Gudun Aure 1 Complete Hausa Novel

Author :  Binta Umar Category :  Romance

Chapter   14 / 18

39K to 42K   out of 51.4K words

Yana zuwa wasa lafiya lau ba a dukansa, sai na kyaleshi, dama kamar yadda ta fad'a babu yadda za a yi yaro ya rayu shi kadai, ko shi Kamalu dana takure a wuri d'aya don ba yadda zai yi ne. Shiyasa lokacin da suka fara zuwa makaranta kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha saboda murna.
Na gargad'e shi sosai, akan ya kula. Inda hankalina ya kwanta ma direba ne yake kai su ya kuma dawo dasu, Islamiyya ce kawai suke tafiya da kansu tunda a cikin unguwar take.

Yusi ya riga ya zama d'an d'akin anti Maimuna, don jininsu ya hadu da Salima, itace ta k'ara ri'ke shi, ko makaranta tare suke tafiya, ba ya jiran d'an uwansa, Yana shiryawa yake zuwa wurinsu, sai dai shi Kamalun ya tafi shi kad'ai.
Hakan ya daga hankalin Jamila, macece mai zargi, ta hana mu sakat a gidan, neman rigimar yau daban dana gobe, fadi take na zo na rikita musu gida, ina ko'karin rabawa yaransu zumunci, tunda dalilin sha'kuwar Yusi da yaran anti Maimuna ya haddasa ba'kar gaba da rikici tsakanin yaran nasu. Turzumi da 'yan'uwansa, kaf sun daina shiga wurin Anti Maimuna, wanda dama can nan ne, dandalin wasansu, saboda ita tana da sau'kin hali, kuma tana jurewa hayaniya shiyasa kowane yaro yake da sakewaa wurinta, ba kamar ita jamilar ba.

Ni dai tunda muka yi cacar baki akwanakin baya, ban sake bi ta kantaba, al'amurana sun sha kaina. Yanzu na ajiye d'inkunan jakkunkunan da nake yi, na durfafi manya dinkuna irin na mutan nijar mali, da sengal. Tun lokacin da na je Maiduguri bikin Babandi na yi wa Ya Falmata d'inki, Allah Ya haskaka al'amarina. Jama'a suka dinga kar'bar style a wurinta. Kawai sai ta yi tunanin sayan kayan aiki da irin sutturun da suke tu'amalli, ta kira ni a waya tana sheda mini, za ta turo mini da aikin, idan na kammala sai nasa a mata a mota, ita tana da masu saya a hannu.
Na yi ta godewa Allah, saboda na san wani cigaba ne ya zo mini. Sai dai tunda na fara had'a-hadar ayyuka suka yi mini yawa, ranar girkina na kan sha wahala sosai, kuma wani aikin idan ta turo mini da sauri ake bu'katarsa.
Kamalu makaranta dama shine yake taimaka mini da sanya zufa, jera stones kalmasa da sauransu duk ya iya wannan, Hamusu ko Usaini wani daga ciki ya kai mini tasha a dora a mota.
Yanayin aikina ya fara ta'ba zamantakewata a gidan. Domin ranar girkina zahiri ni ma na sani, ba na gama abincin rana da wuri, Yara suna makara a makaranta, wasu lukutan ma haka suke tafiya ba su ci ba, sai sun dawo tukkuna. da daddare ma sai na kai bayan Isha'i, ban fito daga kicin ba, gajiya ta rafkar da ni, maigidan ya zo da buk'ata na kasa katabus, jikina ya mutu, babu wata kulawa da yake samu.
Anti Maimuna dai tana yi mini kawaici ba ta ta'ba korafi ba. Jamila kuwa mun sha musayar yawu da ita, domin duk lokacin da ban gama abincin rana da wuri ba har yara suka tafi makaranta ta dinga mita kenan, kamar ta zage ni, tana fad'in ai ba neman kudi na zo yi ba, bautar aure na zo yi, akan me zan dinga azabtar dasu. Wasu lukutan shiru nake yi mata, amma idan ta kai ni bango kaca-kaca nake yi mata na ce ba zan yi girkin ba, ta yi duk abinda za ta yi.....✍️
*Gudun aure 1k on talgram via 0542382124....Binta Umar gtbank ko 7084653262 Binta Umar Opey bank. Yan nijar dala dari katin Airtel. Ga masu bin wannan book din ina miko gaisuwata zuwa gareku. Ina daf da kammala free peges tuntuni dai an fara payment labarin nan ba mu fara shi a hakan zan ce muku sharar fage ne. A hanzarta biya domin jin yadda za ta kaya. Na gode muku masu messages fatan alheri tare da yabo bisa wannan littafin Allah Ya saka muku da alheri🤲💝*
*07084653262*


