Madadi 1 Complete Hausa Novel

Author :  Binta Umar Abale Category :  Romance

Chapter   16 / 17

45K to 48K   out of 48.8K words

samu ta fita daga gidan tunda kafin fitarsa sai da ya rufe kofar palon da key.

Yana shiga ya hangota kwance kusa da Mussadiq........Ya tsaya daga bakin kofa tare da yin gyaran murya, mikewa tayi a zabure tana kallonsa, Yace."Ya zaki zo ki takure kanki ki anan bayan kin san ko shi Mussadiq din gadon na iya yi masa kad'an." Kasa tayi da kanta tana wasa da hannayeta, Ya juya tare da fad'in "Ki taso daga cikinsu ki dawo dakina ki kwanta ko bakiji abinda nace d'azu ba."?
Murya na rawa tace" Abbah dan Allah ka kyaleni na kwanta a cikinsu sai nafi iya bacci. girgiza mata kansa yayi yana lumshe ido yace."Ba zaki takurawa kowa ba ki taso kawai."
Da sauri tace"Sai na kwanta a 'kasan kafet babu damuwa.'' Yace."Idan baki taso ba zanzo na daukeki da kaina bana son gaddama." Ganin yayi maganar cikin rashin wasa sai ta tsorata! da sauri ta sauko daga gadon Mussadiq ta biyo bayansa suka fita daga dakin.

Suna shiga dakinsa ya nuna mata ledojin da ya shigo dashi yace."Ki dauki guda d'aya akwai kazar amarcinki a ciki kada nan gaba ace ana bina bashi."

Naja'atu ta dinga kallonsa le'banta na rawa, babu shakka mutumin nan da gaske yake abinda ta fada kenan a zuciyarta......Tana kallonsa ya nufi toilet ta dinga girgiza kanta tana sake takure jikinta cikin kujera wai shin me yake shirin faruwa ne?.........Ganinsa ya fito daga toilet daure da towel iya 'kugu! faffad'an kirjinsa mai cike da yalwar gashi a waje sai yasa 'yan hanjinta hautsinawa! cikinta ya wani murd'a mata! da mugun sauri ta sunkuyar kanta a 'kasa! ashe haka yake da 'kirar mazantaka gani tayi kirjinsa a cike dam! ga jikinsa a murd'e! cikinsa a shafe tamkar wanda baya cin abinci!
Karkarwa jikinta ya shiga yi gumi na yanko mata daga ko wace kusurwa ta jikinta....



*GA MASU BUKATAR KARANTA BOOK DIN ZASU TURA #300 SINGLE, VIP GROUP #600 GA ACCONT D'IN DA ZA'A TURA KUDIN.......0542382124.....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBAR......07084653262.....IDAN KIN SAN BA BIYAN KUDIN LITTAFIN NAN ZAKI YI BA DON ALLAH KADA KI KIRA WAYA TA KO KIYI MIN WATA MAGANA TA WHASAP*

*MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA SO KU BIYA KUDIN LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS.........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE.*


