Gudun Aure 1 Complete Hausa Novel

Author :  Binta Umar Category :  Romance

Chapter   15 / 18

42K to 45K   out of 51.4K words

da fitar Usaini ya shigo d'akin Muna zaune da yara gabad'aya a falo, ina yanka wasu riguna su kuma suna kallon tibi. Ya zauna kan kujera, suka dinga jera masa sannu da shan ruwa, ya amsa a takaice. Na daga kaina na dube shi. Babu fara'a, a fuskarsa, zaman da ya yi ya nuna yana buk'atar magana da ni, ga kuma yara.
Na dubi Yusura a nutse na ce." Ku je d'aki ku yi kallon a can tunda da tibi. Suka tashi da saurin na ajiye almakashin hannuna. Na ce."Barka da shan ruwa."
Ya dube ni. "Barka dai, wanene yanzu ya fita da buhunhunan shinkafa da su taliya?"
"Usaini ne k'anina su Baba na sayawa."
Ya zuba mini ido na minti daya kafin ya ce." A ina ki ka ga kudin sayan wad'annan kayan abincin Amina, rankatakaf fa komai akwai kayan sun tassama dubu dari uku a yadda rayuwar nan take tsada."

Dariya na yi na ce.'' Ka raina wannan sana'ar da nake yi kenan, wallahi da ita na saya domin neman lada."
Ya hade fuskarsa. " Gaskiya ban yarda ba, idan kin sayi wani abu da kudinki, to za ki ta'ba nawa da nake ajiye muku idan kin yi hakuri ma ai duk shekara ina fitarwa da surukaina abin bud'e baki."

Cikin zuciyata na ce' an zo wurin' Zuciya ba ta da 'kashi zaman da ya yi, sai da na hasashi zargi a fuskarsa.
Na ce." To, Allah ne dai shahidi kuma shine zai yi mana hisabi bisa zargin da ka yi mini, ba zan yi rigima da kai a wannan watan ba, amma na barka da Allah ."
Daga haka ban sake magana ba, na d'auki almakashina na cigaba da aikin gabana.
Jikinsa a sanyaye ya tashi ya fita bai sake ce mini komai ba.
Duk yadda na so na daure zuciyata na cigaba da kyautatawa mutumin nan kasawa na yi. Da na kalleshi zan ji haushinsa ya turnukeni. Zama fa kawai nake yi dashi, har yanzu ba na jin sonsa a raina amma shine yake ko'karin gaya mini magana.
Ya dinga raragefe neman shiri, na share shi, da kyar ya shawo kaina na ha'kura na sakar masa jiki yana ta fad'in shi fa ba zargina yake ba, kawai su'btar baki ce ya yi.....✍️
*Gudun aure 1k on talgram via 0542382124...Binta Umar gtbank*
*07084653262*
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*



*TALLA!*
🌲🌳🌿☘️
*DA MAGANI A GONAR YARO!!*
*08089965176*
*07084653262*
*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*
[11/27, 10:17 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*

TEEMAH DATA SERVICES MTN
1GB @550
2GB @950
3GB @1450
4GB @1550
5GB @1700
CHECK CODE *323*4#
VALIDITY 30DAYS
CHAT@08112392177
CALL @08037026306
8037026306 fatima musa ibrahim opay
*TALLAH!*
🛍️ “Ko ba ki da niyyar siya ba, ki zo ki shiga ki kalla kayayyaki — wallahi sai kin bude ido! Ballantana kuma nasan za ki tashi da kaya saboda kyau da araha.” ✨
🌸✨ “Shigo duniyar da kyau da jin daɗi suka haɗu — daga kyawawan laces na alfarma, Atamfa , abaya masu salo, zuwa kayan ado masu kyalli, kayan girki na zamani da sauran ƙarin abubuwa. A Meerah B Collection , muna adashen kayan kitchen daily 1k to pack 100k items weekly Monthly ✨🌸We are sale kitchen items, electronic, WE ALSO DEAL WITH CONTRIBUTE monthly weekly daily after 10 days for kitchen items or electronic gaba daya wanna package 60k nake had'a sa zaku iya mallaka ta hanyar adashi
https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t

