Masarautar Qamar Sirrin Fadar Sarauta by Khadija KMU

Author :  Khadija KMU Category :  Romance

Chapter   12 / 27

33K to 36K   out of 79.4K words

kawai take cewa cikin ranta







Hurriya kam tana komawa ana kiran sallahr magrib



Alwala tayi sannan tayi sallah bayan tagama ta nufi babban kitchen tareda crossing hannunta abayanta kallon yadda kowa yake hada hada tayi haule reza naganinta tazo wurinta saida ta kalleta tace yar nan naji ance kinsha ciwo Hurriya daga mata kai tayi





Kallon Haule reza tayi sannan tace aiki zamuyi zan biyaki haule najin kudi ta daga kai Hurriya bayani tayi mata yadda komai zai kasance







Sannan ta koma daki Bintu ta bama kudi ta siyo mata sabuwar reza da omo klin sai lemun tsami da gishiri kallonta Bintu tayi tana mamakin mi zatayi dasu saidai tasan kota tamabaye bata da amsa indai Hurriya ce don haka taje ta siyo mata duka abinda ta aiketa





Isha i Hurriya tayi sannan ta sanya earpiece a kunnenta tanabin waka Bintu tazo tayi mata saida safe sannan ta nufi makwancin ta







Saida dare yayi sannan haule reza tazo da kularta wadda ta juyo tafasaasun ruwan zafinta



Wurin Hurriya taje inda Hurriya take kwance don kamar ita take jira tanajin nishinta ta tashi









Haule reza ta kalleta tace muje Hurriya daga ita sai hijab ta tashi hannunta rike da abinda ta aiki Bintu suka nufi wurin wasila don da ita takeso afara Hurriya tsayawa tayi tana kallon yadda komai ya fara gudana duk yadda Hurriya ta fada ma haule reza haka ta fara gudanar da ayyukanta don saida ta fara Gangarawa ta daura ma wasila kyale ta dode mata baki wanda tana tabata ta tashi daga Bacci tana zare ido saitin fuskarta wasila tazo ta kalla sannan ta kalli hurriya tace ayi anan? Hurriya girgiza kai tayi



Haka haule reza ta rinka tambayarta saida tazo kan kafafunta sannan Hurriya ta daga mata kai Hurriya matsowa tayi tanuna mata Daidai inda zata yanka wurare biyar ne wanda duk idan aka taba ma mutum shi akafa tohm sai Allah haule reza kallonta ta rinkayi tana kallon rashin tsoro da rashin tausayin dake cikin idonta



Wasila kam ihu ta rinkayi Amman sam baya fita kiyi mana inji Hurriya ba bata lokaci haule reza ta daura sabuwar reza mai matukar kaifi sannan taja wurin da karfin tsiya wani irin azababben ihu ta saki Amman to no avail saboda baya fita baba haule ta riketa



sannan Hurriya ta fasa klin dinta guda daya ta zuba mata shi wani irin uban kara ta saki tana shure shure Hurriya murmushi tayi sannan ta barbada mata gishiri ta hada da matsa lemun tsami a ciwon





Saida ta sanya haule reza tayi mata yanka biyar sannan ta barbada mata ingredients dinta



Tun tana kuka har kukan ya daina fita ba imani kwata kwata tattare da Hurriya ta bude kular nan ta debo tafasassun ruwa ta watsa mata akafafunta duka biyun ai wasila suma tayi



Haule reza kallon irin launin azabar da Hurriya take mata tayi tana mamakin rashin tsoro da rashin imanin yarinyar nan. Ta tabbata zuwa gobe kafarta tayi mummunar konewa .







Haka Hurriya ta rinka binsu saida ta tabbata duka tayi masu azaba iri daya don duk saida haule ta daure masu baki sannan tayi masu yanka biyar biyar Hurriya ta zuba masu omo hade da gishiri da lemun tsami sannan ta kona kafafun da ruwan zafi







Bayan sun gama tace a a aske ma Hansa u gashin kanta tass ita kuma wasila da Barira har yanzu tana binsu bashi ta wuce ta nufi makwancinta





Haule reza kallon bayanta tayi yadda take tafiya kamar tana tausayin kasa haka take takawa tunda take bata taba ganin mutum marar imanin Hurriya ba



Duk ihun da suke da neman ceton rai da suke ko dar bare gizau haka Hurriya ta rinkayi masu launin azaba don tasan ba wanda bai suma ba acikinsu







Tabb inji haule tace akwai kallo dai wurin nan saidai sune suka ja ma kansu daman ance in kasa wata ba kasan wataba.











