Gudun Aure 1 Complete Hausa Novel

Author :  Binta Umar Category :  Romance

Chapter   8 / 18

21K to 24K   out of 51.4K words

kawai kawar da kaina. Da 'kyar aka samu sasanci. Amma dukda haka d'angaruwar nan sai da aka biya shi kud'in taya da wili acewarsa ba a haka ya ajiye kurar ruwansa ba.
Kudin beli dubu talatin. Suka buk'ata Kowanne dubu goma gabad'aya kudin hannuna basu wuce dubu sha uku ba. Babu yadda za a yi na yi belin mutum biyu na bar dayan. Tare suke shashancinsu, bayan haka ma iyayensa ba su da wani karfi ta abinda za su ci suke yi. Na bada abinda ya rage a hannuna na fita na ciro sauran na na cika musu sannan suka ba mu yaran muka kama hanyar gida lokacin tara saura na dare.
Lokacin da za mu shiga gidan ne na lura da dinginshin da Kamalu yake yi shi da Saminu sai ra'be-ra'be suke yi suna bin bango.
Usaini kuwa sai talle musu keya yake yi. A haka muka shiga gidan duk suna tsaye cirko cirko. Na bude d'akin na shiga na zauna 'kafafuna har yanzu ba su daina rawa ba.

Tun ina jin hayaniyarsu har na daina ji tabbacin kowa ya watse ya kama abinda yake gabansa. Na tashi na le'ka tsakargidan ta tagar dakina. Sai na gansu su biyu a zaune a tsakargidan su kad'ai. Shi Kamalun Yana ra'kube a kuskurwa ya rungume gwiwarsa. Yusi din yana gurfane a gabansa Yana kuka. Na daure zuciyata sosai na ce." Kai Yusi kukan me kake yi ku taso daga nan ma."
Ya kalleni da sauri yana cewa." Mama don Allah ki yi hakuri kada ki dake shi, jikinsa da ciwo da kafarsa ta kumbura, ya ce ba zai sake yi ba."

Na ce." Ai ba zan dake shi ba, ku taso ku dawo d'aki."
Ya riko hannunsa yana cewa." Yaya ta so mu je, ta ce ba zata dake ba." Ya dago kansa ya kalleni. Na ce." Ta so ku shigo ba zan dake ba." Sai hawaye shaaa! suka fara zubowa daga idonsa. Na d'auke kaina da saurin gaske na bar jikin tagar.
Rigijib haka na zube kan tabarmar duk ko'karin da nake yi wurin danne masifaffan kukan dake ta damuna kasawa na yi. Ya kufce da karfin gaske na sanya hannu na toshe bakina. Na silale na kwanta ina kukan haikan tare da tunanin ranar da Allah zai yaye mini k'uncin dana ciki tunda ga kuruciya.

MAFARI

Malàm Salisu mai hula shine mahaifinmu. Mutum ne mai ha'kuri da sanyin hali. Uwa uba kuma mara son hayaniya domin da wahala wata hatsaniya ta tashi a cikin unguwarmu ka ji sunansa a ciki. Ya kan kokari wurin ganin ya kama girma da mutumcinsa. Yadda ake fad'a tun yana k'arami ya tashi da zuciyar neman na kansa . Dalilin da ya sanya ma kenan ya fara fatauci zuwa gari gari kai huluna. Sai da Iya mahaifiyarsu ta nuna rashin yardarta da hakan tukkuna ya ha'kura. amma dukda hakan fataucin ya janyo masa alherin arzikin had'uwa da uwargidansa wato Mamanmu kenan mai suna Saratu. Asali Maiduguri kowa ya san gari ne da ake sana'ar huluna irin daban daban. A nan garin Allah Ya had'a shi da Mamanmu a kasuwa ta je sayayya kusa da shagon da yake zama ya gudanar da sana'arsa. Ba a ja dogon lokaci ba da suka aminta da junansu soyayya ta kullu sai iyaye suka shiga cikin lamarin aka gudanar da bincike ta kowane bangare babu wata matsala waliyan Babanmu suke shige gaba har garin borno aka dauro aure.
Babanmu bashi da matsalar wurin zama tunda mahaifinsu su uku kacal ya haifa kuma kafin rasuwarsa sai da ya bawa kowa wurin zama. A gidansa da yake unguwar kabuga cikin kwaryar birnin Kano Mamanmu ta tare da komai na al'adarsu. Sun yi farinciki sosai a lokacin da suka ga wurin zamanta ya yi kusanci da gidan aminiyar Dada wato mahaifiyarta. Suka dinga godewa Allah da ya sanya akwai wadda za su barwa amanarta a garin.
To Gwaggo maihaifiyarsu Yaya Aminu itace ta zama uwardakin Mamanmu kuma uwa a gare ta.

