Taki Zaman Aure Sirrin Zuciyar Mace by 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Author :  𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 Category :  Romance

Chapter   27 / 72

78K to 81K   out of 215.5K words

mata komai kamar yadda yayi min a aurena, a lokacin ne take fada min shi ya saka ta makaranta ta yi karatu har take aiki.

“Amman ban taba ganin kin tafi aikin ba?”

Ta yi murmushi.

“Yanzu kin ga ina da ciki wata 6 kuma gaskiya bana sha'awar aiki, na fi sha'awar zama a gida yanzu na kula da mijina da aurena, daman dai babu abun da na rasa kawai ra'ayi ne, yanzu kuma na gane hakan ina son zama a gidana ko ba komai hankalinsa zai fi kwanciya za mu kula da shi tun da ba ni kadai ba ce a yanzu”

“Haka ne, amman aiki yana da sha'awa ina son aiki sosai”

“Amman ke baki gama karatu ba aka miki aure ko? Na ga ke din yarinya ce sosai har yanxu baki gama wayo ba”

Na sauke kaina kasa.

“Haka ma a gidanmu ake cewa wai bana da hankali ba na da wayo, wai kanwata ta fi ni wayo, amman ni bana ganin haka”

Ni da ita muka juya muka kalli kofar falon da aka bude Hafiz ne ya shigo ba a irin lokacin da ya saba dawowa ba, har da yar tsabararsa.

“Welcome Barrister”

“Yan mata na har biyu, me ake tattaunawa?”

“Hira ce kawai ta karatu take fada min tana sha'awar aiki, ni kuma yanzu ya gumshe ni har na aje sai nan gaba kuma idan komai ya daidaita”

Yayi murmushi ya miko min ledar hannunsa sai na saka hannu biyu na karba, sai dai na lura kamar hakan be mata dadi ba domin a take fuskarta ta canja.

“Aiki kike sha'awa Noor, ni yanzu bana sha'awar mace ta yi aiki, ita ma saboda ta dage sai ta yi ne, zan saka ki makaranta ki yi karatu mai zurfi saboda gaba, amman zancen aiki ba yanzu ba”

Na wara ido baki sake kai kace son karatun nake.

“Da gaske zaka bar ni na yi karatu?”

“Me zai hana ni fa dan boko ne, karatu sai kin ture yarinya”

Zan yi magana ta cafke ta nuna masa murnarta a fili na jindadin yadda yace zan yi karatu tana ta yabonsa har da masa godiya.

“Ke gani ko ai na fada miki ki kwantar da hankalinki Barr be da matsala ko kadan, shi mai son kyautata ma iyalinsa ba”

Annashuwa ta suka fuskarsa.

“Wato gulmana kika yi ko? Na kama ki”

Sai ta yi dariya tana kallonsa. Shi kuma ya kalleni.

“Ba zaki bude ledar ki ga miye a ciki ba Noor”

Na bude ledar na ciro gasashiyar kaza da kayan ciki mai Onion and vegetable sai kamshi suke. Leda ta uku kuma faranti ne dauke da yar tsutsar nan da na yi sha'awar ci tun ina zuwa restaurants din Kareem.

“Waya fada maka ina son wannan?”

“Na taba ji gurin Kareem”

“Na gode”

Ina fada ina kallonsa gaba daya ya gana faranta min zuciya a yau.

“Me aka dafa?”

“Ghanian jollof na yi”

“Ku kunci kenan?”

“Har kunci kenan?”

Ta amsa.

“Eh mun ci”

Na mike tsaye rike da leadar.

“Zan tafi bangarena na ci wannan sai na sha tare da tea”

“Okay Amarya aci dadi lafiya”

Ta fada na fice daga bangaren na dawo bangare na, wanke hannuna ne kawai ya same ni dole na wanke hannun na zauna na fara ci ina jin wani shauki saboda mai da take da shi gashi ta yi laka laka kamar kitsen kilishi. Bayan na gama na wanke hannun na yi alwala na yi sallah ina nade carpet ya shigo rike da plate dake dauke da kayan ciki da kazar da ya siyo dazun.

