Author : Binta Umar Category : Romance
can.
Na ce."Ai da zan dake shi da tuni na dake shi Yusi, addu'a na ke yi masa, Allah Ya shirye shi." Ya saki ajiyar zuciya Yana fad'in." Bari na je na kirawo shi."
Ya fita da sauri.
Minti uku da fitarsa Hamusu Ya shigo. Muka gaisa ya ce." Tun jiya na so na shigo mu tattauna Allah bai nufa ba, da yake ban dawo da wuri ba, Gwaggwo duk ta sheda mini abinda ya faru, anti Amina jama'ar gari suna ta zaginmu akan mun sakar miki wahala, don Allah wannan karon kada ki ce a a, ki ba mu yaran nan, su koma hannunmu da zama, komai Yana da lokaci, kuma in sha Allahu yaran nan, sai duniya ta amfana dasu."
A nutse na ce." Ban ki maganarka ba Hamusu, kuma ban ce kun gaza mini ba, ni dai har duniya ta nade babu kalmar zagi ko 'batanci akanku, duniya ban ga abinda za ku yi mini ba Hamusu, domin Iya k'auna kun nuna mini. Ba wai ba na son ba ku yaran nan ba ne, ina tausayawa Gwaggo da shekarun tsufa suka cimmata. Ta rainin yaranta cikin nutsuwa da kwanciya hankali, ba zai yiwu ace kuma yanzu da take buk'atar kulawa a kai mata wahala ba. Ku barni da yaran in sha Allahu babu abinda zai gagare ni."
Ya ce." Ai kin san na kusa aure, zaman da yaran za su yi a hannun Gwaggo na hucin gadi ne, daga zarar na yi aure da 'yan watanni sai su koma hannuna da zama, in sha Allahu zan ri'ke su da kyau, haka nan yarinyar da zan aura na sanar da ita duk abinda yake faruwa kuma ta ce ta amince za ta ri'ke su."
Na dube shi cikin nazari. Wato wasu lukutan maza suna da gajeran tunani. Ta ya za a yi amarya daga aure ta fara jigila da yaran ma da bana mijinta ba. Akwai matsala babba wadda shi ba zai fahimta ba a yanzu sai zama ya yi zama tukkuna. Yanzu yarinyar zata furta karya domin tabbatuwar auran, idan ta ga ta shiga daga ciki sai ta canza alkibula.
"Hamusu wannan karon ma dai Ina ba ku hakuri, kuma ma dai har gida zan zo wurin Gwaggwo mu tattauna, aure zan yi nan da sati biyu in sha Allahu, kuma wanda zan aura ya amince mini, zai kula mini da yaran nan, ba ni na nuna ina son hakan ba, shi da bakinsa ya furta, ka ga kuwa bai kamata mu watsa masa kasa a Ido ba, sannan ina so da ni da yaran gabad'aya mu yi nesa da unguwar nan, Kamalu ya canza abokai, muna cigaba da addu'a sai ka ya dabi'un nasa sun canza gabad'aya.
A sanyaye ya ce.' Anti Amina surutun mutane shi yake damuna wallahi, Baba Sule sai ka ce babu dangatanka duk inda ya zauna sai ya zagi Gwaggo, ya aibata mu, kuma kin ga ba lefinmu ba ne, duk talaucincmu ba zamu kasa ri'ke yaran nan ba."
Cikin takaici da b'acin rai na ce." Ka yi hakuri Hamusu, don Allah kada ka sanya damuwar Baba Sule a ranka, ni kaina bai barni ba, kuma Allah da zuciya yake amfani, kai dai ka cigaba da yi musu addu'a. Komai zai zama tarihi."
Ya ce." In sha Allahu rabbi anti."
Yaran suka shigo d'akin. Gabad'aya muka dube su. Da gaske dai d'ingisa k'afar yake gefanta ya kumbura kadan. Ya zube a bakin k'ofa, murya na rawa yake gaishe da kanin Uban.
Bai amsa ba hankalinsa yana kan kafarsa ya ce." Garin tura kurar ruwan ka ji ciwo, domin an ce kaine jami'i wurin d'aukar kurar ko?
Ya girgiza kansa yana fad'in." Ba ni ba ne, Shamsu ne ya tura kurar ni kuma na d'auki jarakuna biyu, muka nufi kasuwa, sai Saminu da ya cire wili da taya ya sayar."