*1k on talgram via 0542382124...Binta Umar gtbank mutanan nijar dala dari katin Airtel. Ga masu karatu a arewa book akwai more peges domin na yi nisa a can din.*
*07084653262*
*08089965176*
*@arewa books*
*Bintuumarabbale.*
*Free pege*
*18*
Wannan ya wuce da wasu kwanaki wani abu bai sake faruwa ba, tunda Ina iyakacin bakin kokarina wurin ganin na fita hakkin maigidan da abokanan zamana a duk ranar girkina. Sosai Yusura take taimaka mini da wasu ayyukan, itama Iyami tana nata bakin ko'karin. Goman karshe hada-hada ta yi yawa. Ya Falmata ta sake jibgo mini wasu ayyukan tare da sharad'in ana buk'atarsu kafin sallah. Babu abinda nake hangowa sai ruwan kudin da zan samu. Wannan dalilin ya sanya na hana kaina sukuni bacci arziki ba na yi. Yanzu haka kekuna biyu gareni ni na hau daya Yusura ma ta hau tunda ta fara iya wasu abubuwan ina nuna mata. Kamalu da Yusi suna aikin jera stone's da sauransu.
Ranar girkina kuwa Iyami na sakarwa ragama duk da na san da cewa ba haka tsarin gidan yake ba. Iyakacinta shara da wanke-wanke, sai zuwa cefena da 'yan aike aike, amma ni kam har girkina na bar mata, muka yi da ita zan dinga bata dubu biyu kullum idan zata tafi. Ita kuma Yusura la'asar ta na yi zan tashe ta ta je ta feraye doya ta soya ita na dorawa alhakin hakan.
Anti Maimuna ba ta ta'ba tankawa ba ila iyaka idan an kammala ta zo ta dibi abinci. Babu korafi a tsakaninmu tana dannewa koda taga abinda bai yi mata ba, gashi dai itace uwargida amma bata neman fitina da kowaccen mu, dalilin da ya sanya ma kenan na sayi shadda mai tsada yadi goma sha biyar na bada yadi bakwai a dinkawa Kamalu da Yusi sauran Kuma nake da kudirin yi musu d'inki na gani na fad'a ita da Yusura duk da cewa maigidan ya yi musu kala uku Yusura da su Kamalu bai bambamta da yaransa ba, hakan ya sake ba ni karfin guiwar yi wa 'yarsa duba da irin kara da kawaicin da uwarta take yi mini, uwa uba kuma yarinyar tana kaunar Yusi sosai, komai ka ji tace Yusifa.

Yau bayan shan ruwa da kadan ina bandaki na ji sautin muryar Jamila a falona.
Da sauri na cud'a jikina na zuba ruwa na fito. A gurguje nake yi komai dalili girkina ne, ba na so kuma maigidan ya shigo ya riskeni a hargitse, dama na fahimci kwana biyu a wuya yake da ni, dalilin baccin da yake riskata ina yi bayan ya gama zaman majalisarsa ya shigo, duk ranar girkina baya samun wani Abu a wurina saboda mugun gajiyar da nake yi. Shiyasa yau na sauka daga kan keke da wuri domin ina so na faranta masa.
Tana tsaye sai fad'a take yi wa Yusura. Ita kuma yarinyar ta yi shiru idonta ya ciko da hawaye. Raina ya baci ainun. Na ce." Ke kuma menene haka don Allah za ki tasa yarinya a gaba kina fad'a mata wasu maganganu ko zamanki take yi ne a gidan?"
Ta kalleni kafin ta ce." Amma dai kin san abinda ki ke yi ba kya kyautawa, ya za a yi ki dinga bawa wannan yar yarinyar aikin da bata iya ba, idan ita Maimuna ba zata iya yi miki magana ba to wallahi ni ba ki isa ba, ba zai yiwu mu dinga cin abu da 'karni ba, domin koyaushe doyar da yarinyar nan take yi ba ta soyuwa zubarwa muke yi ni da yara, wallahi ba zai yiwu ba dole maigidan ya ji abinda yake faruwa domin tun wuri ya yi wa tufkar hanci."
Na ce." To sai ki bi shi ki gaya masa ai yana waje ba nisa ya yi ba, idan ya shigo sai ki sanya ya sake ni, ko ya kori Yusura tunda ta soya doya ba ta soyuwa ba."

Ta bude baki kenan za ta yi magana ya shigo. Ganinta a tsaye ya sanya ya ce." Da azimin ma sai kun yi mini masifa a gida, menene kuma?"

