Madadi 1 Complete Hausa Novel

Author :  Binta Umar Abale Category :  Romance

Chapter   11 / 17

30K to 33K   out of 48.8K words

KU BIYA KUDIN LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS.........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE.*


*🗯️MADADI!!💍*
_(Ba Haram Bane!!)_

*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
~~~~~~~~~
*12* Cikin wani mawuyacin hali Halisa ta tashi duk jikinta yayi mata mugun tsami! ga wani irin ciwo da kanta ke mata, da kayar ta rarrafa ta shiga dakinta ta zauna bakin gado tana ri'ke kanta, a maimakon tayi addua kawai sai ta fashe da kuka tana fad'in mugwayen kalmomi a kan mijin nata saboda kawai yace zai yi mata kishiya shine take addua Allah yasa ya samu karayar ariki komai nasa ya lalace! Allah yasa ya taulace ya zama wanda bashi da cin yau bare na gobe insha Allahu kuma Naja'atu sai ta zame masa masifa a rayuwarsa, tana kuka take wannan surutan tamkar wata mahaukaciya, Cikin wannan yanayi suka shigo gidan shi da yaran gabad'aya dan dubara yayi wa Baba malam yace zai tafi dasu Mussadiq saboda zasu koma makaranta, baba malam baiji dadin haka ba dashi da Abba Magaji sun fahimci cewar abinda Naja'atu tayi musu ne yasa yaji sha'awar dauke yaransa.......Kai tsaye Dakinsa ya nufa yana so ya samu nutsuwa sosai kafin ya tunkari Halisan dan ya fahimci dole sai ya karyar da kansa mussaman yanzu da ya dauko nauyi 'yayansa ya d'ora mata.........Mufida da Saddiqa Mussadiq suka nufi bedroom din Halisan nan suka tarar da ita ba yanda take sai sambatun surutai take da alama dai har yanzu mutanan nata basu gusa daga jikinta ba, Mufida taje ta zauna kusa da ita tare da dafata tana kiran sunanta.........Saddiqa da Mussadiq a bakin kofa suka tsaya saboda dama can sun san halin masifar Halisan ba kaunarsu take ba sai taga Abbansu take yi musu magana da wasa da dariya, shiyasa suka kasa 'karasawa, Halisa ta juyo tana kallon 'Yarta Mufida ganin su Saddiqa a tsaye a bakin kofa yasa ta mike tsaye a furgice tace"Ku dan Ubanku waye ya kawo ki gidana maza ku fuce mun daga d'aki shegu tsinannu 'yayan asara."! Saddiqa da Mussadiq suka zabura! a tsorace suka fita daga d'akin sukaje suka nemi kujerar palo suka zauna jikinsu sai rawa yake dama can Saddiqa da Mussadiq suna masifar tsoron Halisa Naja'atu ce take musu maganinta.......Mufida na goge hawaye tace."Mommy ya kike zaginsu su Yaya Saddiqa ne fa 'yan uwana." Wani irin bahagon mari ta kifawa yarinyar tana huci! tace"Zanci Kutumar ubanki wallahi shegiya munafuka ni zaki fad'awa su d'in 'Yan uwanki ne? Wallahi duk ranar da kika 'kara kiransu da sunan 'yan uwanki sai naci ubanki." Mufida tana kuka tace"To mommy me yasa kika tsanesu bayan mamansu ta mutu dan Allah ki daina yi musu abinda kike musu babu kyau."! A fusace! ta sake gaura mata wani mari tana wata irin fuffuka tace"Tashi dan babanki mara mutunci ki bar min dakina ko kuma yanzu na sumar dake." A gigice! yarinyar ta mike hannunta dafe da kuncinta ta fita daga dakin tana kuka, wanda yayi dai-dai da fitowarsa daga daki yana sanye da jallabiya ruwan toka, Ganinsu Saddiqa sunyi muzu-muzu a zaune yasa jikinsa yayi sanyi ya kalli Mufida dake dafe da kunci tana kuka, yace."Menene? Cikin rawar murya tace"Mommy ce ta mare ni tace na fito mata daga d'aki. Ba tare da yace."Komai ba ya kama hanyar dakin Halisan, Har yanzu tana zaune gefan gado ta had'a tagumi babu maganar sallah a tare da ita, cikin nutsuwa ya shiga dakin bakinsa dauke da sallama, Kallonsa ma ba tayi ba ballanta ta amsa masa sallamarsa, gefanta ya zauna yana kokarin ri'ke hannunta ta fizge a fusace! ta mike tsaye tana nunashi da hannu tace"Kaga dan girman Allah ka fita ka bani guri naji da abinda ke damuna baka da abinda zaka ce dani." Yaji