*TALLAH!*
🌲🌳🌿☘️
*DA MAGANI A GONAR YARO!!*
*08089965176*
*07084653262*
*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*
[11/26, 10:38 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*
*TALLAH!*
*Gidan 'kawa ne da kece raini.💯*
🛍️ “Ko ba ki da niyyar siya ba, ki zo ki shiga ki kalla kayayyaki — wallahi sai kin bude ido! Ballantana kuma nasan za ki tashi da kaya saboda kyau da araha.” ✨
🌸✨ “Shigo duniyar da kyau da jin daɗi suka haɗu — daga kyawawan laces na alfarma, Atamfa , abaya masu salo, zuwa kayan ado masu kyalli, kayan girki na zamani da sauran ƙarin abubuwa. A Meerah B Collection , muna adashen kayan kitchen daily 1k to pack 100k items weekly Monthly ✨🌸We are sale kitchen items, electronic, WE ALSO DEAL WITH CONTRIBUTE monthly weekly daily after 10 days for kitchen items or electronic gaba daya wanna package 60k nake had'a sa zaku iya mallaka ta hanyar adashi

https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t

*@Arewa books*
*Bintuumarabbale*
*17*
*Free pege*
Ashe akan ga'ba muka yi wannan sa'insar. Sai maigidan gabad'aya ya d'auki laifi ya d'ora mini, yadda yake yin fad'a shi ya kara tabbatar mini da cewa a kufule yake da ni, dama yana Jin haushina.
"Zaman aure ki ka zo gidana Amina, na gaji da rabon fad'a, kusan koyaushe Jamila sai ta kawo mini korafi akanki, na gaya miki tuntuni matan nam suna zaune lafiya, ban saba da irin wannan tashin hankalin ba, me zai sanya daga zuwanki ki d'aga mana hankali, muddin ba za ki bi umarnina ba, kamar yadda na sanya ki ka ajiye aiki, to d'inkin ma za ki daina yi mini a gida, domin ba zai yiwu ki zo kina neman kudi a gidana ba, kuma kina watsi da umarnina, ni kaina ba na samun kulawa a ranar girkinki, kin fi bawa neman kudi muhimanci, ki gyara muddin kina so ki zauna da ni."
Ban katse shi ba har sai da ya kai 'karshen maganarsa na ce."Ka yi hakuri don Allah, in sha Allahu zan gyara, maganar kuma na zo zan lalata maka gida babu wannan ajandar raina, da zuciya daya na shigo gidanka, sai kaine ma ka 'boye mini wasu abubuwa, amma hakan ba zai sanya na ce ka sake ni ba. Abu na biyu kuma ina kara gaya maka babu wata mace da zan yi wa biyayya, idan lallai sai na bi tsarin da matanka suka ginu akai ne to lallai ba ka shirya zama da ni ba, zan dai yi maka biyayya tunda kai ka ajiye ni. Sannan don Allah ina neman alfarma a wurinka idan zan samu."
Na kai 'karshen maganar ina dubansa. Ya ci kunu sai girgiza kafa yake yi da kyar ya ce."Wace irin alfarma ce?"
"Ina so na nemi mai aiki 'yar matashiya wadda za ta dinga taimaka mini, ka ga Allah Ya sanyawa lamarina albarka, ina so na yi amfani da damar kafin ta kubce mini."

Ya nisa kafin ya ce."Ita Iyami da take zuwa tana yi muku wanke-wanke da shara menene laifinta? Ba fa na son neman fitina Amina, idan ki ka ce zaki d'auki mai aiki ki ke kad'ai zai iya kawo hayaniya a gidan."

"Ba ka fahimta ba, zan samu wadda za ta taya ni aiki ne ranar girkina, tunda kun ce yara suna makara a makaranta, kai ma baka samun kulawa daga wurina, shiyasa na yi wannan shawarar."
"Ban yadda ba."
Ya fada hankalinsa yana kan wayarsa. Shiru wurin ya yi gabad'aya raina ya gama baci da abinda yake yi mini. Ya ce." Sai dai ki dauko wata daga cikin yaran dangi, zan yi miki wannan alfarmar. Amma ban yadda da d'auko mai aiki ba, bayan kuna da ita, na gaya miki babu wani tsari da za ki zo dashi da zumar rusa mini zaman lafiyar gida."