Hello fans yanzu zan rinka posting from Monday to Thursday saidai daga Friday zuwa Sunday ba post



Idan kuma kun fiso a rinka skipping rana daya tohm I will be waiting for your opinions







Love xoxod'þ=Ø|Ü<Øýß

[12/02, 4:54 PM] Khadyn Sp: <ØßMasarautar Qamar

A story about a mysterious palace



By Khadija (KMU)



27&28



Kwanciya tayi Hurriya tareda sauke ajiyar zuciya don yanzu ne zata iya Bacci cikin dadi don idan batayi masu hukunci ba gaskiya ba sunanta Hurriya Faisait Hamood ba.





Haule reza kam tana mamakin inda yarinyar nan ta samo kalar launin azabar datayi masu don bata taba ganin hakan ba saidai fa ba karya Hurriya muguwa ce tace sannan ta nufi makwancinta





Yau da safe da aka tashi aka iske duka yan click dinsu Barira suna jinya don kusan ihun wasila ya tadasu don azaba ta ko ina takeji kuka kam yinshi take kawai don a halin da take ciki da za a cire kafar to da tanaso indai har zata rabu da ciwon da takeji.





Barira kam har garin Allah ya waye itada suwaiba to asume suke saida aka samu da kyar suka farfado irin ciwo daya ne Dukansu suke fama dashi Dukansu saidai kowa na mamakin wanda yayi masu wannan danyan aikin







Hurriya yau ta samu ta tashi da wuri don har sallahr asuba ta samu damar yinta da wuri. Tanajin sai jaje akeyi Bintu ce tazo da gudu tana haki ta kalli Hurriya sannan tace naji abinda ya faru gasu barira Amman don Allah kece?kice bake bace don Allah kice man haka Hurriya kallonta tayi sannan tace nice Bintu And idan suka kara koda hararata abun da zanyi masu sai yafi wannan Bintu kallon Hurriya tayi sannan tace haba Hurriya miyasa zakiyi haka kinga kafafunsu idan kika gani sai sun baki tausayi wallahi dama kin kyalesu sunje da halinsu tunda yanzu suma zasu ce zasu rama kema zaki ce zaki rama kuma ance sarkin yawa yafi sarkin karfi kuma ma kinsan kaura saurayin barira ne sai ance shaho saurayin Hansa u ne



Bintu batasan duk maganar da takeyi Hurriya tayi tafiyarta







Juyawar da zatayi taga ba Hurriya saidai ganin inuwar Hurriya tayi







Hurriya tana fitowa saiga hauke reza wadda ta taya danyan aikin jiya



Kallon Hurriya tayi tana washe baki sannan tace Hurriya naga sako nagode kuma don Allah inson kibani dama yadda idon akace gobe su kara to bazasu kara ba



Hurriya shiru tayi mata har tagama babatunta batace komai ba



Kitchen taje inna hanne na kallonta tazo tace Hurriya an tashi naji danyan aikin da kika aikata baki kyauta ba



Hurriya dage girarta tayi tace banzo don inji kyautawa da rashin kyautawa wurin ki ba malama ki zuba min ruwan zafi in kama gabana





Inna Hanne kallonta take kamar statue zata iya cewa tunda Hurriya ta tashi daga rashin lafiya to yaune ta samu jin muryarta mai tsayi har haka inna hanne wadda tayi curr tana kallonta tsarki ya tabbata ga Allah sannan tace lallai kedin gimbiya ce duk aranta take maganar don kwata kwata bataji haushi ba





Inna Hanne daukar bokitin tayi ta zubo mata ruwan zafi suka jero tare inna hanne rike da ruwan Hurriya kuma rike da kayan wankanta har suka zo toilet



