KAMAR DA WASA BY UMMI A’ISHA

Author :  Ummu Hairan Category :  Love

Chapter   33 / 42

96K to 99K   out of 124.3K words

shigo amma shiru. Washe gari ita da kanta ta hada breakfast mai sauki tana falo tana karyawa yafito yanata"

"shan kamshi kamar bai iya dariya ba,"

"Wuceta yayi zuwa kan table yazauna shima yafara karyawa abunda yasake kona ranta kenan yasata mikewa takoma bedroom tabar masa falon gaba daya, tana zaune gefen gado da system akan cinyarta saboda nanda kwana biyu zata koma aiki dama sati daya aka bata kawai taji yana"

"knocking abakin kofa,"

"""Yes..."" Yafada atakaice, bude kofar yayi ya dan leko kansa ciki batare da yashigo ba yace,"

"""Ki duba store koda akwai abunda babu wanda kike bukata saiki rubuta fita zanyi """

"Batare da ta kalleshi ba tace,"

"""Kayan miya zaka siyo kadai """

"Baice komai ba yakoma yaja mata kofar, wanka yaje yayi yafita bai wani jimaba yakawo kayan miyar yasake komawa kai tsaye gidan anty asabe yawuce ta can suka tafi kasuwa tare da ita, kayan lefen husnah suka hado sannan suka sabunto lefen Bilkisu nada suka sassauyo kayan ciki da akwatunan saboda kafin yakoma makaranta za akai lefen husnah sannan za ayanke rana, wuni cur sukayi akasuwa shida anty dan sai yamma liss suka koma gida duk da tana ta cewa yazauna yaci"

"abinci yace a'a girkin amarya zaije yaci,"

"""Babu ko kara ko fahad?"" Ta fada tana dariya, baiyi magana ba yasaka sau cikinsa yanufi gida."

"Kamar yadda jiya bata san fitarsa ba haka yauma batare da ta saniba yayi tafiyarsa shiyasa abun ya tsaye mata arai, tana kitchen tana girkin abincin rana khulsum tazo dauke da danta khalifa,tare suka karasa wuni da yamma tatafi, khulsum na tafiya bayan takoma ciki tayi wanka tana shiryawa fahad yadawo, yunwa yakeji sosai sannan gashi yagaji lilis, rigar shaddar dake jikinsa yacire ya zamana daga shi sai yar farar singileti da dogon wando, zama yayi kan table yafara bude abincin dake wurin, jallop din shinkafa ne sai hadin vegetables salad mai dauke da dafaffen kwai aciki. Yana tsaka da cin abincin yajiyo karar wayarshi amma bai iya tashiba saboda yana jin dadin abincin sosai ba kadan ba, yayi missing girkinta da ita kanta gaba daya, saida ya koshi dam sannan yataso yana rikeda tissue yana goge bakinsa, dai dai lokacin itama tafito daga cikin daki, kallon juna sukayi tazo tawuce shi tanufi dining area ta bude fridge ta dauko banana milk shake ta zuba acikin glass cup tazo tawuce daki, ganin abinda ta debo yasashi shima komawa dining area din yazuba cikin cup ya shanye yana lumshe ido saboda gardi da dadi gashi yadau sanyi ba karya, rigarshi da ya cire yaje ya dauka tareda wayarshi yashiga daki, zama yayi saman katifa yana"

"kokarin kiran husnah saboda itace ta kirashi dazu, tana dagawa yace,"

"""Am sorry my love.... Dazu kin kirani time din ina tare da antynki ne ina cin girkinta mai dadi """

"Duk da taji haushin maganarsa amma saita waske tanuna kamar bataji zafin hakan ba tace,"

"""Babu komai my prince dama zan fitane zamuje kasuwa nida Fa'iza. """

"""Adawo lafiya my love. Allah yatsare"""

