Gidan Gandu Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  BieBie Category :  Romance

Chapter   29 / 29

84K to 85.7K   out of 85.7K words

don ban taba yi ba sai a kanki, Ashe tsoho ya rigani hango hakan, nd bansan me zanyi ba idan be hadani da ke ba, kece Zabina, kinji?tace Nagode, what kingode? Ke matar likita, wannan kunyan naki na shiga rayuwata, yanzu fa kika gama min wanka, y isit so dificcult to look me in d eye nd tell me u love me? Zan fayi addua Allah ya sa babyn ki mace ce ba namiji ba, inga ta inda za a ma Tsoho takwara, da sauri tace wallahi ba Amin ba, InshaAllah namiji ne, kai koma mace ce shes welcome, Don wallahi sai an ma tsoho takwara ko namiji ko mace, zaid yace how? Tace Musbahatu za'a sa mata, Zaid ya riqe cikinsa yana daria, wato sai dai anyi mai takwaran ko? Tace Gbam! Yace ban manta ba, look me in d eye nd tell me u love me, ta hada idanuwanta da nashi, ina sonka, i love u, ina kaunarka, ina maka son da ban san irinshi ba, ba kalaman da zasu bayyana kalar son da nake maka, sonka a jinina yake, i love u so much Dr Zaid, i want to spend d rest of my life with u, I cannot live without u, Allah ya bar mu tare, dadi kamar ya kashe zaid yace Amin Maman Musbahatu ko Musbah, tayi daria ta sa hannunta biyu ta rufe fuskarta tana daria. Ya zame hannunta ya bata wani hot kiss, cikin wata kasalalliyar murya yace, I am going to change the way u look at me, i'll put desire in ur eyes, u are mine since day one, even if we are from different worlds u belong only to me, u're created to be with me alone, i will choose u in a hundred life time, in a hundred worlds, in any version of reality, I will find u and I will choose you, because u are mine, nd u belong to me. I love you so much Rumaysa'u ta share hawayen farincikin da ya gangaro mata ta rungumeshi tace i love u too yazayd, i love u more.

_Bibilicious Biebee_

6⃣5⃣ 🏡Gidan Gandu🏠 by💕Biebee Isa💕

Hausawa nacewa Idan Zaka so mutum ka so shi saisa saisa, Idan zaka k'i shi to ka k'ishi saisa saisa, kar ka yawaita so, kuma kar ka yawai ta k'i, don wata rana So na rikidewa ya koma K'i, haka ma K'i na rikidewa ya koma so, Idan zaka so mutum, to ka so shi dan Allah, idan kuma zaka k'i mutum ka qi shi donAllah. Ni na yarda da wannan batu, na yarda da wannan zance, idan akayi laakari da Yadda Masoyan nan 12 suka kasance Maqiyan juna a farko, kamar masu ganin hanjin juna, suka tsauwala k'iyayyar juna, farat daya, dalili daya ya chanza Akalar Kiyayyar nan, ya koma soyyayah, yanzu sun kasance kamar tif da taya, har suna ikirirarin basa iya rayuwa ba juna ba. So tsaftataciyya suke ginawa a rayukansu, Tabbas Tsoho ba ya Raye, amma suna jinshi a kusa dasu, He lives in them, saboda duk abunda zasuyi su kan yi tuni da abun da ya umurce su a baya, sai su ga kamar a lokacin ne yake basu umurnin yin Abun. Burin Tsoho ya cika, kansu hade, Su Baba Mudassir da Baba labaran tsaye suke kan gidan, duk abunda suka san tsoho zaiyi shi sukeyi, wanda suka san bazaeiyi ba ba sayi, ko da a ka zo raban Gado, hankali kwance a ka gudanar da rabon, kowa ya samu kasonshi, Dama kafin ya rasu ya danqa ma waenda basu da gadonshi filaye da gonaki, Wasu daga cikin 'yayan tsoho sun gina Massalatai, islamiyoyi, rijiyoyi a kauyuka da sunan Musbahu Bn Zailani. Matanshi sun hada kansu, ba zaka taba cewa akwai wani abunda ya taba shiga tsakanin su ba, sun zama Tsintsiya madaurinki daya. Kullum Adduarsu Allah ya kara hada kansu, ya kai ma tsoho ladar abubuwan da sukayi domin shi..