“Kin manta wannan Noor ko ba ki ci.”

“Na ci wannan abun na koshi”

“Ki aje wannan anjima sai ki ci”

Na karba na juya zan fice sai na ji ya rikoni yana kokarin rumgume.

“Kin yi min kyau yau fiye da kullum, ko dan kin dan sake jiki kin sake fuskar nan ne”

Na yi murmushin yake Ina sauraren yadda yake yawo da hancinsa a wuyana. Sallamar Na'ima ce ta katse hanzarinsa a dole ya sake ni da sauri yana amsawa. Ya fice daga dakin da sauri

“Wai Anty tana kiranka”

“Okay”

Na bi bayansa na shiga kitchen na aje naman sannan na fito na dawo falo na zauna ina kallo. Da zai shigo yi min sai da safe ne yake sanar da ni wai an yi gobara a gidan Baba, hankalina ya tashi sosai jin cewar gidan ya kore gaba daya.

“Amman ba a rasa kowa ba?”

“Da an rasa rai da Baba ya fada min, kin san baya boyo, amman dai gobe zamu je mu duba”

“Da dare nan aka yi wutar?”

“Da yamma”

“Dan Allah ko zaka kira min Baba na ji shi?”

Na tambaya tare da fatar zai karba bukata sai dai hakan be samu ba.

“Ki yi hakuri gobe zamu je mu duba”

“Tohm”

Kusan sai da na yi mafarkin wutar saboda na kwanta a abun a zuciyata, washe gari na gyara komai na shirya da wuri ina gama karyawa ya shigo bangarena da shirinsa muka fita, a nan ma na ga rashin jindadin fitar ta mu a tare a fuskar Aisha domin ta kasa saki fuska kamar yadda ta saba sai ce masa take ya dawo ya ci abincin rana.

“Wata kila ba zan samu dawowa ba, ita ma ai zata dawo ta yi girki ko?”

Ya kalleni ina zaune a gidan gaba.

“Eh”

Ta yi mana Allah ya tsare na rufe motar yaja muka kama hanya. Ba mu yi nisa da fara tafiyar ba ya kama hannuna ya rike yana murzawa a hankali.

“A kwana biyun nan fa ina ta jin sonki yana kama ni, kin san ni ban san dadin auren budurwa ba sai yanzu, Allah yasa na same ki fiye da yadda bake tsammani”

Na yi shiru ba dan ba gama fahimtar inda zancensa ya dosa ba. Shi kuma be sake ce min komai ba har muka isa unguwar, ina kallon gidansu Zafeer dai da idona ya cika da kwalla, a nesa da kofar gidanmu ya faka ba tare da ya kashe motar ba ya ce.

“Ki fadawa Baba idan zan zo daukarki xan shigo mu gaisa ina masa jaje”

Na kalleshi kadan na dauke kai, wata kila ya fara gajiya da halin Baba ne, ko kuma dai yana jin abun da yake nema a yanzu ya samu shiyasa yake son kaucewa daga jikin Baba. Ko da yake Baba din ne iya masa sai Allah ba kowa ne zai jure ba. Bude motar na yi na fita sai da na isa kofar gidanmu sannan yayi reverse ni kuma na shiga cikin gidan namu da ya kone tun daga waje har cikin gidan. Da gudu na karasa gurin Hana dake kwance tsakar gidan da konuwa a fuskarta zuwa cinyar hannunta.

“Innalillahi Hana”

Ta fara yunkurin tashi zaune. A lokacin da Baba ya fito bandakin da sauri yaka aje butar ya kalleni yayi murmushi.

“Aha ahhh wa nakd jin muryarta a gidan kamar Nooriyya yar albarka”

Na juya na kalleshi ina hawaye.

“Baba ashe gobara aka yi?”

“Kin gani dai haka Allah ya kawo mana, wutar da dare, ina mijin naki? Baki ce ya shigo ba? Kika bar shi a waje? Ba kara ya shigo ya ga yadda gidan yayi ba”

Ya fara tafiya sai na dakatar da shi.

