk wannan kuma ya sake ki? Ga cikin shi a jikinki”

“Ni na ce ya sake ni, ba zan iya zama da shi ba, ba zan iya zama da mazinaci ba”

Ina maganar ina kuka har na cinye duka sandwich din na shanye lemu na aje kofi, na mike tsaye Kareem be sake cewa komai ba. Ya dauki cups din ya kai kitchen ya kawo min tissue ma karba ina tsaka da goge hannuna ya jefa min tambaya.

“Noor ko da ya tuba?”

“Eh, ba zan taba iya zama da namiji mai neman mata ba”

“Kina da gaskiya, abu mai kyau na mai kyau ne, go ahead and live your life”

Na aje masa tissue a gurin na nufi kofar fita.

“Noor, kin san bana baki shawarar da zata cutar da ke ko?”

Na juyo na kalleshi.

“Daga gidan nan ki tafi gurin Mahaifiyarki kuma ki fada mata komai karki boye mata, ba zaki iya handle wannan ke kadai ba, you're too young for this”

Ban ji ina iya musa masa ba, saboda haka na amsa masa da kai sannan na juya na fice daga falon. Mai gadin ne ya bude min gate sai na nuna masa akwatina ya dauko ya ba ni na fara ja har na isa babbar titi na tari Napep na hau na fada masa umguwar da zai kai ni. A daidai gate din gidan Mama ya aje ni na ciro kudinsa na bashi ina jin marata na ciwo sosai.

Na fita ina jan akwatin na shiga cikin gidan, hankali be tashi ba sai da na shiga falonta, Mama tana cikin jindadi da kwanciyar hankali, rayuwar da bata samu ba a gidan mahaifinmu gashi a nan ta same ta, anya zan iya zuwa mata da wannan tsarabar? Kaddara ta shafi Hana, yanzu kuma ta shafi Mama...!! Na juya na fara tafiya bana son na zama silar mutuwar auren Mama, ta fada min jikinta be dauki mace a baki komai ba, face rigar da zai iya sakawa ko ya cire.

“Subhanallahi”

Na juyo jiki babu karfi na kalleta da kumburarrin idanuwana, wani tsadadden green lace ne a jikinta har kyalli yake.

“Noor...”

Ta fada cike da mamakin ganina.

“Lafiya me ya same ki? Jini kike zubarwa”

Na sauke kaina kasa na kalli kafata zuwa tile din da jini ya bata gurin da na taka na juyo. Kamar jira ake na kalla

50 / 72