Hurriya wanka ta shiga tayi sannan ta fito ta nufi daki

Sai kallonta akeyi don ba inda maganar bataje ba ita tayi masu Hansa u wannan hukuncin wasu ta burgesu wasu kuma ta basu tausayi wasu kuma zaginta kawai sukeyi but who cares





Shiryawa tayi cikin uniform dinta wadanda sukayi mata kyau Sosai



Comb ta dauka ta tsaga kanta hudu sannan tayi kalaba manya manya guda hudu wanda suka sauka har gadon bayanta nade gashin tayi har saida ya dawo Daidai keyarta sannan ta fesa turarenta ta fita





Sashen imad ta fara zuwa aikam cikin sa a ta gyara ko ina har dayan dakin shi wanda yake bacci





Tanajin karar ruwa hakan ya tabattar mata da yana toilet don haka tana gama mopping ta fito ta wuce part din zinariya wanda tunda ta fara aiki bata taba gifta kofar data wuce ta kitchen ba





Don haka tana zuwa tayi wanke wanke sannan ta fara hada breakfast tanajinsu suna gulma murya can kasa kasa Amman sautim maganar su radam a kunnen Hurriya wata a cikin kuyangin ce tace hmmm labari da dumi duminsa fa



Kowa cewa yayi munajinki subira ta kusa dawowa fa ance sati mai zoo zata dawo, wata acikinsu ta fara salati tana jajanta masu subira fa suna cikin matsala ta dade batazo kasar nan ba don haka dayawa kilan sun manta wacece subira AI kuma ba lallai kowa ya iya manta subira ba saboda irin record din da ta bari





Hurriya duk tanajinsu wata acikinsu tace shekara fa ta kusa zagayowa shiru Dukansu sukayi suna zare ido wata acikinsu tace nidai bani da kyaun da za a rasani a masarautar nan





Jakadiyar zinariya ce ta shigo ta kallesu tace me kukeyi ku wuce ku kai abincin Dukansu daga mata kai sukayi itadai Hurriya na aikinta





Tana gama aikin ta fita ta nufi inda suke wanki tana zuwa ta iske wasba tana wasa da dan icce tana ganin Hurriya wasba ta saki iccen ta rugo wurinta tana dariya tace tun dazu nike jiranki Hurriya bata ko kalleta ba tayi gaba inda ta saba wanki





Kayan ta fara wankewa wasba kam ta samu wuri kusada Hurriya ta zauna tana ta bama Hurriya tatsuniya mai ban dariya duk intayi sai taga Hurriya fuskarta daure sai tace bari in canza haka wasba ta zauna tana bama Hurriya labarai masu ban dariya Amman Hurriya ko murmushi batayi ba bare dariya





Wasba kuma taki tafiya sai can wani yaro yazo ya kirata ance ana kiranta tashi tayi ta ruga tana tsalle ta juyo tayi ma Hurriya alama da hannu Inasonki





Hurriya tsoki tayi ta cigaba da wankinta tana waka





Yunwa ce ta fara galabaitar da Hurriya saboda tun tashinta yau bataci abinci ba don haka tana ida shanya kayan ta nufo dakinsu





Harabar wurin tagani tasan cewar ba lafiya ba don haka ba tare da bata lokaci ba kutso wurin





Kowa ita yake jira a taron mutanen da akayi ta riga tasan da haka bata damu ba taja kai tana niyyar shiga wurin shaho ne ya tare hanyar yana watsa mata idanunshi masu firgita ma mutane lissafi itama kalloshi tayi tare da tsirtar da miyau a kafarshi tace disgusting kaura ne yazo a 360 don ranshi yana matukar tafarfasa da wannan makirar yarinya mai kyau sai kace ita tayi kanta duk masarautar nan waye ya isa ya taba barirarshi ya kwana lafiya babushi