“Baba ya tafi yace yana maka jaje za ku gaisa idan zai zo daukata”

“Au be tsaya ba? Tohmmm... Toh toh ba matsala ai duk daya ne, kuna dai zaune lafiya ko?”

“lafiya Kalau Baba, Baba me yasa ba a kai Hannatu asibiti ba? Kuna ce fa”

Na fada ina kallon maganin gargajiya da aka shafa mata.

“Ina kudin yake Noor? Kin san yanzu abun duniya ba zama yake ba, ban da rayuwa ba ni da komai a yanzu, sai kuma wanda ya ga Allah ya ga Annabi ya kyautata mana, kina kallon yadda gida ya zama kamar kango, abun bakin cikin ma sai da na sake masa sabon fenti”

Ya fada kamar zai fasa kuka, na daga kai ina kallon bakin wutar da ya rufe ginin ya hana a gani fentin.

“Ai na so Hafiz din ya shigo ya ga yadda gidan ya koma”

Na kalli Baba bance komai ba. Kamin ya shiga tambayata ya kishiyata ya zaman gidan Baba wata matsala, na amsa masa da komai lafiya. Ina nan wasu makotan suka shigo jaje suna ta maraba da ganina har suna fadin wai na fara natsuwa saboda na kasa hada ido da su.

“Aure na natsar da mutun, wai Noor ce a haka, Allah ya bada zaman lafiya”

A fuskar Baba nake ganin yadda kalamansu suka masa dadi, bayan sun fita shi ma ya fita a nan na samu damar hira da Hana tana fada min yadda wutar ta fara.

“Daga dakin Mama ta fito, kuma bachin ya mana nauyi duk ba mu san ta kama ba sai da hayaki ta cika gidan, Yaya yana dakinsa na zaure Baba kuma a waje ya kwana ni kadai ce a daki”

“Ya aka yi ta kai ga jikinki?”

“A lokacin da na farka na ga wutar tana ci sosai har kusan kofa ba damar na wuce ta saman kuma ta sauka kan katifa sai ta kama tufafinmu ceiling saman kuma yana ta narkewa yana fado min a jiki kin san na roba ne idan ya digo kamar fatar zata cire nake ji, sai da Alhaji Bashiru ya shigo ya fitar da ni”

“Ni ma ban sani ba sai jiya da dare Hafiz yake fada min, amman Hana baki ma Yaya magana ba ya kai asibiti?”

“Ba shi da kudi ai kin ga da ya kai ni, Baba kuma ba zai iya kashe kudinsa ba ji yake hasara yayi, ban dan ma gobarar nan ba jibi za a kawo amaryarsa shiyasa kika ji yana fadar yayi fenti”

Na gyara zama ina mamaki.

“Auren dai yana nan da gaske?”

“Noor to me zai hana? Mama ma aure zata yi?”

“Ita ma? Yaushe? A ina?”

“Garin nan, wani mai rufin asiri ma kuwa motarsa ma abar kallo ce”

Dadi na saka ni murmushi.

“A ina Mama ta hadu da shi?”

“A cikin unguwa ya zo gidan wani abikinsa”

“Amman shi ne ba a fada min ba? Bani da labarin kowa babu mai zuwa gurina kun bar ni can ni kadai”

“Noor ba a kusa kike ba balle nace zan taka da kafa na tafi, ba ni da kudin abun hawa kuma mijinki ma zai gaji idan aka ce kullum zai na je”

“Ba zai gaji ba ita ma kanwarta tana yawan zuwa ai, ko jiya ma taje kuma baya cewa komai”

“Sai na samu lafiya zan zo”

Da kanwata da kusan zan iya cewa tawainiyata ma muka sha hira muka koshi, ina ta sake saken yadda zan saci kafa na tafi na ga Mama babu hali, domin na san Baba zai yi fada idan ya dawo be tarar da ni ba, dole a wayar Yaya na gaisa da ita har nake tambayarta ance zata yi aure.