Ya girgiza kansa tare da furta." Allah Ya shirye ku. Ya dube ni kaina a kasa domin duk sanda na kalli yaron Ina ji kamar na fasa ihu.
Ya ce." Bari na je na kira Abdullahi mai chamis ya zo ya duba shi.
Na ce." Anya Hamusu kafar nan, ba targad'e ba ne, dukansa fa suka yi 'yan sandan."
Ya ce." Ai dole su dake shi tunda ya yi yun'kurin guduwa, idan suka riga suka kamaka, kawai ka mika wuya.
Sai ya fashe da kuka Yana cewa." Ban yi yun'kurin guduwa ba, wani daga cikinsu ne ya rike ni ya dinga dukana da takalmin kafarsa."
Babu wanda ya tanka masa a cikinmu.
Hamusu ya tashi ya fita. Ni kuma na cigaba da abinda nake yi. Sai kawai na tsinkayi muryarsa yana cewa." Mama ina kwana?"
Na dube shi a nutse na amsa.
Ya yi shiru fuskarsa duk hawaye a bushe. Ya furta." Don Allah ki yi hakuri kin ji."
Na ce." Ai na ha'kura tuntuni."
Sai ya rarrafo kusa da ni, yana fad'in." Ki dake ni, idan hakan zai sanya ki daina damuwa a kaina, jiya na ga ba ki yi bacci ba, kina kuka."
Na ce." Yaushe ka ga ina kuka Kamalu? Idan ka ce ban yi bacci ba wannan na yarda, amma ban yi kuka ba."
Ya yi shiru yana sauke ajiyar zuciya.
Na ce." Na yafe maka, Kai ma ka yi mini alkawari ba za ka sake ba."
Da sauri Ya ce.'' Wallahi ba zan sake yi ba, kuma ba zan kara kula Saminu ba."
Na ce." Allah Ya kyauta, Kai be Yusi d'auko kofi a kwando ka je ka sayo kunu, ina da sugar, sai ka wuce gidan awara."
Da sauri ya yi abinda na umarce shi, ya kar'bi kudin ya kama hanya ya fita da saurin gaske.....✍️
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
[11/23, 10:21 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*TALLAH!*
'Yan uwa
Barkanku da zuwa FAMAS SCENTS OF LEGENDS,
duniyar turarukan wuta masu kamshi na musamman mai samar da nutsuwa da kwanciyar hankali.
Mun tanadar muku da turarukan wuta masu dadin kamshi kamar su
Sandal flakes
Hawee
Gabgab
Halut
Dorot
Coconut chips
Dufr(farce)
Black khumra
Brown khumra
White khumra
Oil perfumes da
Body sprays
Dan turara gidajenku,tufafinku da jikinku.
Ga duk mai buqata zai iya tuntuban mu ta lamba kamar haka
Call/WhatsApp
07037489958
Location:Gonan Ganye,zaria
Kaduna state
Nationwide Delivery
*DATA Mai karfi da quality 💯*
TEEMAH DATA SERVICES MTN
1GB @550
2GB @950
3GB @1450
4GB @1550
5GB @1700
CHECK CODE *323*4#
VALIDITY 30DAYS
CHAT@08112392177
CALL @08037026306
8037026306 fatima musa ibrahim opay
*@Arewa books*
*Bintuumarabbale*
*Ga wad'anda ba su san jira akwai more peges a arewa na gode🙏*
*Free pege*
*14*
Hamusu ne ya yi duk abinda ya kamata akan rauninkan dake jikin Kamalu. Abdullahi mai chamis ya zo ya duba shi sosai, ya bashi maganin da ya dace. Sannan ya bi bayansa yana tambayarsa abinda za a ba shi.
Da k'yar na lallab'i Yusi ya shirya ya tafi makaranta. Babanmu ya leko yana fad'in." Ina Kamalun yake ne, ban ji motsinsa ba."
Na ce." Gashi nan, a kwance yana bacci, Abdullahi ne ya ba shi magani.
Ya shigo d'akin sosai yana duba kafartasa. Ya girgiza kansa babu kuzari a tare dashi ya furta." Allah Ya taikaita muku wahala."
Na amsa da "Amin Ya Allah."
Ya dube ni kafin ya ce." Maganarki da Alhaji Muntari tana nan ko?"
Kai na d'aga a hankali na ce." E, Baba." Sai ya kama hanyar fita yana fad'in." Allah Ya tabbatar miki da alheri."