Sai ita ta watsa mata tuwo a fuska gashi kuma tayi masu wani irin salon launin azaba tabbas yau sai ya wulakanta



cikin zafin nama kaura ya daga dorinar shi zai zuba mata Hurriya da yau itama ranta yagama baci don bazata iya tuna when last tayi irin bacin ran nan ba ta rike dorinar da karfi tanayi mashi matsiyacin kallo wanda ke dauke da tsantsar mulki da kuma izza tace the moment you beat me with your filthy hands you re going to be executed ta matso tana mashi whispering tace kana kuskuren dukana to hukuncika kisa





Ta saki bulalar ta tsotsi bakinta cikin isa da mulki tace duk wanda bai fasa dukana ba acikin ku Amman ku tabbata duk wanda yayi gigin kara tabani a masarautar nan da sunan duka to sai ya amshi laifin shi na taba lafiyar Hurriya Faisait Hamood this is a promise and try me and see ta watsa masu wani wukantacen kallo tace jakuna daku matsiyata ta shige cikin dakin tana barin kowa baki bude





Kaura da shaho kam kamar wasu duwatsu haka sukayi don sungani à idanun yarinyar duk wanda ya kara tabata to kilan lahira zai bakunta yadda ta furta kisa kuma yadda ta nuna hukunci mai tsanani mutum zai amsa saidai tayi matukar kunyata su





Shiru Dukansu sukayi tareda juyawa suka tafi cike da borin kunya



Ikon Allah yan wurin kowa ya rinka fada to miyasa basu daketa ba mi tace masu har haka watsewa akayi kowa da alajabin wannan Hurriyar



Sa ade da karime suna kallon komai sa ade ce tace wallahi na tsani waccar shegiyar Hurriyar karime tayi wata dariya tace naki akeji amman ki bari zamu yi maganinta a masarautar nan tunda kowa ya gagara maganin shegiyar



Bintu ce ta gifto matsawa tayi saitin su tace kafin kuyi maganinta ni Zan sanya tayi maganin ku mutanen kawai tana kallon yadda suka zare ido alamun shakka dariya tayi ta shige ciki



Sallah ta iske Hurriya nayi Bintu kallon yadda take sallar kawai tayi ta girgiza kai ta zauna tana jiran tagama sallahr







Bayan ta sallame sallahr ta juyo ta kalli Bintu wadda take gyangyadi murmushi Hurriya tayi wanda batasan tayi shi ba don da sauri ta maidashi sannan tace Bintu Bintu adan firgice Bintu ta tashi Hurriya kallon katifa tayi sannan tayi ma Bintu alamu data kwanta



Ba musu Bintu ta kwanta wani irin bacccin gajiya ya dauketa murmushi Hurriya tayi sannan ta dauki wayarta da ta amso chargy dazu wurin haule reza





Bude wayar tayi wani tunani yazo mata da sauri ta cire tunanin waka ta kunna ta kishingida nesa da Bintu





Inna hanne ce tazo da plate da kula na abinci kallon Hurriya tayi da ta lumshe ido tanajin waka sam batason wakar da Hurriya keji don akwai abubuwa da yawa gabanta karatun AlQur ani ya kamata ta rinka ji ba waka ba Amman Hurriya is not helping matters





Murmushi tayi ganin yadda take bin wakar





Inna hanne tace Hurriya Hurriya saida inna hanne ta daga murya Sosai Hurriya ta tashi kallonta tayi ta dage mata gira alamun lafiya shigowa tayi tare da ajiye kular sannan tace abinci na kawo maki daga mata kai Hurriya tayi sannan ta koma ta kwanta ta dade bata motsa ba don har inna hanne ta tafi idonta rufe



Saida taji yunwa na damunta Sosai sannan ta bude idonta tare da cizon lebenta ta sauko ta zuba shinkafa da mai da yaji hada maggi mai tauraro





Kamar tanajin tausayin cikinta haka ta fara cin abinci har saida taji ta koshi sannan ta ajiye cokalin tasha Ruwa







Yau ya kama wata daya kenan da kona masu su barira da Hurriya tayi su kuma su shaho da kaura tunda Hurriya tayi masu warning dinan basu kara zuwa ba Amman sun kudirta aransu abinda zasuyi mata mai muni ne