"Daga haka sukayi sallama yakatse wayar dama tun lokacin da suka jone da husnah ko ba ya gari idan zata fita saita tambayeshi shiyasa har sun dade da sabawa da wannan tsarin sam basa kallonsa asabon abu. Irin zaman da su Bilkisu suka faro shi suka cigaba da yi na ba ruwan kowa da kowa, gaisuwa kuwa tab rabon da taji fahad ya gaisheta har ta manta gashi yanzu wani sabon salon wulakanci da ya koya shine sai yarinka kiranta da Bilkisu, idan zaiyi mata magana sai dai yakira sunanta, yauma da zai fada mata sakon su ayiyah tana daki tana ware kayan sawarta tana karasa"

"shiryawa cikin drewar, zama yayi gefen gadonta yace,"

"""Am Bilkisu ayiyah tabani sako. Tace wai gobe za akai lefen ya Abba gidansu salim idan kinada"

"lokaci kije akai dake """

"""Naji "" Tafada atakaice saboda tasoma kosawa da wannan rashin kirkin nashi akan me zai rinka"

"kiran sunanta kai tsaye? Duk da bawai yau yafara ba amma yau kamar hakan yafi kona mata rai. Washe gari da yamma bayan tadawo daga aiki ta shirya tatafi gidansu fahad sai kaffa kaffa ayiyah takeyi da ita, dama tasan bata da matsalar uwar miji dan ayiyah na mutukar sonta hakama sauran yan uwan mijinta kawai dai abinda ta lura shine matar ya sunusi wato anty juwairiyya bata faran faran da ita tun wancan lokacin har yanzu dan tun aurensu nafarko taketa kukkushe Bilkisu tana cewa ai fahad tsohuwar yayarshi ya auro dan wannan a haihuwar kajima ai ta haifeshi, ko yauma da ta shigo gidan kowa yanata murna da lale marhabun da ita amma banda Anty juwairiyya shiyasa itama takama class dinta daga gaisuwa bata kara cewa komai ba,tarba ta girmamawa aka yimusu agidansu salim akwatuna shida masu kyau suka kaiwa nusaiba bayan an karbi kayan da babu jimawa suka koma gidansu fahad lokacin magriba tayi, Bilkisu tafito tsakar gida tana alwala"

"sai ga fahad yashigo daga masallaci yake anty juwairiyya na ganinshi tafara cewa,"

"""Kaga sabon ango....kaima nanda wani satin zamuje Kaduna mukai maka naka. """

Baiyi magana ba sai murmushi kawai duka hannayenshi na cikin aljihun rigar farar shaddar da

"take jikinsa,gun Bilkisu yakarasa ya tsaya kusa da ita tana alwala,"

"""Zaki tafi yanzune injiraki ko sai anjima sai indawo in daukeki?"""

"Jin abinda yace ba karamin dadi yayiwa Bilkisu ba saboda tasan dai ko babu komai anty juwairiyya zata gane fahad na yinta kuma tanada wani matsayi na musamman agareshi,rausayar da"

"kai tayi ta kalleshi sannan tace,"

"""Da sallah nake son nayi... Ko sauri kakeyi?"""

"""A'a kiyi mana... Kiyi sai mutafi"""

"""Yawwa nagode"" tafada tana kokarin shiga falon ayiyah inda anty juwairiyya ke tsaye tana kallonsu sai jan fahad take da maganar bikinsa shida husnah amma yaki biye mata suyi saboda shi yanada wani abu guda daya akan Bilkisu, idan daga shi sai itane baya raga mata ahalin yanzu amma idan agaban mutane ne ko wani to yana nuna har gobe yana sonta yana martabata, shiyasa abun bai cika damun Bilkisu ba saboda sai idan iya shi da itane yake nuna shine oga dole ta girmamashi. Har ta idar da salla bai bar kofar falonba yana tsaye da wayarshi a hannu yana"

"dannawa, lokacin da take yiwa ayiyah sallama tana jiyo anty juwairiyya nace masa,"