Na amsa da "Amin." Cikin sanyin jiki.
Ummansu Hadiza ta le'ko ta duba jikin Kamalu, mun d'an jima da ita muna tattaunawa kafin ta fita daga d'akin. Na dinga zuba Ido ko zan ga Anti Sakina ta le'ko, ta duba shi, tunda dai ta san bashi da lafiya, amma shiru ba ta le'ko ba, kuma ina jin kayaniyarta da yaranta a tsakargida.
Na nemi wayar Sahura domin tunda na rakata neman aiki ba mu sake had'uwa ba, ko a waya.
Tana d'agawa take fad'in." Kina raina wallahi sis, kuma yau nake cewa zan kira ki kwana biyu network Yana yi mana wahala a unguwarmu."
Na ce." 'Kwarai kuwa, kuna da matsalar network a nan wuraran, ya gida, da yara?"
"Wallahi duk suna lafiya, ina su Kamalu fatan kowa lafiya."
Na ce." Alhamdullahi wallahi, kin ga har na je bikin Babandi na dawo, anti Yagana tana gaisheki da kyau."
"Ina amsawa wallahi, ina son zuwa garin nan k'awata."
Na ce." Sai ki bari idan auran Fadila ya tashi sai ki je."
Dariya ta yi tana fad'in." Ubangiji Allah Ya nuna mana, ai kaya ma zamu had'a ni da Yara mu je mu cashe da biki."
Dariya na yi, a hankali na ce." Sahura aure zan yi nan da sati biyu masu zuwa."
Da mad'aukakin mamaki a tare da ita ta furta "Aure sis!"
Na ce." E, wallahi Sahura."
"To ya aka yi ki ka canza shawara da gaggawa haka, wanene wannan da lokaci guda ya canza ki?"
"Ba wani ba ne Sahura Alhaji Muntari ne dai
wanda na baki labarinsa ranar da na zo gidanki...... Gabad'aya na kwashe duk abubuwann da suka faru na gaya mata, domin bahaushe yana cewa 'Abokin kuka shi ake fadawa mutuwa'
A sanyaye ta ce." Sis, kin yi bincike sosai a kansa ko? Ni fa ba na son irin wannan gaggawar a sha'anin aure Amina, ki nutsu don Allah, kada wata matsalar ta sanya ki jefa rayuwarki cikin garari, na tsorata da na ji kin ce matansa biyu yaransa takwas, ba ki hango matsala ba."
"Sahura ya zan yi? wallahi kaina ya kulle gabad'aya, gida sun takura mini, Kamalu Yana nema ya fi 'karfina, wannan ce kawai mafita a gare ni. Idan na ce ba zan yi aure ba, zan je na kama haya na zauna jama'a su canza mini manufa, ya zanyi ne Sahura, dole ko ba na so na amincewa mutumin nan domin na rufawa kaina asiri, yadda ya nuna alama kamar akwai nagarta a tare dashi, da bakinsa ya furta zai ri'ke mini yarana ba ni ce na nema ba, shiyasa na amince da auransa."
"To, shikkenan sis, amma don Allah ki tsananta da addu'a akan lamarin, Ubangiji Allah Ya tabbatar miki da alheri, Allah Ya sa abinda muke hasashe a kan mutumin ya tabbata."
Na ce." Amin Ya Allah Sahura na gode sosai, in sha Allahu ai kafin d'aurin auran zan zo mu tattauna."
"To Allah Ya nufe ki, sai ki zo ranar da ba aiki, mu yini muna hira."
Na yi dariya tare da ce wa." Sahura Ya aikin kuwa? Ina fatan babu wata matsala."
"Wallahi babu matsala, ai na gaya miki na fara a sa'a, sati daya da fara zuwana ma'aikatar ya yi mana rabon kayan abinci. Harda kudin cefane.
Na ce." A lallai, ma sha Allah, na taya ki murna, Allah Ya sa a d'ore."
Na fad'a cikin barkwanci.
Tana dariya ta ce." Za a dore in sha Allahu rabbi, ai kamar yadda ya gaya mana idan mun bi dokokinsa, zai kyautata mana, wallahi akwai alamun tausayi a tare dashi, shiyasa nake ko'karin ganin ban sa'ba dokokin aikinsa ba."
"Ai kam Sahura ba girin-girin ba, Inji hausawa ta yi mai, Alhaji Tajo ne fa, ni dai ba na yinsa, tunda ya yi sanadin uban 'ya'yana."