Bintu kam da Hurriya sun zama tamkar yan uwa don Hurriya har ta fara bude mata wasu abubuwan duk da she s not allowed to do that saboda she s not to trust anybody in this life saidai mi after all she s human being too tana amsa sunanta yar adam don haka itama tanada émotions kamar kowa kawai ta iya boye émotions din nata saboda emotions dinta babbar barazana ce a rayuwarta bata yadda ace wani Abu yafi karfinta ba tunda ita har takeda kanta so she have full control of herself don haka she control everything around her herself her maids kowa da kowa saidai yanzu kanta kadai zata iya controlling





Bintu ba karamin son Hurriya take ba don ita kadai take kallo taji sanyi a rayuwarta ko kuma ince a masarautar Qamar bata da kowa sai Allah sai Hurriya



Ita kanta Hurriya idan har kasan mi kakeyi yadda take kallon Bintu kadai zai nuna maka tana matukar tsantsar Qaunarta don idonta har wani gleaming na pure love yakeyi



Yanzu haka ma Bintu ce ta siyo masu awara da rake itada Hurriya



Zaune suke saman wani dakali su biyu Hurriya ba dankwali a kanta gashin kanta duka ya zuba a gadon bayanta don bata daureshi ba







Kallon wurin da wasba ke zama tana wasa da icce Hurriya tayi kafin ta sanya hannu cikin awarar wadda ta tauna sai kuma tayi murmushi wanda duka dimples dinta suka lotsa dan gleam din dake a gefen idonta ya kara fitowa Bintu lahaula wala Quwatta illah billah kawai take ambato Lallai babu karfi da iko sai gurin Allah wanda yayi hallitar nan ba tare da makusa ba ita Hurriya wani irin kyau ne take dashi har haka?







Shin gwara da ya kasance bata dariya da ace tana dariya tabbas da dariyar ta zamar mata babban kalubale a rayuwarta acikin masarautar wani irin kyau take gani kota Ina gaban Bintu banda faduwa ba abinda yakeyi ita mace ma kenan wai tohm inaga namiji





Hurriya ta dage girarta daya ta kalli Bintu sannan tace kallon na miye?





Ba komai inji Bintu kasa rikewa Bintu tayi don da farko batayi niyyar fadar abinda ke cikin ranta ba cewa tayi MashaAllah Hurriya kina da kyau Hurriya batace mata komai ba ta kara sanya a wara a bakinta.

[12/02, 4:54 PM] Khadyn Sp: <ØßMasarautar Qamar

A story about a mysterious palace



By Khadija (KMU)



29&30



Saida taci awarar kusan guda hudu sannan tasha raken wanda aka daddatsa guda biyu





Bata Qara cema Bintu komai ba ta sauko Bintu nagani Hurriya ta fara tafiya itama ta sauko tana cewa Hurriya jirani banza Hurriya tayi da ita aiko Bintu ta rugo ta samu suka jera tare tana haki





Tana shiga aka fara kiran Sallahr magriba sallah sukayi sai ga inna hanne ta shigo wadda yanzu Hurriya na bata amsa yanzu idan tayi mata magana kallonsu tayi Dukansu Hurriya nagama sallah ta linke hijab sannan ta dauki wayarta ta makala earpiece inna hanne tace Hurriya kidan rufe kanki don Allah tunda dare yayi kinji





Ko kallon inda take Hurriya batayi bare tasan ran amsa ta fita zuwa part din Imad







Ba inda ta tsaya sai part din Imad wanda zasuyi tafiya gobe kuma yace mata tare zasuyi parking she must come





Ba kowa parlon don haka ba inda ta tsaya sai bedroom dinshi yana zaune ya mike kafafunshi yana amfani da MacBook sai Qamshi dakin yake na turaren wuta mai sanyin dadi



Lumshe ido Hurriya tayi sannan ta bude idonta masu kyau ta tsotsi lebenta



Batace mashi komai ba ta bude duka wadropes dinshi akwai wani wuri dake da jerin tarin designers suitcase, Daya daga ciki ta dauka mai matukar kyau da tsada na Bottega veneta ta ajiyeshi sannan ta fara shirya mashi kaya tunda ta shigo yake kallonta ta karkashin ido don ba

12 / 27