*🗯️MADADI!!💍*
_(Ba Haram Bane!!)_

*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
~~~~~~~~~

*LAST FREE PEGE*
*19_20*
'Dauke kanta tayi lokacin da taga yana kokarin sanya gajeran wando, ta tsirawa 'kasan kafet ido gabanta sai duk uku-uku yake, muryarsa taji ta dokin kunnanta inda yake cewa"Ta tashi taje tayi wanka tazo ta kwanta, ba tare da tayi kuskuran kallonsa ba ta mike salo-salo ta nufi bandakin, to koda ta shiga toilet din ma kasa yin komai tayi ta jingina jikin bango(garu) tana tunani yanzu idan Abbah Abbas yace zai kar'bi sadakinsa ya za tayi? wani irin tsoro ne ya shige ta, taji gabad'aya gwiwowinta sunyi sanyi! ita yanda ma za'ayi ta kwanta gado d'aya dashi take tunani gashi ta lura dashi sai wani abu yake yi tamkar bai damu da halin damuwar da take ciki ba.......Da kyar ta d'an sirka ruwa yayi d'umi tayi wankan, ta wanke bakinta kamar dai koda yaushe kafin ta kwanta sai tayi brush ta daura towel jikinta ya tsane tsaf sannan ta mayar da kayan jikinta ta fito, kwance ta same shi saman gado babu komai a jikinsa sai gajeran wando ga fitilar dakin a kunne! simi-simi ta nufi kan kujerar data ta bari, sunanta taji ya kira cikin ma'koshi, tsayawa tayi ba tare data juyo ba, Yace."Ba kiyi wankan bane."? a sanyaye tace."Nayi." Yace."To cire hijabin kizo ki kwanta." Tace."Abbah kayi hakuri zan kwanta kan kujera." Mikewa zaune yayi yace."Tunda nake da Halimatu bamu ta'ba raba shimfida ba saboda haka bana so mu fara haka dake, kizo ki kwanta a makwancin ki Ni babu abinda zanyi miki.'' yafada yana nuna kusa dashi.
Hawaye suka zubo mata tayi tsaye tana kallosa gami da d'umbun mamakinsa.
Ganin ta'ki zuwa yasa ya mi'ke ya nufi inda take, cikin gaggawa tayi 'kasa da kanta dan gabadaya ji tayi ilahirin tsigar jikinta na mi'kewa sakamakon ganinsa babu kaya a jikinsa.
Yana zuwa ya ri'ke hannunta yaja ta suka nufi bed din, zaunar da ita yayi ya zauna yana kokarin cire mata hijab din jikinta, ta ri'ke hannunsa tana girgiza masa kanta bakinta sai rawa yake tana so tayi magana amma tana gudun yayi mata fad'a.

Bai saurareta ba sai da ya cire mata hijab din yabi jikinta da kallo, Atamfar d'azu ce a jikinta, d'inki kuma mai nauyi ne da dogon hannu gashi garin ana zafi dalili kenan daya sanya shima bai kwanta da riga a jikinsa ba, Yace."Ki dan cire koda rigar jikinki ce sai kiyi daurin kirji da zanin dake jikinki zaki fi jin dadin kwanciya."
Cikin rawar murya da rawar baki tace"A'a ai bana kwanciya babu riga a jikina komai zafi zan iya kwanciya a haka." Girgiza kansa yayi ya raba 'kafafunsa ya jawo ta yasa a tsakiyar sa yana fad'in akwai cutuwa ki kwanta da riga a jikinki. kawai sai ya shiga kokarin cire mata rigar......Rirri'ke hannunsa take tana fad'in "Allah zan iya kwanciya da riga a jikina dan Allah kada ka cire min riga Abba......Bai saurareta ba sai da ya cire mata rigar jikinta yayi saura daga ita sai breziya ganin haka yasa tayi saurin sa hannayenta duk biyun ta rufe kirjinta dasu, hawaye na zubo mata! kokarin mikewa zaune take a jikinsa ya hanata kafafunsa ya hard'e da nata sosai ya matseta a jikinsa, ya kwanta rigingine itama ta kwanta rigingine duk rabin jikinta na jikinsa, bargo ya janyo ya rufe musu jikinsu ya d'ora hannunsa guda saman cikinta dai-dai cibiyarta.....Naja'atu ihu! ne kawai bata kurma ba amma hawaye tuntuni yake gudana a fuskarta..

Addua yake so yayi musu amma ya gagara yi dan gabadaya hankalinsa tashi yayi jikinsa yayi wani irin sanyi wata irin sha'awar yarinyar ce ta taso masa, gabad'aya a yanda ya tsara shine ba zai taki yarinyar ba sai an dan kwana biyu tukkuna yana so ya nuna mata kulawa ne ya kuma nuna mata cewar abinda take tunanin baza ta samu ba dangane da auranta dashi to ba haka bane dalilin da yasa kenan ya shirya tsaf! domin ya siye zuciyarta da kalolin soyayyarsa.