"""Ko da amaryar ake soyewa ne dan kanina. """

"""Kai anty nifa gaskiya kin saka min ido da yawa..."" Yafada yana dariya, sosai Bilkisu taji dadin amsar da yabata, fitowa tayi rikeda irin kayan snacks din da aka basu agidansu salim wanda anty asabe ta zubo mata, karba yayi daga hannunta yawuce gaba tana biye dashi abaya har waje, su ya Abba na zaune akofar gida shida salim sai taji duk kunya ta kamata musamman ma lokacin da zata hau bayan babur din nashi dole saida ta dafa kafadunshi duka guda biyun, har sukaje gida babu wanda yace da wani ci kanka sai dai idan sun dan shiga kwari ko gargada yaji ta rikeshi da haka suka je gida. Cikin yan kwanakin aka kammala komai na zuwa kd domin kai lefenshi komai iri daya yayi ma husnah da Bilkisu bai banbanta ba ita Bilkisu ma bata san wacce wainar ake toyawa ba, ita dai kawai abinda tasani shine bazata taba daukar raini ba nashi ko na matarshi, ranar da aka tafi kai lefen ma bai fada mata ba saboda har gobe irin zaman da ya zabar musu sukeyi, ita anata ganin ai ba ita yadace ta rinka shan kanshi ba ko kuma ta nemi shiri dashi, shiyasa gaba dayansu ba wani dadin zaman sukeji ba saboda kowa baya sakarwa kowa, har aka kai lefen aka saka rana wata biyu babu wanda ya gaya mata batama saniba gaba daya, shi kam fahad shirin komawarsa makaranta yasaka gaba yana kammalawa ya tafi bayan yabar mata duk abinda yasan zata bukata. Wani lokacin Mariya ko maryama ayiyah ke turo mata su tayata kwana amma ba kullum ba, tunda yatafi kuma bai kirata ba sai bayan kwana hudu da tafiyarsa nan dinma iyakarta gaisuwace daga nan ya tambayeta ko da akwai abinda take bukata tace babu shikenan yace mata sai anjima, hakace take faruwa har yayi sati uku da tafiya a lokacin ne yazo gida weekend, tun ranar Thursday yazo yana son komawa Monday ko Tuesday,lissafin bikinsu kuwa saura sati hudu babu yan kwanaki, a wannan zuwan da yayi yai niyyar fadawa Bilkisu maganar aurenshi da husnah, ranar ya fada mata da safe tana karyawa zata tafi aiki saboda Monday ce shikuma yana kwance"

"kan three sitter yana kallo, a laptop dinshi,"

"""Bilkisu aure zanyi fa...., yau saura sati uku da kwana biyu..."""

"Saida ta dan ja numfashi sannan cikin halin ko inkula tace,"

"""Allah yabada sa'a... Ko akwai wani abu da zanyi baya ga haka?"""

"Girgiza kai yayi yana murmushin takaici bai san sai yaushe Allah zai karbi addu'arshi yasa Bilkisu ta soshi kamar yadda yake sonta ba, ita kuwa tsabar takaici da bacin rai ko gama cin abincin ba tayiba tabarshi ta tashi ta dauki wayarta da handbag dinta tafita dama tun dazu mai napep din dake"

kaita aiki yazo. Fahad kwanciyarsa yaci gaba dayi har saida husnah ta kirashi tace yataimaka yazo

"ya dinka mata atamfarta domin da ita take son tatafi gida jibi, jibi zata gama exams dinta kuma idan tatafi bazata dawoba sai bayan bikinsu saboda hutun session ne, tashi yayi duk jikinsa babu karfi yayi wanka yashirya cikin kananan kaya, bakar riga da milk colour din trouser, zama yayi ya karya sannan yafita yasamu husnah a shagonsu salim tana jiransa, tsokanarsu salim yafara yi yana"

"waka yana cewa ga amarya ga ango, tare suka haura saman shagonsu fahad inda zaiyi mata dinkin."