Mamanmu ta jima bata haihu ba. Hankalin Babanmu ya tashi don ganin yadda 'kaninsa Sule daga yin auransa har ya haihu. Kun san dai zama irin na Malam bahaushe. Babanmu ya fara wasu dabi'u. Ya canza gabad'aya. Gashi dai bashi da wani karfi kullum da 'kyar suke kai labari amma a hakan ya fara fafutukar kara auran wata bazawara. Ashe a lokacin Mamanmu tana da ciki ba ta sani ba, Shima bai sani ba. Tsabar tashin hankalin da take ciki ya gigitata ta kasa gane halin da take ciki. Ita macece mai bala'in kishi. Dalilin da ya sanya ma kenan ta figale ta lalace koyaushe ita da mijinta babu zaman lafiya. Shi kuma a lokacin idonsa ya rufe da son haihuwa.

Sai ta tattara kayanta ta gudu gidan Gwaggo da kudirin ba zata koma ba ta gama auran gabad'aya. Ita ba zata zauna da kishiya ba. Gwaggo ta dinga rarrashinta Amma fafur ta ce ba zata koma ba.

Shi kuma Babanmu kamar sammatace a lokacin baya ganin kowa da mutunci sai Ummansu Hadiza. Domin Iya mahaifiyarsa ma ta rasa gane kansa. Ta je gidan Gwaggwo akan Mamanmu ta koma dakinta. Gwaggo ta ce idan mijin yana buk'atar cigaba da zama da ita ya zo a samu sasanci.
Ashe Baba Sule ne yake zuga shi akan kada ya je ya rabu ma da auran Mamanmu gabad'aya tana da farar kafa ba zai ta'ba cigaba ba. Auran Murja wato Ummansu Hadiza shine alheri a tare dashi tunda yayar matarsa ce, kuma gidansu akwai arziki na dukiya da kuma na haihuwa.
Babanmu ya yarda da maganar d'an'uwansa. Ya jingine Mamanmu a gidan Gwaggwo ita ba mai aure ba ita ba mara aure ba.
Lokacin da Gwaggo take yun'kurin sanar da su Dada halin da ake ciki a lokacin Mamanmu ta dinga wani irin ciwon kafa babu tafiya sai rarrafe.
Gwaggo ta aika aka sanar da Babanmu halin da ake ciki. Ya ki zuwa tunda a lokacin ma har an d'aura aure ya tare da matarsa a daya daga d'akunan dake cikin gidan.
Gwaggo ba miji ne da ita ba, ya rasu shekaru kusan biyar kuma ya bar mata marayu hud'u itace take d'awainiya dasu a lokacin inda Allah Ya rufa asiri tana 'Yan sana'oi na hannu a lokacin shiyasa asirinta yake a rufe. Haka ta yi ta jigila da Mamanmu asibiti akayi gwaje-gwaje likita ya tabbatar da ciki na wata shida kuma har ya juya shine sakamakon ciwon kafafun da take yi.
Ba a mamaki da ikon Allah amma lamarin ya bawa kowa mamaki. Gwaggo ta sanya aka kira babamu a karo na biyu yaki zuwa. Sai ta shirya ta nufi shagonsa anan ta same shi da maganar ta kuma nuna masa sakamakon a rubuce.
Ya tsorota sosai kuma ya yi mamaki da ikon Allah jikinsa ya mutu ya gaza had'a ido da Gwaggo ya dinga kame-kame Yana ko'karin kare kansa. Gwaggo ta ce to tunda haihuwa ce matsalar sai ka zo ka d'auki matarka ka kuma ji tsoron Allah ka yi adalci da ni da kai duka amana aka ba mu. Ta kamo hanyar gida ta bar shi da alhini.
Baba Sule ya so ya zuga shi domin ya firje ya'ki amincewa da cikin akan ba nasa ba ne. Babanmu ya ki yarda da shawararsa saboda shi yafi kowa sanin yadda ya sami matarsa.