Rintse idonsa yayi yana sauke wata zazzafar ajiyar zuciya, gaskiya da wuya ya iya daurewa dan gabadaya hankalinsa ya tashi jinta a cikin jikinsa, ba tare da yayi tunanin komai ba kawai ya shiga wasa da hannunsa a saman fatar cikinta yana d'an shafa ramin cibiyarta..... Hannunsa da yake yawo a jikinta tayi saurin ri'kewa 'kam! tana wani irin kuka tace"Abbah dan Allah ka bari dan Allah."!! Shuru yayi yana sauke ajiyar zuciya, ita kuma ta kama hannunsa ta ri'ke kamau! tana sheshsheka! Lumshe idonsa yayi yana adduar Allah yasa bacci ya daukeshi ya huta, amma yasan da 'kyar yau ya iya rintsawa sakamakon azababbiyar sha'awar dake taso masa.

Ita kuwa jin ya daina shafa jikinta yasa ta sauke ajiyar zuciya amma dai duk da haka bata sakar masa hannu ba yana d'amke a cikin nata, a wautar ta wai so take yayi bacci sai ta sake shi ta kuma bar masa gadon......Kawai sai taji ya mike zaune da sauri ya burkitata 'kasan gadon, rintse idonta tayi ganinsa yayi mata rumfa zai danneta!
"Wayyo Allahna."! Tafada muryarta na hard'ewa, hannunsa yasa a saman fatar le'banta yana shafawa a hankali a hankali! Tsira masa ido tayi jikinta sai karkarwa yake.
Gani tayi duk ya koma wata kala idanunsa sunyi jawur! duk da ya rage hasken fitilar dakin bai hanata hango tsabar sha'awarta a cikin 'kwayoyin idonsa ba!!

Ganin tana yi masa wani irin kallo ne yasa ya kashe dusasheshen hasken da ya bari a take d'akin yayi duhu lokacin ne kuma Allah ya bata damar ture shi ta mike zaune da sauri tana laluben hanyar sauka, hannunta ne ya sauka kan jikinsa, taji ta ri'ke wani abu mai tauri da kwari a hannunta! a gigice ta saki ta dira kasan bed d'in tana makyarkyata.
Kamota yayi da saurin gaske ya mayar da ita ya kwantar, still ya sake yi mata rumfa da jikinsa.......Hucin numfashinsa ne ya dinga dukan fuskarta hakan ya tabbatar mata da cewar fuskarsa na dab da tata! ta dinga kuka tana kauda kanta!
Saukar fuskarsa taji a tsakanin wuyanta yana sakar mata wasu zafafan kesses (Parsonality) Wanda yayi bala'in rikirkita mata lissafi.......
A take tsigar jikinta ta shiga tashi sakamakon jin yanda yake goga mata gashin fuskarsa a jikinta sai tsikarinta yake yi tana jin 'kaikaiyi!
Bud'e baki tayi da kyar tace."Ab.....Abbah please ka bari ba girman ka bane bana jin dadin wannan abin da kake mun."
Kamar ta 'kara tunzarashi dayin abinda yake yi ya cigaba da goga mata gefan fuskarsa a fuskarta da wuyanta, a jiyar zuciya ta shiga saukewa tana kauda kanta had'e da tutture fuskarsa........Cikin dubara irin tashi ya samu nasarar had'a bakinta da nasa ba tare da tayi tsammani ba kawai sai jin bakinta tayi a cikin nasa yana tsotsa tamkar mai tsotsar alawa! ta dinga kokarin cire bakinta ta kasa saboda ya riga ya ri'ke da nasa! Wasu hawayen bakin ciki da takaici ne suka shiga zubo mata, *Wai yau Abbah Abbas shine ke kissing d'inta baki da baki kai wannan rana ba zata ta'ba mancewa da ita ba*

Shi kuwa wani irin sha yake wa bakinta kamar zai shanye mata ruwan bakinta tsotsa yake yana sa harshensa a sa'ko da lokonan bakinta har wani tallafo kanta yake yana kyarma da rawar jiki, kai!! bai ta'ba jin baki mai sugar irin nata ba wani irin za'ki yawun bakinta ke dashi.....................Da 'kayar ya cika mata harshe aikuwa gabadaya da le'bunanta da harshen suka d'umame da radad'in zafi sakamakon jin ba'kon abu da sukayi suka dinga yi mata zafi da zugi! kuka take tana dukan kirjinsa had'e da turje-turje da kafafunta! Cikin wani irin hali ya sauke daga kanta ya samu gefen gadon ya zaune had'e da dafe kansa!
Gabad'aya yarinyar ta tayar masa da hankali gashi yana ganin ba zai samu biyan bukatarsa ba a gurinta.