"Bilkisu kam tana can office tarasa me yake yimata dadi, ita dai tasan ba kishine ke dawainiya da itaba kawai dai bata son yarinya karama tazo ta nemi rainata shiyasa bataji tana farin ciki da auren da fahad zaiyi ba, duk zuciyarta babu dadi take gudanar da ayyukan dake gabanta, lokacin da taje yin voicing din news kuwa kasawa tayi saboda sai tafara tiryan tiryan sai ta tsaya tana inda inda kamar yaune tafara koyon aikin daga karshe dai sai hakura tayi ta mayarwa head of news din tace kanta ke ciwo bazata iyaba, haka ta tarkata nata inata tafito domin tafiya gida dama yau khulsum bata zo ba, abin bakin ciki saida taje gida taga ashe yau bata fito da keys dinta ba wato mantaso tayi aciki da safe bata dauko ba koda yake da safenma acikin kunar zuci take saboda maganar da fahad yafada mata na aurenshi ko ina ruwanta da zaizo yasata agaba yana wani cemata aurenshi yakusa? Tsaki tayi ta tsayar da mai napep dinta dama Allah ya taimaketa bai tafiba, wayar fahad taketa kira amma bai dagaba har sau uku, tasan duk yadda akayi baya tare da wayar saboda bai fiya kin daukar wayaba matsawar yana kusa, yanzu bata da zabin da yawuce tabishi plaza shagon dinkinsu ta karbo nashi mukullan, hakan tayi tashiga napep tatafi plaza dinsu, lokacin shikuma yana zaune shida husna dasu tj yana yiwa husnah dinkinta su tj kuma sai hirar siyasa sukeyi shidai dariya yakeyi kawai saboda ganin yanda suka hakikance suke tada jijiyar wuya saida cikin kowa yafara kugi saboda yunwa kowa yadare yatafi neman abinci yarage saura su biyu ashagon, ahaka Bilkisu tashigo ta samesu, da mamaki fahad ya dago yana kallonta ranta abace fuskarta adaure"

"amma shi sai ya fadada tashi da murmushi saboda husnah dake zaune,"

"""Hajjaju yadai? Lafiya kuwa?"""

"""Inata kiranka baka daukaba...., keys dina ashe ban fita dasu ba... Bani na wajenka"""

"""Kashhhh, bari salim yadawo, dazu wallahi yazo ya karba yaje siyo fetur ne a Babur dina kuma"

"duk keys din tare suke... Sorry fa..."""

"""To ya zanyi da mai napep dake jirana?"""

"""Ba matsala bari na sallameshi sai na mayar dake gida nima nakusa tashi,have a sit"" yafada yana nuna mata wurin zama kan wani benchi dake ajiye shi kadai babu komai akai, tashi yayi da kanshi ya sauka kasa domin sallamar mai napep din, daga ita har husnah babu wadda yayi tari ita husnah ma wayar hannunta take latsawa yayinda Bilkisu ke bin shagon da kallo har ta dire kallonta kan husnah wacce ke sanye cikin riga da skirt na leshi c green taci daurin zahra buhari hakan yabawa kitson dake kanta damar lekowa ga dan siririn mayafinta kalar kayanta kan kafadarta barima guda ukune jere akunnenta kallo daya zaka yimata ka fahimci yar jami'a ce dan tsantsar wayewar da take tare da ita sam bata san cewa itace budurwar fahad ba amma ita husnah tuni tagane Bilkisu itace matar fahad hakan yasata dan kallonta ta gefen ido tabbas black beauty ce kuma ita dinma"

babu raini tun daga dressing dinta pink din materia ne ajikinta mai tsada shiyasa komai nata pink

tayi amfani dashi ciki kuwa harda hill din takalmin kafarta saboda ita ba ma'abociyar saka flat

bace.....