To ashe haihuwar ra'kuma daga babamu ne. Domin itama Ummansu Hadiza duk da take bazawara kuma ta haihu a wani wuri ba daga shigowarta ta haihu ba sai da Mamanmu ta haifi anti Yagana da shekara biyar tukkuna Ummansu Hadiza ta samu cikin d'anta na fari, kuma cikin ikon Allah da ya ta haife shi kwana biyu Allah Ya kar'bi abinsa. Ta dinga kuka tana cewa Mamanmu ce ta 'kona shi da ruwan zafi tunda a lokacin da ya rasu Mamanmu ba ta jima da yi masa wanka ba.

Dama zaman doya da manja suke yi. Mamanmu tana dannewa ne a matsayinta na Uwargida. Kada ace ita ce bata k'aunar zaman lafiya. Amma dai duk da haka watarana idan Ummansu Hadiza ta kai ta bango fitowa take yi su yi ta cacar baki. Tana da ha'kuri a wasu lukutan. Amma ba ta son raini. Shiyasa anti Yagana take fad'in halinmu daya da ita na rashin san wargi.

Kusan lokaci daya aka samu cikinmu ni da Hadiza a yadda Ummansu Hadizan take ba mu labari tare suka dinga laulayi har Allah ya kawo lokacin haihuwar tazarata da Hadiza ta kwana tara ce. Ita aka riga haihuwa sai ni. A lokacin ita an yi mata hakika da tinkiya katuwa. Ni kuwa Babanmu ya ce bashi da kudi sai dai Mamamu tayi ha'kuri tunda ya yi mata na fari.
Mamanmu ta dinga kuka tana fad'in ba ta yarda ba ai 'yar sunna ce, yadda aka yankawa kishiyarta tinkiya itama sai an yanka mata. Shi kuma ya ce Ai ba dole ba ne, shi dai ya rad'awa 'yarsa suna Amina. Kamar yadda ya rad'awa 'yarsa Hadiza.
Can gidansu Mamanmu da suka ji labari abin bai yi musu dadi ba ko kad'an. Da yake Dada tana kiwon akoyiyi sai tasa aka yanka guda daya. Aka soye tsaf da zasu zo duba ni suka kawo mata da sauran abin buk'ata.
Dukda haka abin bai saki Mamanmu ba, domin bambamci ko a kayan barka sai da Babanmu ya nuna na Hadiza sun fi yawa ni kuma nawa kad'an. Da ta yi magana ya ce ai ita ya yi mata ba fari.
Wannan abin ya dinga haddasa rikici a gidan. Babanmu daga ya d'auko hanyar gyara idan ya gane kuskuransa sai Baba Sule ya rusa. Ya d'ora shi a wata hanya ta daban.....✍️
*1k on talgram via 0542382124..Binta Umar gtbank*
*07084653262*
[11/20, 1:17 PM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*

*TALLAH!*
Albishirinku mata 'Yan gayu yan gwalisa kuyi maza kugar zayo shagon
(Aysha/Addah beauty saloon and spa).
Shin kintaba zuwa ingancaccen saloon din Aysha/Addah, idan baki taba zuwa ba kiyi maza kar a barki a baya domin sun qware a wajen aikinsu Wanda suke services dinsu cikin sauki tare da annasuwa
Suna wanke kai(wash and set)
suna wanke qafa(pedicure)
And sunayin steaming iri iri suna saida (supplements)suna kitso dama duk wani abu daku so Wanda akewa mace ta amsa sunanta mace yar qwalisa
Address dinsu nanan a Federal low-cost opposite open University gombe state
Ko kuma ku tuntune mu a wannan number kamar haka,
08037925676
Or
08167764242
Whatsapp ko kuma Call we’r available 24/7..