Ta fara gaya masa abinda ya kawota. Ya dube ni tare da cewa." Amina ba karya Jamila ta yi ba doyar nan bata suyuwa karni take yi yau ni kaina ban iya ci ba wallahi, bayan kunyar da ki ka ba ni a cikin abokai, ashe dama ba ke ki ke yin aikin nan ba?"
Shiru na yi masa ban tanka ba. Ya dubeta tare da cewa" Tafi wurinki zan yi maganin abin." Ta juya ta tafi ba ta sake cewa komai ba.
Yana shigowa falon na sake daure fuskata. Yaran suka tashi suka bar wurin.
Bai ce mini komai ba, ya wuce cikin kuryar d'aki. Minti biyu na ji yana fad'in." Ina ki ka ajiye mini dabinon nan dana shigo dashi kwanaki?"
A cunkushe na ce." Ka duba cikin doruwa."
Gabana ya buga da karfin gaske tuna abinda na ajiye a dorowar. Da sauri na tashi na shiga d'akin na same shi a tsaye hannunsa rike da kwalin maganin, daya hannun kuma robobin dabinon ne.
Jikina ya yi mugun sanyi. Kai a kasa na nufe shi.
Ya dubeni ya jijjiga kansa. Cikin mamaki da al'ajabi ya ce." Maganin hana d'aukar ciki a gidana Amina, Ashe ha'intata ki ke yi dama, ina ta wahalar banza wuri zuba kwaya-kwayena ke kuma ki sha magani su tsinke su bi rariya, dama da wannan nufin ki ka shigo mini Amina? me ya sa ki ka yarda da haihuwa da tsohon mijinki wanda bashi da ko kwabo sai ni da Allah Ya rufawa asiri ki ke gudun had'a zuri'a da ni bayan tun kafin mu yi aure na gaya miki ni mutum ne mai burin tara zuri'a."
Cikin sanyin jiki na ce." Wallahi ba haka ba ne, na yi hakan ne domin ni da kai mu huta, mu mori amarcinmu, amma mai zai sanya na guji haihuwa da kai bayan kana da nasaba, kuma Allah Ya rufa maka asiri, idan na yi haka ai na yi butulci ga Allah, don Allah ka yi hakuri."