“Da yardar Allah kuwa Noor, idan lokaci yayi ai dole za a fada muku”

“Mama yaushe zaki zo?”

“Yaushe aka yi auren ma balle na kwashi kafafuwa na tafi Noor? Ni fa uwace ba zai yiyu na tafi gidanki ba sai da dalili”

“Amman Mama kin ji Baba yayi wuta?”

“Uhmmm Allah ya kyauta gaba, Noor ki rike aurenki da mutuncinki, idon mutane yana kanki kowa jiran yake wani abu ya faru da ke, kuma kin ga zaman gidanku nan ba shi da dadi, da alama kuma mijinki mai hankali ne da tunani, kishiyarki kuma ki rike ta da mutuncin kuma ki yi taka tsantsan da ita, ki rika kula da rayuwa na san halinki da sakarci, balle kuma an dauke ki an kai ki gurin babbar mace ina yarinya karama, ta fiki wayo ta fiki hankali kuma ta fiki sanin kan mijinku, ki bi a hankali kuma ki rike addu'a kar na ji kar na gaji wani abu ya faru, kuman ko da wasa bana son na ji kin bibiye Zafeer aure ya rabaki da kowa yanzu”

“Toh Mama, zan kiyaye, Zafeer ni ba zan taba yin magana da shi ba, ai Baba yace be yafe min ba idan na yi masa magana”


“Toh sai ki kiyaye, ki zauna lafiya a gidanki kin ji?”

“Toh Mama”

Sallama muka yi sannan ta kashe wayar na mikawa Yaya.

“Mahaifiyar Kareem ta rasu ko Yaya?”

“Eh kwana uku aka yi ai ba a bude restaurant din ba, sai da aka yi sadakan uku duk mun je masa gaisuwa”

“Yayi kuka?”

“A gabanmu zai yi kuka? Sai dai a boye ko? Kin masa gaisuwa”

“Hafiz be bari na tafi ba matarsa kawai ta tafi, wata kila sai nan gaba idan na fara fita”

“Kila”


Saman sama muke taba hirar Yaya na fada min Kareem din ya rame sosai abun ya taba shi. Na yi zaton Hafiz zai dawo da rana ya dauke ni saboda yayi min zancen girki amnan shiru be zo ba sai bayan Isha'i a lokacin Baba har ya gaji da jiransa. Yana yin sallama Baba ya tarbeshi jiki na rawa suka gaisa sannan ya shiga nuna masa gidan yana fada masa yadda gobarar ta fara.

“In shaa Allah zan kira ka Baba sai mu yi magana na ga abun da ya dace ayi”

“Na gode Allah ya saka da alheri ya kara rufa asiri...”

Baki har kunne baba yake Fadar haka, sai dai ko kadan ban ga alamar sake fuska a gurin Hafiz ba, yadda yake rawar jiki da Baba ma wannan karon ban ga yayi haka ba. Ba Baba kadai ba ni kadai na yi tsammanin zai bawa Baba kudi ko kuma ya ce akai Hana asibiti amman ba ko daya har muka fito gidan. Na shiga motarsa shi ma ya zagaya ya shiga sai da yayi min wani kallo da ban fahimci ma'anarsa ba sannan ya tashi motar muka fara tafiya.
Ban kalleshi ba, sai dai na ji a jikina yana yawan kallon gefe da nake zaune.

“Noor na ga kin bata rai, ko kin yi marmarin gida ne?”

Na yi shiru bance komai ba, hannu na ga ya mika bayan motar ya dauko kwali ya dora min a cinya.

“Ya kamata ke ma ace kina da waya ko?”

Na kalli kwalin wayar na kalleshi ina zaro ido.

“Tawa ce?”

Ya daga min kai, sai na rasa ina zan saka kaina tsabar farinciki domin taba rike wayar kaina ba. Yana faka mota harabar gidan na fita da sauri na shiga bangaren Aisha ina nuna mata wayar, sai ta fini farinciki da jindadi ma ita ta taimaka min na saka sim din ta nuna min yadda ake operating wayarsa.