*@Arewa books*
*Bintuumarabbale.*
*free pege*
*11*
Sanyin halin Babanmu shine ya sanya Baba Sule yake yi masa kutse a cikin duk al'amuransa . Kwata-kwata Allah bai had'a jininsa da Mamanmu ba tunda ta zo gidan gaisuwar kirki ba ta had'a su ba. A wasu lukutan ma sai ya zo ya yi abubuwansa ya fita bai kulata ba kuma tana a matsayin matarsa d'an'uwansa ciki daya sai dai ita take ture komai ta gaishe shi. Idan kuma 'yan miskilancin suna kusa da ita kuma sai ta share shi har ya gama abinda ya kawo shi gidan ya tafi yana habaice habaice sai ka ce wani mace.
To irin wad'annan matsaltsalun su Mamanmu ta dinga ajiyewa a ranta har ya haddasa mata ciwon zuciya wanda shi ya zama ajalinta duka ba a ankara ba, ta dinga ciwo a tsaitsaye har sai da ta fara kumburi tukkuna Baba ya farga suka nufi asibiti likita ya tabbatar da cewa zuciyarta ce ta ta'bu. Gwaggo ta shiga rudu sosài don har Mamanmu ta ma ta fita dauriya, ita ta dinga tausarta. A lokacin shi ma babamu ya tsorota sosai ya mayar da hankali wurin nemo mata magani na gida dana asibiti. Ya nemi alfarmar gwaggo akan kada ta sanar da gidansu halin da ake ciki.
Kulawar da take dan samu dalilin ciwon sai Ummansu Hadiza ta sanya kishi a ciki. Itama koyaushe sai ta kirkiri ciwo ta kwanta tace bata da lafiya. Haka babamu ya zama kamar zautacce a wancan zamanin ga rashin kwanciyar hankali daga cikin gidansa ga neman abinda za a ci.
Lokacin muna da shekara takwas a duniya. Ni da Hadiza tare muka tashi cikin ikon Allah suka sake samun ciki a lokaci daya. Abin ya had'ewa Mama laulayi da ciwonta da yake tashi a sa'i da lokaci don dai ma Gwaggwo da Babanmu a tsaye suke akanta duk inda suka ji magani mussaman na hausa suna ko'karin saya mata. Kuma idan an jarraba ana dacewa. Sai dai idan kwana ya kare babu yadda za a yi. Mamanmu ciwonta ya tashi da zafin gaske ga ciki na wata biyar a jikinta.
Suna zuwa asibiti aka bata gado lokacin ma ba ta gane wanda yake kanta.
Kwana biyu 'yan gidansu suka zo, domin duk abinda yake faruwa babu wanda ya sani a cikinsu. Gwaggo ganin yadda abin ya yi tsanani ya sanya ta sanar dasu. Wani d'anuwan Dada da yake da rufin asiri ya bada umarnin a d'auketa a kaita babban asibiti zai biya kudin da duk abinda aka buk'ata. Babu rabon shan wahala da asara rai ya yi halinsa a lokacin da ake yin cuku-cukun. Mamanmu ta rasu da cikin a jikinta a daran alhamis aka kaita Juma'a da safe.
Alokacin da kuruciya ban fahimci mutuwa ba. Ni dai kawai na daina ganinta idan na tambayi Gwaggo sai tace mini ai ta tafi saudiya.
Da aka share makoki Dada ta bukaci da Baba ya ba ta ni, tunda ni ce karama. Ummansu Hadiza ta ce a bar mata ni din za ta had'a ta ri'ke mu tare 'yarta idan an d'auke ni Hadiza ba za ta ji dadi ba.
Ganin yadda ta nuna damuwarta akan hakan ya sanya Babanmu ya ce Dada ta yi hakuri ta d'auki anti Yagana idan ya so ni sa'i da lokaci sai a dinga kaini garin muna gaisawa.
Haka kuwa akayi suka tafi da anti Yagana tana kuka Ina kuka haka muka rabu. Gwaggo ta rungume ni tana cewa na yi hakuri za a dinga kaini lokaci zuwa lokaci.