Ta dinga kyalkyala dariya tana fad'in." Ho 'kawata, idan ki ka tsani abu, duk inda makusa take sai kin nemo, wallahi mutumin arziki ne, ga kyauta da sakin fuska ga ma'aikatansa."
Na ce." To a ba ni hakkin mijina kawai a zauna lafiya, shekara kusan goma yana yi masa bauta, ai ya ci ya bashi fansho."
Ta ce." A rigimarki ba, ai ko gomnati ce sai mutum ya zartar shekara goma suke biyan fansho da garatuti, balle kamfani da babu wannan yarjejrniyar. Amina nifa na fi zargin akwai wad'anda suke cin amanar mutumin nan a bayan fage shiyasa ki ke ganin kamar bashi da Imani."
Na ce." Ai duk wanda yake aiki a k'arkashinsa ba zai ga aibunsa, mussaman idan Ya na amfanuwa dashi, shiyasa idan na fadi abinda ya yi mana sai jama'a su karyata ni, ke dai kin sani, ba sharri ba ne ko?"
Ta ce." Na sani, shiyasa ma ai ki ka ji na ce miki akwai masu ha'intarsa a bayan fage, wallahi na san da saninsa ba zai wulakanta wanda yake moruwa dashi ba."
Na ce." Lallai Sahura harda rantsewa akan mutumin da ba ki jima da saninsa ba, to shikkenan mu bar maganar kawai, ba za ki fahimta ba ai."
"Ai dole mu barta sis, tunda ba kya so, amma dai Ina kara tabbatar miki da nagartar mutumin, idan mu'amula ta had'aku, za ki gazgata cance na."
"Uhm" Kawai na ce' "Kin ga gyaran jiki, nake so na fara tun yanzu, bahaushe ya ce' Idan kana da kyau ka kara da wanka, dukda breast dina ba sa samu wata babbar matsala ba, amma dai Yana da kyau na kara gyarasu, a cike suke sai dai sun dan rankwafa, nan ba sosai ba, Ina so ki bincika mini maganin gyaran nono mai kyau, dana sanyi, da na'ima, ina buk'atar na matsi sadidan, amma harbel nake so, ba na buk'atar na bature."
"Aikuwa gyaran Yana da kyau kawata, don ma Allah ya yi mini kyawun suffa, wallahi da yawa wasu ba za su yarda kece ki ka haifi su Kamalu ba, kamar wata budurwa fa."
Dariya na yi na ce. Lallai Sahura, ke ma abinda za ki fad'a kenan, to na gode sosai, dukda haka dai zan gyara jikina, kin ga ina da kishiyoyi, Yana da kyau na je gidan zam-zam."
Ta ce." Kaya ya tsinke a gindin kaba, shekaran jiya na ji Maman Anisa tana waya da wata mai magani GARKUWAR MATA sunanta. Maman Anisa za ta cire yarinyar da take goyo daga nono shine tace ta had'a mata magani. Gaskiya duk abinda na ga Maman Anisa ta saya nagartacce ne, har take tabbatar mini da ingancinsa domin yawanci 'yan gidansu a wurin matar suke sayayyan kayan gyara, in sha Allahu zan karbo miki lambarta sai ki kira ta kuyi magana ko ta whasap ne, tana garin Kano tana kuma tura kayatanta kowane gari. Duk wani na'unin maganin matantaka idan kina bu'kata akwai wurinta cikin farashi mai sau'ki da rahusa, don har sari suke bayarwa.....08089965175 a yi magana kai tsaye ta wannan lambar..
"To yawwa, don Allah Sahura ki yi kokarin karbo mini lambarta yau din nan, sai ki turo mini, ina so mu yi magana da ita da wuri ta Aiko mini na fara amfani dashi." Ta ce." In sha Allahu rabbi yanzu zan shiga gidan da kaina na kar'bi lambar.
Sallama muka yi, na ajiye wayar na tashi domin gyara d'akin, da tunanin lamarin da yake fuskanto ni, ina ro'kon Allah Ya wanzar mini da alheri.
Ina tsaka da aiki Ya kira ni. Dama na yi hasashen hakan, wata'kila Yana ta kira lokacin muna waya da Sahura.
Na zauna a nutse na daga wayar da sallama a bakina.