Ya tashi ya kama hanyar fita ba tare da saurari abinda zan ce ba. Yadda na fahimce shi ya fi tsoron Jamila fiye da anti Maimuna, ko meye dalilin haka oho! ko da yake 'yar kauye ce ai, Allah kadai ya san irin surkullen da take yi a gidan.
Gabad'aya sai ya jefa ni a cikin tunani. Ba yarinyar da zan je na nemi alfarmar iyayenta su ba ni kai tsaye sai Yusura yarinyar Sahura. To kuma idan na yi hakan ban yi wa kawata adalci ba, itama tana zuwa aiki, kuma yarinyar itace take d'awainiya da 'kananta tunda ta yi wayo.
Na yini ina nazarin yadda zan yi, domin fa zahiri idan ba mai'aikin nan na samu ba abubuwan ba za su gyaru ba, ni kuma ba zan fasa neman kudina ba, gashi daga farawa ta zuwa yanzu na samu kudi sun kai dubu dari biyu da hamsin, babu yadda za a yi na yi watsi da wannan damar da Allah Ya kawo mini, dole na yi wa marayun yarana digin da zasu amfana a gaba, ubansu bai bar musu komai ba.
Da yamma bayan la'asar yara duk suna makaranta, ina kan keke Sahura ta yi sallama. Cike da farinciki na tare ta. Ina fad'in." Wallahi yau yini na yi da tunaninki."
Ta zauna kan kujera tana cewa." Sai gashi Allah Ya kawo ni, daga aiki nake sai kawai na ce bari na karaso mu gaisa, kin san babu wata nisa fa tsakanin nan da wurin aikin na mu."
Na ce." Aikuwa kin kyauta mini wallahi bari na kawo miki ruwa.

Na kawo mata ruwa da d'an snacks da lemo na zauna ina fad'in." Me zan girka miki, na san kina tattare da yunwa daga ganinki."

"Wallahi a koshe nake, ai ba daga wurin aikin nake kai tsaye ba, mun je can gidan ogan mun duba mahaifiyarsa bata da lafiya, yau kwana biyu kenan da dawowarta daga egypt ganin likita, shine fa muke tattara mukaje dubata, mun ci mun sha ba na tare da yunwa."
Na ce." Ayya, to ko ruwa ai kya sha Sahura." Ta d'auki d'aya ta kai bakinta tana fad'in."To shikkenan."
Bayan ta ajiye ragowar ruwan na dubeta a nutse na ce." Sahura ya aikin fatan komai lafiya, na ga fa kin yi kumatu, ko ya yi muku karin albashi ne ."

Sai ta fashe da dariya tana cewa." Muna sa rai dai 'kawata, kin san ma na nemi alfarma a wurinsa za a mayar da ni daya daga cikin kamfanoninsa dake kusa da mu, saboda kafin na je Ina makara gaskiya, to da ya tambayi dalili sai na gaya masa, na kuma nemi alfarma."

Na ce." Hakan zai fi miki gaskiya, to Ina yi miki fatan alheri kawata, Allah Ya hadamu da rabonmu na alheri ."

Ta amsa da Amin tana bin falon da kallo. Ta ce." Su Kamalu suna makaranta kenan?"
"Suna makaranta wallahi, kin san wani abu kuwa?"
Ta girgiza kanta tare da mayar da hankalinta gare ni.

"Alfarma nake nema a wurinki, ban sani ba ko Idiris zai amince buk'atar tawa dai ta wucin gadi ce, idan ma zan samu a ba ni duka har aure zan fi son hakan."

"Wace alfarma ce wannan ki fad'a kai tsaye muddin Ina da iko, zan yi miki ai mun zama daya."
Yadda ta fadi maganar da karsashi, shine ya bani kwarin guiwar fayyace mata halin da nake ciki. Na d'ora da cewa." Sai kuma na yi tunanin yarinyar tana taimaka miki kema, sannan tana kula da 'yan'uwanta a duk lokacin da ki ka tafi aiki, shine dalilin da ya sanya na janye maganar a zuciyata."
Murmushi ta yi tare da dafa kafad'ata ta ce." Ki daina fad'in haka, idan ta ni ce yau ma Yusura ta dawo hannunki, ai da kai da kaya duk mallakar wuya ne, na san za ki kula mini da ita, maganar kula da gida da yara kuma, ba ki ji Ina gaya miki cewa wurin aiki za su dawo da ni kusa da gida ba, ai kin yi maganar akan ga'ba in sha Allahu kuma Abbansu ba zai k'i amincewa ba."
Ajiyar zuciya na sauke mai sanyi na ce." Na gode kwarai da wannan karamcin kawata, in sha Allahu duk sabgar makarantarta zan yi mata kokari sai ta dora daga inda ta tsaya tunda akwai makarantu anan din."
Ta nisa tana kallona." Kina ganin dai babu matsala a wurin abokanan zamanki ko?"