#KhadeejaCandy

PAID PAGE 6️⃣


©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024

Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar

And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....


You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153


_______•••_______

“Allah ya tsare ya sa albarka”

Ta yi min addu'a sai na amsa da amin sannan na karbi wayar bayan ya saka min number shi da number Baba da kuma na Aisha.

“Amman fa karki je ki kira Saurayinki da wayar nan na sa halinki”

Ta fada tana min wani kallo kamar na zolaya, ni kuwa na kalli Mijina na kalleta da mamaki.

“Ya za'ayi na kira sho kuma? Na fa yi aure yanzu na sani”

Ta sake fuskar zolaya tana min wani kallo na rashin yarda.

“Ke dai kin san yadda muke sirrinmu ko? Kawai dai ki kiyaye, ke matar aure ce a yanzu kin ji kanwata”

Na amsa mata da tohm domin kawai na takaita zancen sannan na mike tsaye rike da wayar da kuma jata na fice daga bangaren. Ina shiga bangarena na tare a kujera ina ta kallon wayar bude nan taba nan hotunan da na yi kuma sun fi a shirin a zama daya. Ima tsaya da daukar wani hoton sai hango Hafiz na yi ta cikin hoton ya leko kansa. Na juya na kalleshi ina dariya shi ma dariyar yayi ya matso kusa da ni ya zauna.

“Daukin wayar ne har yanzu”

“Eh na gode Hafiz”

“Ki daina cewa Hafiz Noor”

“Tohm Yallabai”

A bakin gaskiya ta na fada sai dai na lura kuma hakan dariya ya saka shi domin dariyar yake kamar na fadi wani joke.

“Ur Welcome..”

Ya kama hannuna na rike ya juyo da kafadata daya na fuskance shi da kyau.

“Noor, please karki ba ni kunya i trust you, kar na ji ko na ga abun da zai bata min rai wayar nan, ba ma waya kadai ba a komai ma, kin ga Aisha ta fada min abubuwa da kika fara fada mata akan zamantakewar duka duka kuma yaushe muka fara zaman auren? Sirrin dake tsakanina da ke na mu ne mu kadai kawaye iyeye ko abokiyar zama babu wanda zai sani, wanda ke tsakanina da ita kuma ita ma zata rike babu wanda zai sani, kin ga da farko na ji haushi amman daga baya na yi tunani hankalinki da tunaninki ba irin nata ba shi, saboda shekarun ba daya ba, amman ina son na ja kunnenki karki fadawa kowa sirrinmu kin ji? Kuma zancen baki so na kika aure ni na san wannan ita ma ta san wannan ba sai kin yi ta nanata mata ba kina fada mata yadda na raba ki da saurayinki, yan'uwana ba su san irin auren da muka yi ba, so bana bukatar su san cewar wai baki so na kika aureni kinji”

Na daga mishi kai.

“Me tace na ce”

Na tambaya ina mamaki, domin ban san na taba fada mata wani abu a game da Hafiz ba, yo ni da har yanzu ba mu taba hada shimfida ba ta ina zan fada sirrinsa? Kuma yaushe nake fada mata yadda ya raba ni da Zafeer.

“Cewa ta yi kin kura min ido kamar zaki cinye ni”

Ya ja hancina hana kallon cikin idona. Na sauke kai kasa.

“Baki jin yunwa ne? Ko kin ci abinci a gida?”

“Aa ban ci ba, kai baka ci ba?”

“Ban ci na so ki dawo ki girka, ni ma ban samu dawowa ba sai daren nan”

“Girki cikin dare akwai wahala kamin ka fada na yi bachi”

“Wa zai dafa?”

Na dan saci kallonsa na sauke ido, ba dai yana nufin ni na girka ba? Ganin na yi ya mike tsaye.

“Taso muje mu siyo wani abu a waje”

Na mike tsaye ina rike da wayata, a nan na bar jakar da na dawo da ita daga gida. Hannuna ya kama muka fita daga falon be sake

27 / 72