Babu sassauci a tare dashi Ya ce." Watanki takawas a gidan nan Amina don Allah ki gaya mini amarcin da ki ka bari na ci dake, tun baki fi sati biyu ba a gidan nan ki ka daina ba ni kulawa, bayan kin san ni din namaji ne mai buk'ata, kin fi bawa neman kudinki muhimmanci, a gaskiya wannan lamarin ba zai tsaya iyakacin ni dake ba, dole waliyinki Sule ya ji abinda yake faruwa domin akwai cutarwa a ciki."
Jin haka ya sa na fashe da kuka ina fad'in." Don Allah kada ka fitar da maganar nan wallahi zan gyara, magani kuma daga yau na daina amfani dashi, ka yi hakuri ba zan sake ba."
Kuka nake tukuru, harda face majina. Sai jikinsa ya mutu, ya riko ni muka zauna kan gado yana cewa." Tunda wannan shine karo na farko na yi hakuri, kuma kin yi alkawarin ba za ki sake ba, amma ina so yau ki ba ni kulawa ta mussaman domin a mutukar buk'ace nake dake."
Da sauri na ce." In sha Allahu na yi alkawari ba zan sake shan magani ba, kuma san dinga baka kulawa." Ya girgiza kansa yana bina da wani shu'umin kallo.
Saurin fahimtarsa da rashin riko ya sanya nake jin zan iya cigaba da rayuwa da shi duk da cewar har yanzu zuciyata bata gama aminta dashi ba.
Dinkin da na yi wa Salimat ya d'agawa Jamila hankali, ta fito tana ta zage zage da neman fitina, tana kiranmu da munafukai ni da Anti Maimuna. Babu wadda ta kulata a cikinmu. Hakan ya k'ara yi mata ciwo, da maigidan ya dawo ta gaya masa. Ya shigo yana tambayata na ce masa hakane na yi wa Salimat da Yusura d'inki iri daya.
Ya yi shiru na minti biyu kafin ya ce." Kema Amina ba ki so zaman lafiya, mai zai sanya ita jamilar ki kasa yi mata kawaici, itama ai sai kisa yaronta daya zata ji dadi."
Saboda ba na so maganar ta yi tsayi na ce." Allah Ya kaimu wata shekarar sai ayi, amma ka gaya mata d'azu da ta fito tana zaginmu ba tsoronta ba ne ya sanya na yi shiru, saboda muna watan Azimi ne, wallahi ta kara zagin iyayena sai na yi mata duka."
Yana dariya yake cewa." Ke yanzu kina ganin Jamila zata daku a hannunki?"
Na ce." Abu ne mai sau'ki." Sai ya tashi ya fita yana dariya tare da cewa." Amina rigima kenan."
Washe garin sallah Yusura ta tafi gidansu don tun kafin sallar take ce mini a can za ta yi. Kamalu har ya yi naci da magiya ya gaji, so yake na bar su su je gidan Gwaggwo su yi sallar a can na ce a a dalili ba na son abinda zai sake danganta shi da unguwar muddin ba da ni ba, balle har su hadu da Saminu. Haka nan ya ha'kura, gashi ba wani shiri yake yi da yaran gidan ba, sai ya sake takura sosai, shi Yusi Yana can wurin Salimat a can ma yake wanka kaf kayan sallarsa suna wurinta. Anti Maimuna ce ta tursasani barinsa ya bi yaran gidan zuwa gidan kakarsu uwar mijinmu Hajiya dogara. Ba yadda na iya da ita, saboda zahiri Ina ganin kimarta ganin yadda take mu'amulantata a gidan. Kamalu ya dinga murna da tsalle, Yusi yana kyalkyala masa dariya. Da zasu tafi sosai na yi masa fada akan ya kiyaye ya kula banda rawar kai, kuma babu ruwansa da Turzumi tunda ba shiri suke yi ba. Ya yi mini alkawarin zai kula.
Sai dai kuma sai da na yi dakacen barinsa zuwa gidan Hajiya Dogara dalilin satar da tace ya yi mata.
Suka dawo gidan kowa ransa babu dadi, domin tun a can Turmuzi ya Tara 'yan unguwa suka ture shi suna yi masa ihun b'arawo.
Yadda ya shigo a firgice shine abinda ya tabbatar mini da cewa babu lafiya. Yana zama ya fashe da kuka! Hawaye masu tsananin gudu suka dinga tsere a kumatunsa.
Ina ji yo hayaniyar yaran gidan daga waje muryar Jamila tana ta tashi. Salimat da Yusi suka shigo. Ta zauna a sanyaye tana cewa." Wallahi bai d'aukarwa Hajiya Dogara kudi ba, ni na rasa ma a inda ta ji cewa Yana sata. Abinda ma tunda muka je gidan bai zauna ba Yana kofar gidan a zaune, sai da zamu ci abinci ne na ce a kirawo shi, wai amma tana bud'e jakarta ta duba ta ga babu dubu daya sai tace shine ya d'aukar mata. Sai da zamu tawo tukkuna tana daga kasan tabarma ta ga kudinta ashe anan ta ajiye.
Amma sai ta yi shiru ba tace komai ba, kuma tana ji fa Turmuzi ya Tara Yara suna yi masa ihu amma bata hana shi ba, kuma bata gaya masa cewa taga kudin ba."
Murmushin takaici kawai na yi na ce." Salimat tashi ki je kawai Allah Ya kyauta."
Ta tashi jikinta duk a sanyaye ta fita.
Yusi ya dube ni, murya na rawa ya ce." Mama me yasa kowa ya tsani Yayana ne?" Sai ya fashe da kuka ya kwanta kasan kafet yana rerashi."
Na dubi Kamalun da lokaci guda ya firgice. Na ce ka gaya mini gaskiya ka d'auki kudin Hajiya dogara ko baka d'auka ba?"
Ya sa hannu ya goge hawayen da yake zuba a fuskarsa. Ya ce." Wallahi ban d'auka ba Mama sharri ta yi mini."
Na girgiza a kai, a raunane na ce." To shikkenan ni ma na aminta baka d'auka ba, yadda yanayinka ya nuna, ka share hawayenka ka ji ko."
Ya sauke ajiyar zuciya tare da sanya duka hannuwansa biyu Yana goge fuskata.

Koda maigidan ya dawo ban ce masa komai ba. ba wai don abin bai yi mini ciwo ba, sai don kimanta mahaifiyarsa. Amma zahiri da wata ce ta yi mini haka inaga sai na daureta. Kuma maganar ban san abinda zata haifar ba tunda Ina kan dokin zuciya, kuma uwa ta zarta komai. Ina fata hakan dai ya zama na farko domin idan ta sake faruwa ba na tsammanin zan yarda.

Na san ya ji labarin abinda ya faru, amma bai tare ni da maganar ba, sai ya ja bakinsa ya yi shiru, hakan ya k'ara
sanya ni karatun ta nutsu, tunda bashi ya haife shi ba, ai ba zai damu da abinda akayi masa ba, wata'kila shima ya yarda da zargin da akayi masa tunda shi Kamalu a kuyarsa ta riga ta yi kuka.
Uku ga sallah 'yan gidanmu suka zo kaf dinsu har da yaran Baba Sule. Su Hadiza yanzu an yi hankali an daina giggiwa yadda na lura ma kamar shakka take yi ganin yadda Allah Ya rufa mini asiri. Zuwansu bai daga mini hankali ba tunda muna da abinci wadatacce kajin sallar da muka soya suna da yawa ko rabi ban ci a kasona ba. Ina gama yi musu abinci na

15 / 18