"Babu wata matsala Sahura, ai tunda maigidan ya amince magana ta kare, Jamila ce matsalar gidan itama na san inda zan yi da ita.

Ta sauke ajiyar zuciya a nutse ta ce.'" in sha Allahu rabbi ina komawa gida zan sanar da Abbansu duk yadda muka yi za ki ji ni a waya."
Na ce." To shikkenan, ina godiya k'warai, Allah Ya bar mana zumunci."

To cikin ikon Allah ba a sha wata wahala ba a wurin Idiris ba ya amince. Sahura ta kira ni a waya tana gaya mini na tura a d'auko yarinyar domin babanta ya amince tare da tabbatar mini da cewa ya yi farincikin hakan saboda shedar da ya yi mini yana da tabbacin yarinyarsa za ta samu ingantaciyar rayuwa."

Na ji dadin dawowar Yusura hannuna. Dama tun fil'azal yarinyar ta horu da aiki, shekararta goma sha hudu ta iya komai, sai dai ba duka nake sakar mata aikin ba, ina sanya mata hannu saboda yawan aikin ba irin wanda take yi ba ne a gidansu, na nan da yawansa. Ranakun da ba ni da girki kuwa, idan na fita na gaisa da matan gidan na koma wurina ba na sake fitowa, za mu dukufa aiki ni da yaran gabad'aya, lokacin makaranta da sallah ne yake tashinmu.
Kafin ki ce kwabo al'amurana sun 'bunkusa, duk sati sai na hada bacco na kaya sama da set talatin an kai Maiduguri. Tun ina lissafin dubu dari biyu uku hudu a cikin acct dina, sai na dawo lissafin miliyan. Al'amarin ya dinga ba ni tsoro da mamaki. Sai kawai na ajiye a raina cewa 'Allah ba yadda ba ya shirya lamarinsa'

Ranar da muka wayi gari da Azimi na farko. Baba Sule ya dira a gidan. Dama ya kan zo sa'i da lokaci da matsalarsa na d'auki kudi na bashi. Wannan karan kuma da buk'atar na saya masa kayan abinci ya zo, saboda wai Usaini ya gaya masa harkokina sun bud'e yanzu, gashi babu abinda na nema a gidan aurena, tunda dai kowa ya sheda gidan Alhaji Muntari da kulawa ta fanni abinci da suttura babu yunwa. A cewarsa neman da nake yi sai na wahalta musu tunda suna raye sai na samu lada."
Na riga na san son zuciyarsa sarai, idan ba haka ba mai zai sanya ya dinga zuwa yana cewa na bashi kudi, har binciken halin da nake ciki yake yi. Na dube shi a tsanake na ce." Baba ka koma gida in sha Allahu zan aiko muku da kayan abinci kai da Babanmu dama na yi niyyar hakan, amma don Allah ka dan rage zuwa, tunda ka ga ba ni kadai ba ce a gidan ina da kishiyoyi kada hakan ya janyo mini matsala."
Ya ce." To, zan rage zuwa idan kin san abinda ya dace, ni dana had'a auranki da Alhaji Muntari ai kamata ya yi ace ina da kaso a wurinki, amma sai na ro'ka k'i, ki dinga tunani"

Na ce." Ni fa ba wani abin nake samu da mutumin nan ba Baba, don Allah ka daina wannan maganar, duk alherin da nake yi muku daga aljihuna yake fitowa, saboda haka don Allah ka d'auke 'kafarka ba na so wani ya ta'ba muku mutumcinku."

Da kyar na rarrashe ya kama hanya ya tafi bayan na d'auki dubu biyar na bashi a matsayin kudin mota. Kwana biyar da zuwansa na gama had'a komai. Sai na fara tunanin yadda za a yi a fita da kayan domin kuwa matan gidan za su iya zargin na mijinsu ne na d'iba tunda yana ajiyesu da yawa. Da daddare aka shigo mini dasu lokacin kowacce tana wurinta, sai na yanke shawarar kawai a fitar dasu da daddare. Na kira Usaini a waya na gaya masa ya zo da adaidaita sahu ya d'auka kowa ya kai masa, na dora musu dubu talatin talatin akai.

Cikin rashin sa'a, lokacin da Usaini ya zo d'aukar kayan maigidan yana nan, tare da abokanansa a waje dama suna zaman shan ruwa idan sun yi asham sai su watse, abinda na cewa Usaini kenan bayan sallar asham zai zo. Minti goma

14 / 18