Mi'kewa zaune tayi tana kuka tana laluben zaninta domin ta daura a jikinta wannan karon ma a cinyarsa ta d'ora hannunta, jin kamar gashi-gashi yasa da sauri ta cire hannunta! tana matsawa baya! can lokon gadon ta makure jikinta ta janye bedshirt din ta rufe jikinta dashi tana hawaye.

Sautin kukanta ne ya cika masa kunne, ya dan juyo a hankali yana kallon bayansa, duk da akwai duhu a dakin bai hanashi hangota a can 'kuryar gado ba, ya dan shafa kansa cikin wani irin hali na damuwa gami da bukatuwa ya mike ya nufi toilet domin ya tsarkake jikinsa....Har ya fito daga toilet din bai daina jin sheshshakar kukanta ba, sai ya kunna fitilar dakin a take dakin ya gauraye da haske.
Rintse idonta tayi da saurin gaske tana sake matse jikinta guri guda, bed din ya hau, sai ta zabura tana rawar jiki tace"Abbah dan Allah kayi hakuri kada kayi min komai."
Ganin yanda take ta makale jikinta a jikin bed din yasa ya dan janyo hannunta aikuwa ta 'kwala 'kara! had'e da fizge hannunta ta sauka daga bed din tana kare jikinta da bedshirt din hannunta.

Ranshi ne ya 'baci da abinda take yi kawai sai ya rabu da ita ya kai hannu ya kashe hasken dakin, kwanciyarsa yayi ya rufe kafafunsa da blankent.

Ita kuwa kan Sofa ta lalla'ba taje ta zauna tana me tsirawa bed ido gani take kamar zai biyo ta kan kujerar................Abbah Abbas bacci ne ya dauke shi bacci mara dad'i baccin da ya sanya shi mafarkai barkatai. Naja'atu kuwa yanda taga dare haka taga rana sai gefin asuba bacci ya soma fizgarta, jin motsin tashinsa yasa firgigit ta mike zaune tana zazzare ido.

Yana kunna hasken dakin ya mike ya nufi toilet ya daura alwala kamar dai yanda ya saba ya gabatar da nafila kafin ya wuce massalaci.....Sai da ya fita sannan ta sauke ajiyar zuciya ta mike da sauri taje ta duba rigarta tasa ta dauki hijabinta ta zura da sauri ta fita daga dakin.


Dakin su Saddiqa ta nufa koda ta shiga dakin sai ta gansu duk a kwance basu tashi ba, taji dadin hakan da sauri ta nufi toilet din dakin, ta tub'e kayan jikinta, ruwa ta hada tayi wanka kana tayi brush sai ta daura alwala ta fito.....A gurguje ta shirya ta tsaya kan Saddiqa tana tashinta, gabadayansu suka tashi tace"Ku tashi kuje kuyi alwala."
Saddiqa ce ta fara tashi ta nufi toilet din, ita kuma ta gyara dadduma ta tayar da sallah.

Bayan ta idar da sallar kwanciya tayi kan daddumar ta takure jikinta daga zarar ta tuno da abinda ya faru a tsakaninta da Abbah Abbas sai gabanta ya yanke ya fad'i! har yanzu le'bunanta zafi suke mata idan ta tuno da yanda ya dinga shan bakinta tsigar jikinta duk sai ta mike.

Mussadiq ne yazo ya zauna kusa da ita yana gaisheta, ta mike a sanyaye tana amsawa, Saddiqa da Mufida ma suka gaisheta a nutse ta amsa musu............'Dakin ya shigo hannunsa ri'ke da wani maidaidaicin carbi, Naja'atu tayi saurin sunkuyar da kanta 'kasa kwata-kwata bata so ta had'a ido dashi.
Ya tsaya daga bakin kofa yana fadin "Ashe kun tashi." Mussadiq yace."Eh Yaya Naja'atu ce ta tashe mu." Ya d'an kalleta da gefan idonsa, ya kauda kansa yana amsawa gaisuwar 'yayansa, juyawa yayi zai fita yaji muryarta tana gaishe shi, ba tare da ya Juya ba ya amsa, ya bude kofar dakin ya fita.

Gabad'ayan su suka mike zasu fita tace"Ina zakuje."? Saddiqa tace"Zamuje mu gaisa da Mommy ne." shuru tayi tana kallonsu suka fita daga dakin..


Lokacin da suka shiga gaishe da Halisa yana tsaye a dakin suna magana, ya bisu da kallo har suka fita yana mamakin ina ita Naja'atun wato ba taji maganarsa ta jiya ba kenan? a tunaninsa zata biyo yaran suzo gaishe da Halisan tare, Inda ita kuma sam ba tayi tunanin hakaba saboda ba gaishe da Halisa ne a gabanta ba abinda ke gabanta shi ya dameta.........Ya kalli Halisa a nutse yace."To yanzu nawa kike ganin zasu isa.?