5 years laterlater
Architect Suraj Umar da matarsa Bilkisu na da yaro daya Musbah(Hanif) mai kimani shekara 5
Engr Samir Gambo da Matarsa Amira na da yara biyu mata, yan biyu ne, Hassana(Sadeeqa) da Hussaina (Sajeeda) shekarunsu 3
Dr Zaid Mudassir da Matarsa Sister Rumaysa na da yara biyu maza suma yan biyun ne, Musbah(Afeef)da Rabi'u(Areef) shekarunsu 5
Aero. Engr Mu'ammar Labaran da matar sa Islahulkhair na da diya daya mai suna Aishatu(Yesmin)tana da shekaru 3.
Pet. Engr Jawad Mudassir da matarsa Fadila na da diya daya mai suna Karima(mimi).
Pharm. Zayyad Hussain da matarsa Hanifa na da yaro daya me suna Musbahu(Ayman)shekaranshi 6.

Sun hadu duka a GIDAN GANDU kasancewar duk suna hutu, Yau Tsoho ya cika shekaru 6 da rasuwa. Amma ba abunda ya chanza nadaga Gidan.
*****
Ayman, Afeef, Areef, Hanif Suka shigo parlorn Tsoho a guje suka fada kan Hajia Babba, suna cewa great grandma, munje Kabarin Tsoho, yanzu Grand Pa Abbakar ya kaimu, mun mushi addua, kuma mun gaya mai kuna gaisheshi kuma kunce kuna sonshi. Hajia babba tace Yauwa yan yarorina, kun kyauta, Grtgrandma Ama, kamar naji tsoho yace in gaisheki, duk akayi daria, Aunty nuratu tace u guys are hallucinating, d dead cant talk, Areef yace but Grams nur, i was told that Tsoho lives in us, Right Dad? Zaid ya yi murmushi yace Right son, Ayman yace so u see grams even if his long gone, we feel his presence around, Aunty Abida tace lallai wadanna yaran, u are soo brave, wayan ku yayi yawa. Sukace we have to be brave Grams, afterall we are our fathers sons, akayi daria duka, Ayman yace Grams Zainab, Dad yace min if i grow up, m going to get married to Yesmin, Wowww inji yan dakin, Hanif yace nd mimi will be my wife, Arif yace mummy told me i will be sajida's husband, Aunty Sadiya ta kalli Afeef tace kai baka magana? Wace zata zama matarka? Shiru kawai yayi yana kallonsu, Hajia Babba tayi karaf tace shine hassan ko? Maysah tadaga kai eh, tace ahap, ai idan be dauko halin ubanshi ba sai an chnza mai suna, miskili ne, da ya gado Zaidu sai ya zarceshi, duk akayi daria. Arif yace twin bro zai aura twin sis din sadeeqa, sajeeda,. Mu'ammar yace ku zonan, duk suka taso suka zauna kusa da shi, yace i can see my boy's are smart huh? Ina fatan yanda kuke da baki haka, haka kuke a school and islamia, suka daga kai yes Abba, yace i want u to study hard for now, i want you to grow into handsome prince-s charming nd make alotta money like Ur Daddy Samir, only then i'll get u married to ur betrothed, kungane? School first, ina so kuyi kokari sosai a makaranta, i want u to be amongst d best 3 in ur classes, duk wanda yayi more dan 3rd position, bashi ba hawan private jet dina, nd no vacation a Dubai kuna jina? Suka daga kai yes Abba, mun gane, yace good boys. Aunty Zainab tace mungode 'ya'yann mu, na fahimci cewa kuna gina soyayyar Zabin da tsoho ya ma yaranku a zuciyoyinsu, gwara tun Yanzu su tashi da son junansu, kar sai lokacin suce ba su san zancen ba, kamar yadda wasu sukayi a da, su fadila da Hanifa Suka fashe da daria,Aunty da mu ake kenan? Tace kun tsargu ne? Surah yace mun cika ma tsoho buririkanshi bayan ya rasu, wannan kadai ya rage, yace shima da lokaci yayi InshaAllahu za mu cika mai Burinsa na karshe, Allah dai ya kaimu rai da lafia, duk aka amsa da Amin.