*_Ummi Shatu_*

*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma

08030811300*

49***Har yadawo babu wanda yayi magana acikinsu yana zuwa yazauna a mazauninsa da yatashi

"dazu,"

"""Hajjaju nabar wayar a silent ne ashe ban saniba..."" Yafada yana murmushi,"

"""Babu damuwa..."" Ta amsa hankalinta na kan wayarta dake hannunta, karfe uku saura agogon silver din dake daure a hannunta yanuna duk tagaji kawai alla alla takeyi taganta agida tasha tea ta kwanta ta huta, tsitt shagon yayi baka jin maganar kowa sai karar keken da fahad yake dinki dashi, kowa yanada dalilinsa na yin shiru, husnah da fahad dalilinsu daya ne saboda ganin Bilkisu zaune awurin shiyasa suka kasa sakewa suyi hira ita kuma Bilkisu hayaniyarce bata so domin har wani dan ciwo ciwo kanta keyi,wayarta take dannawa tana chaten da khulsum tana tambayarta abinda"

"yahanta zuwa aiki yau,"

Ninke kayan da yagama hadawa yayi ya mikawa husnah nan takarba can kasan makoshinta ta

"furta,"

"""Thank u my prince..."" Kan labbanta kawai ya kalla yayi murmushi, mikewa yayi yana yin mika"

"saboda zaman da yasha, yana kokarin daura agogon hannunshi wanda yacire yaji husnah ta fauce,"

"""Dama ai nafada maka sai nasace agogon nan wallahi yafi dacewa dani..."""

"Kallon agogon yayi ya kalli husnah shi ba wai tsadar kudin agogonne damuwarsa ba a'a yanda yake son agogonne saboda kwata kwata wannan shine sawarshi na uku a Kaduna yasiyo shi kuma unisex ne maza da mata kowa zai iya sakawa, 7 thousands ya siyeshi amma tun ranar da husnah taganshi ahannunshi tace sai yabata shikuma yahanata yace zai saka mata irinshi a lefe amma da yake kansa yadau caji gaba daya ma yamanta da sunyi magana makamanciyar wannan lokacin da"

ake hada lefen.

"""Hmm ya fahad sai munyi waya dai kawai..."" Tafada ahankali saboda kar Bilkisu tajita,hannunshi"

"ya mika mata,"

"""Bani agogona before kitafi... Bani pls"""

"Makale kafada tayi tajuya zata tafi nan yayi gaggawar riko rigarta ta baya babu shiri ta tsaya, duk abunnan da sukeyi Bilkisu bata san sunayiba domin abinda yake gabanta takeyi wato chaten, saida tajiyo motsin fara kokawarsu sannan ta daga kanta ta kallesu abin yayi mutukar bata mamaki saboda ita kallon salihi mutumin kirki take yiwa fahad amma yanzu sai ganinshi tayi dumu dumu yana kokawa da mace har yana hadata da jikinshi, to meye hakan? Har wajen baranda suka fita suna kokawa yana kokarin kwace agogonshi amma husnah ta hanashi wannan dalilinne yasashi"

"turata jikin bango ya matseta yana neman kwacewa,"

"Ganin kamar sunma manta da ita yasata tashi ta dauki jakarta fuuu tafito, abayan kofa tagansu suna manne da juna har lokacin basu daina kokawar ba, wani dogon tsaki taja sannan tawuce, dukansu tsayawa sukayi suna kallonta tana kokarin kaiwa karshen steps din benen, sakar masa agogon husnah tayi yajuya yabi bayan Bilkisu bai ko koma cikin shagonba bare ya rufeshi cikin ikon Allah sukayi kicibus da nazifi zai koma shagon, yana sauka kuma yaganta tsaye itada salim suna gaisawa alama yayiwa salim da ido nan ya wulla masa keys din dake hannunshi ya cafe yaje ya dauko babur din yatsaya agabanta ,dauke kai tayi sannan ya karkata mata tahau, duk husnah na kallonsu daga can inda take tsaye asama, har saida taga sun

33 / 42