Mikewa tayi daga kan daddumar da take zaune tana kokarin cire hijabin da tayi sallah dashi tace"To ka zauna mana sai nayi maka lissafi." Jim yayi kafin ya zauna! dan yana sane ya'ki zama a dakin saboda yasan halin da yake ciki na sha'awa baya so taja ra'ayinsa ya aikata wani abun da ita a cikin hakkin wata.

Zama tayi kusa dashi tana nanikar jikinsa, ya kalleta babu yabo babu fallasa yace."Kiyi min bayanin nace kamar nawa ne zai isa da zaki siyo mata sutturun da suka dace."


Fuskarsa ta shafa da hannunta ta kai bakinta kan kuncinsa ta manna masa kiss! tana me d'ora hannunta a cinyarsa, ganin irin abinda take masa ne yasa ya gane abinda take nufi! Yace."Kin san dai ba'a cikin kwanakin ki kike ba ko."? Marairaicewa tayi tace"Haba ai kaima kasan ba zab iya bari har sai nan da kwana shida ba wallahi, ni dai gaskiya a bukace nake."

Kallonta ya shiga yi yana mamakin maganarta, yace."To nima bani nake da kaina ba sai kije ki tambayi mai hakki idan ta baki aro na shikkenan."

'Bata rai tayi tana sake shigewa jikinsa tace"Allah ya kiyaye na tambayi yarinyar nan wani abu kaine kake da iko da kanka kuma kafi kowa sanin halin da nake shiga idan ina cikin wannan halin dan haka ni ba zan iya sauraran komai ba sai na samu biyan bukatata." Kallonta kawai yake dan shi ya rasa ma abinda zai ce mata, yana jinta tana ta shashshafa jikinsa tana masa salo iri-iri to abinka da wanda dama yake a bukace a take ya bada kai bori ya hau, suka shiga biyawa junansu bukata...

Gabad'ayansu har ita suka fito palo suka zazzauna suna hira kar'fe takwas shuru basu ga gilmawar masu gidan ba, tara ma tayi shuru, basu fito ba, A hankali ta kalli Mussadiq tace"Ko Abbanku ya fita ne."? Yaron ya girgiza kansa da fad'in "Wallahi ban sani ba dazu dai da muka shiga gaishe da Mommy na ganshi a dakin."

Shuru tayi tana nazarin maganar yaron, ta kalleshi cikin sanyin jiki tace"Kana jin yunwa ko."? Kai ya d'aga mata, mi'kewa tayi ta kalli Saddiqa da Mufida tace"Kuzo ku nuna min kicin din na had'a muku break fast." Suka mike da sauri suna murna, tare suka shiga kicin din nan suka shiga aiki kowanne ta bashi abinda zai taimaka mata dashi..............Halisa ta samu abinda take so sosai ta ri'ke wuta ta'ki barinsa ya huta shi kuma jinta zam-zam! ya dinga d'imautar dashi ya kasa hakura da ita suka dinga abu daya kamar jaraba koda yake dama can sun saba tunda jajayen sawun su......Sai kusan goma da rabi ya fito daga dakin, lokacin su har sunyi break dinsu suna zaune dai a palon suna hira wanda take saka musu baki jefi-jefi......Ido suka had'a ita dashi lokacin da ya fito daga dakin Halisan duk sai ya diririce! lokaci guda ta gane rashin gaskiyarsa kuma ta gane abinda suka dade sunayi a dakin, wace irin magana ce za'ace an shiga daki sama da awa uku anayi ai da akwai alamun tambaya.........'Dauke kanta tayi sam bata wani ji ciwo ba dan ba wai sonsa take ba ballanta taji haushin abinda sukayi mata, cigaba tayi da dan dudduba wayarta dake hannunta, Shi kuma da sauri yake kokarin shiga dakinsa.....Mussadiq yace."Yawwa Yaya Naja'atu ga Abban namu ya fito dama nace miki bai futa ba."
Da sauri ta kalli yaron tana d'an hararasa! Shi kuma Abbah Abbas din tsayawa yayi yana kallon Mussadiq din yace."Waye yazo nema na."? Shuru tayi, Mussadiq yayi karaf yace." 'Dazu ne Yaya Naja'atu take tambaya ta wai ko ka fita saboda munji shuru bamu ga ka fito daga dakin ka ba shine nace mata kana dakin Mommy."
Naja'atu taji kamar ta kwad'awa yaron mari! kada fa Ya d'auka ko sonsa take shiyasa take tambayarsa

Shi kuwa Abbah Abbas murmushi yayi yana dan shafa gemunsa ya kalleta a nutse yace."Ina tare da Halisa muna tattauna

16 / 17