Bai amsa sallamarba ya fara cewa." Na jima ina trying lambarki sai ace busy Amina ke da wa kuke wa da sanyin safiyar nan."
Yanayin yadda ya furta maganar a cunkushe shi ya sanya jikina ya dan yi sanyi. 'Wato shi kuma mai titsiye ne'
Na ce."Sahura ce kawata, muke tattauna yadda sha'anin bikin zai kasance."
Sai ya sauke ajiyar zuciya. Ya sassauta sosai ba kamar farko ba. Ya ce." Ai na d'auka wani ne yake hure miki kunne da sanyin safiyar nan."
Na ce." Wani kuma Alhaji, ai babu shi sai kai, domin zuciyata ta gazgataka akan abokin rufin asirina."
Murmushi Ya yi wanda sautinsa ya fito har sai da na ji a kunnena, cikin jin dadi Ya ce." Kin gama faranta mini rai my love, ashe na samu wannan matsayin ba a gaya mini ba sai da aka gama ja mini aji ko?"
Dariyar da babu nishadi na yi na ce." Ka kai makura a zuciyata, Kuma ina kyautata zato na alheri a kanka, ba zan yi kaico ba."
Ya saki dariyar nishadi ya ce." Na yi godiya sosai da wannan yabo da na samu daga wurinki, Allah Ya ba ni ikon kula daku bakidaya."
Na amsa da "Amin Ya Allah."
Ya ce." Yanzu wace rana ki ka tsayar ta d'aurin aure?"
"Juma'a ta sama ai hakan ya yi ko?".
"Ya yi sosai, dama ke nake jira, don ni ko yau a daura ba ni da matsala a shirye nake."
Murmushi kawai na yi. Ban ce komai ba. Ya ce." Zan tura miki kudin gyaran jiki, da hidimar da za ki yi, sannan na sanya miki kayan d'aki da labulaye, abinda dai da
za ki zo dashi kad'an ne. Don gabad'aya na canza musu furniture din gidan.
"Na gode sosai Alhaji Allah Ya 'kara arziki."
"Amin Ya Allah, zan shigo yau da daddare sai mu sake tattaunawa ko?"
"To shikkenan, Allah Ya kawo ka lafiya."
Muna yin sallama da minti biyar message ya shigo a waya. Ina dubawa naga kudi ne ya turo mini har dubu dari da hamsin. Ban yi mamaki ba, tunda tun farkon haduwarmu ya nuna yana da kyauta da sakin hannu.
Wani abin haushi da takaici, Ummansu Hadiza kuma sai ta tsiri jin haushina. Da farko duk abinda zan zartar sai na nemi shawararta amma ganin yadda ta fara nuna halin ko'in kula da lamarin auran ya sanya na janye jikina. Nake gabatar da abubuwana kai tsaye tunda ni ba yarinya ba ce. Abinda dai yake ba ni mamaki shine; Yadda take nuna mini hassada a duk abin alherin da zai tunkaro ni. Da farko ta nuna sha'awarta da lamarin, amma ganin yadda komai yake tafiya gwanin sha'awa sai bakinciki ya shigo ciki. Hadiza ta zo gidan tana fad'in "Dukda dai ba sanya mu a sha'anin ba, muna da abinda fad'a, mutumin nan dai bashi da wani kuzari a gidansa, matansa sun fi karfinsa, sannan kuma Yana neman mata, kowa ya san haka don har ciki ya yi wa wata yarinya, don dai yana da kudi ne maganar ta mutu."
Ban girgiza ba, ban kuma tanka mata ba. Na cigaba da shirye-shirye na, ina kara mi'ka wa Allah lamarin, gefe guda Gwaggo tana kara kwantar mini da hankali da fatan alheri. Duk wani gyara na yi, na ciki da waje. Na sayi abubuwan da ba ni dasu. Domin da kansa ya dinga gaya mini idan kudin ba su isheni ba na yi masa magana zai kara mini. A iya tunanina dubu dari da hamsin da ya turo mini harda lefe, abin mamaki sai gashi saura kwana biyar d'aurin aure danginsa sun kawo mini akwatina uku cike da kaya manya da takalma da mayafai, wallahi ko wata budurwar albarka.
Takaici ya kara cunkushe zuciyoyin massadana. Ita Ummansu Hadiza bakincikinta a kaina baya b:oyuwa, amma anti Sakina watsar da makamanta ta yi ta zo har dakina tana gaya mini