***
Na koma hannun Ummansu Hadiza gabad'aya. Da farko kamar abin arziki sai daga tafiya ta mika tukkuna ta fara nuna fifiko da bambamci a tsakanina da yaranta Hadiza da Fati wadda ta haifeta bayan rasuwar Mamanmu. 'Kiri'kri take nuna komai. Ina kallo zata sayawa yaranta wanduna da 'yan kunnaye da kayan kwalliya ni ba zata saya mini ba. Sai dai na je gidan Gwaggo idan ta lura babu d'an kunne a kunnena sai ta saya mini ko ta cire na kunnanta ta sa mini. Wasu lukutan ma haka zata dafa ruwan zafi ta wankeni da wandon jikina wanda sai ya fi wata d'aya ban cire ba. Gwaggo itace take saya mini wanduna da kayan kwalliya sannan itace take tsefe mini kai ta ba ni kudin kitso na shiga nan makotansu a yi mini.
Da Ummansu Hadiza ta lura da Hakan sai ta hana ni zuwa gidan gabad'aya. Idan mun taso daga makarantar allo Hadiza zata shige ta kwanta ni kuwa zan yi shara da wanke-wanke sannan na je wurin Babamu na kar'bo kudin cefene na je na yi. Tun ban kai shekara goma sha biyu ba na ke yi mana girki. Nasha k'onewa a hannu da k'afa wasu lokotan idan na nuna mata sai ta yi mini banza, sai ta ga dama za ta ce mini sannu. Haka nake warkewa. Kayan makarantarmu na boko ni nake wanke mana. Wani sa'in ma idan Ina wanki Ummansu Hadiza za ta de'bo 'yan k'ananun kayan tagwayen da take goyo Hassana da Usaina ta watso mini tace na wanke musu.
Ba ni da lokacin kaina kullum idan naje makaranta na dinga gyangyad'i kenan, domin wasu lukutan ma da daddare har aikena take yi wurin masu awo da kantina idan tana buk'atar wani abu.

Watarana mun dawo daga makarantar boko ni da Hadiza nuna tafiya sai ga Yaya Aminu akan Kekensa. Na dinga washe baki ya tsaya a gabanmu Yana murmushi. Hadiza ta murguda bakinta ta bar wurin bata gaishe shi ba. Ni kuwa muka gaisa sosai Yana yi mini wasa kamar yadda ya saba a lokacin da yake tambayata me yasa na daina zuwa gidansu ban rufe masa ba na sanar dashi Ummansu Hadiza ce ta hana ni.
Ya rarrasheni sosai yana fad'in ki cigaba da ha'kuri dadin abin ma ke macace aure za a yi miki watarana sai labari. Ya d'auko dari biyu ya ba ni.

Ina shiga gida Ummansu Hadiza ta rufe ni da fada wai na tsaya shiririta bayan na san akwai abinda zan yi. Na ce mata mun gaisa da Yaya Aminu ne shiyasa ban shigo da wuri ba. Hadiza tana daga cikin d'aki na ji tana cewa wannan cangal din ai dan'iska ne, ki cigaba da tsayuwa dashi zai lalata ki.
Raina ya b'aci sosai. amma sai na share ta ban ce komai ba, itama Ummantasu bata kwa'beta ba. Na cire kayan makarantar jikina domin yin abinda yake gabana.
Sa'i da lokaci Yaya Aminu ya kan ba ni dari biyu a duk lokacin da muka had'u. Ni kuma zan kar'ba da murna da farinciki domin wannan dari biyu da yake ba ni tana taimaka mini sosai a makaranta idan ana birek don ma wani sa'in Sahura tana zuwa da abinci sai mu ci tare ina rage yunwa mutuka. Su Hadiza Ummansu tana basu hamsin hamsin kullum. Ni ce dai bata bawa. To ashe tana lure da ni idan an fito birek din ina sayan Aya da gyada. Sai ta je ta gayawa Ummansu ita kuma ta titsiyeni tana tuhumata wai maza nake bi suke ba ni kudi suna tabbatani.
Na dinga kuka ina gaya mata ba haka ba ne. Yaya Aminu ne yake ba ni dari biyu wasu lukutan. Ta dinga fad'in to shi ma ai d'an iskan ne garjejen tuzuru dashi yana zaune shekara arba'in babu aure ai dole sha'awa ta yi masa yawa ya dinga tare yaran mutane Yana tattabe su. Na ce wallahi babu abinda yake yi mini Umma ki aika a kira Sahura ma ki tambayeta ni ba na kula maza.
Hadiza ta dinga fad'in itama Sahurar ai halinku daya haka take kashe kudi a makaranta.

Da Babanmu ya dawo ta gaya masa. Ya yi mini fad'a sosai, amma shi bai zarge ni ba. Sai da Baba Sule ya zo Ummansu Hadiza ta gaya masa. Ya dinga zagina Yana zagin Mamanmu har sai da ya dake ni da igiyar da muke shanya, yana fad'in

8 / 18