Jawad ya kalli yan matan yace Hello Angels, Mimi, Sajeeda, Sadeeqa da Yesmin suka amsa da yes Daddy, wanna have some Ice cream? Da murna sukace yes Daddy, Okay, before i buy u icecream, ya'll shud get up and say ur Regular Prayers after Salat, loudly. Yaran su 7 suka miqe suka tsaya gaban parlorn yanda kowa na kallonsu, suka hada baki wurin cewa, Oh Allah Grant us Jannah, Oh Allah forgive our Sins, Oh Allah bless our Parents, Oh Allah, Let Tsoho's Soul Rest in Peace, Oh Allah reunite us With our Grt grandpa in Jannah. Amin, kowa ya amsa da Amin, Yaran sun burge kakkaninsu, sunji dadin Adduan da jikokinsu ke ma Mahiafinsu, duk suka hau kabbara suna jinjina ma iyayensu, Hajia Babba ta yabe baki tace wai su wadannan tattaba kunnen namu, ba sa hausa ne, Ko me sai da turanci? Me sukecewa ne, najk harda kiran tsoho,? Zayyad yayi murmushi. Ya fassara mata abin da sukace, Hajia Babba ta shiga tafa hannayenta tana cewa Sankyu Sankyu, Yauwa Yaran Albarka, Allah dai ya Raya ku duka, duk suka Amsa da Amin....

Long Live GIDAN GANDUN MARIGAYI TSOHO , Long live Zailani Family.

TAMMAT BI HAMDULILAHI.
Alhamdulilah, A nan na kawo karshen K'ageggen labari mai suna Gidan Gandu, kar wani ya ga kamar wani abu a ciki yayi kama da abunda ya faru a familynsu, toh wannan labari na Gidan Gandu k'irk'irarene, be faru ba, Nayi shi ne domin Isar da Sako a cikin Alumma, kuma ina fatan sakon ya isar. Abunda nayi kuskure ko ba daidai ba a gafarta min, danAdam Ajizi ne.

Thank u Nuratu Adamu Maiyadi for coming up with the name "🏡Gidan Gandu🏠"
Thanks Yalex, The Only Male i
know that Read this Novel.
Thanks Indon Biebee.
Thank u All Members of FEEDOH &BIEBEE'S ✍🏻FANS
WORLD OF HAUSA NOVELS📚
BEAUTIFUL LADIES💅🏻
GORGEOUS ANGELS👻
AFSHAHAR NOVELS📜
DANDALIN LUBIE MAITAFSIR

FANS👻
Gareku Masoyana, ku sani nayi 🏡Gidan Gandu🏠 domin kune, idan baku ba 🏡Gidan Gandu🏠, Nagode da Soyayyar da kuka nuna min, Da wa'yanda na sani da wa'yanda bansani ba, da masu kirana, da masu min messages, both sms nd whatsapp, da wanda basu samu damar samu na ba, ina miqa Godiata gareku. Thanks a bunch 💕Biebee Isa💕 loves you, wherever u are, you'll never be far, i'm keeping you near inside of my Heart. I love you all.

Nagode! Nagode!! Nagode!!! #Grateful #1love

Urs Truly Zainab Isa A.K.A Hell 💕Biebee Isa 💕IG:@nerb_esa

_Bibilicious Biebee_

29 / 29