zafin maganarta amma sai ya danne ya mike ya iske inda take, Rungumeta yayi a jikinsa yayi amfani da wata murya wacce ya tanade ta dan rarrashinta, yace."Haba Halisa wai duk me yayi zafi ne kike nema ki zautar da kanki akan abinda bai kai ya kawo ba! Menene abin damuwa dan nace zan auri Yarinyar nan Naja'atu? idan kin kwantar da hankalinki kin ri'ke girmanki sai kinfi daraja da kima da martaba a idona! Shin wai baki ga yanda Halimatu ta sadaukar da rayuwata a kaina ba, bana shakka ko tantama Halimatu yanzu tana gidan aljanna saboda ta rabu dani da iyayenta lafiya, kuma ta mutu hanyar haihuwa, har na gama rayuwata ta duniya bazan ta'ba mantawa da Halimatu ba, a kwanakin baya kin soma kwaiwayon hali da d'abi'unta amma tashi guda zaki watsar da abin da kika fara na alkairi, wallahi auran Naja'atu da zanyi ba zai sanya ni na daina kaunarki ba, kin san dai kece macen dana fara furtawa kalmar so, ko Halimatu ma kece kika jawo na aureta, to itama Naja'atun ina so ki sani bani ne nace inaso ta zama *Madadin 'Yar uwarta ba* Iyayenta ne suka nemi haka dan ko yanzu sai da na fada musu cewar maganar auran su barta suka nuna sai anyi So inaso ki kwantar da hankali ki samu nutsuwa ki kula dani da yarana gasu nan na kawo miki su ni kuma insha Allahu zan baki mamaki zan nuna miki ni d'an halak ne auran Naja'atu ba zai sa na juya miki baya ba." Shuru tayi jikinta duk yayi sanyi da kalamansa tace"Nifa ban hanaka aure ba wallahi ko budurwar zaka aura to kaje ka aura amma banda yarinyar nan bana kaunarta saboda bata ganin girmana." Yace."Na fad'a miki fa cewa kece uwargidana duk ragamar mu tana hannuki har ita Naja"atun idan tazo a 'karkashin ki take sai abinda kika tsara a gidan shi za'ayi." Jin wannan maganar tasa yasa ta sauke ajiyar zuciya tace"Nifa wallahi nasan dadin baki ne kake mun yarinyar nan na zuwa zaka manta dani, dan haka gwara tun kafin tazo na san inda dare yayi min dan bana tunanin zan zauna da ita a karkashin inuwa guda." Yace."In banda abinki ba gidanku daya ba to me zai dame ki da ita ko wacce na gidanta idan wannan da kike ciki bai miki ba sai na sauya miki wani." Tsaki taja tace." bazan yarda ba wallahi sai dai ka had'amu gida daya dan bazan amince a cutar dani ba." Yace."To shikkenan duk abinda kike so shi za'ayi, Zan sa a gyara miki side d'inki dake gidana na *'Danbare* ina fata hakan yayi miki." shuru tayi tana zum'bura baki, Ya saketa yaja hannunta suka zauna a nutse yace."Ki fad'a mun duk abinda kike so na siya miki na fad'ar kishiya komai tsadarsa zan siya miki." Tace"Sai nayi shawara tukkuna." Dariya ta bashi amma beyi ba yace."To shikkenan inaso na baki kudi kije ki had'o mata lefe kuma kema ki had'a naki hakan yayi miki." Dadi ne ya rufe ta tace"To Hakan yayi amma inaso ka sanja min mota." Yace."An gama ranki ya d'ade! amma dan Allah daga yau sai yau kada ki sake aikata abinda kika aikata a d'azu! rashin hankali ne kawai kije ki dauko wu'ka kina so ki kashe ni! kina tare da shed'an a lokacin idan da tsautsayi sai ki aikata aikin dana sani ki 'kare rayuwarki cikin uku'ba kuma ki mayar min da yara marayu." Hanci ta sha'ka! cikin takaici tace"Haba ai wallahi idan ma nayi maka rauni ban huce bacin raina ba, kana kallonta ina magana ka tsalleke ni ka tafi ai dole zuciya ta ta tunzurani a kanka." Yace."Tom yanzu dai duk magana ta wuce Gobe insha Allahu bayan sakkowar sallahr juma'a za'a daura auran amma ina tunanin ba zata tare ba sai nan da sati biyu." Halisa gabanta ya fad'i tace"Da wuri za'a daura auran ashe."? Yace."Baba Malam ne ya yanke hukuncin haka." Cikin tsabar bakin ciki da takaici tace"Aikin banza aikin hofi 'kwad'ayayyen tsoho mai son abin duniya ai dama dole ya gaggauta yin abun kodan bukatarsa ta biya." 'Bata rai yayi yace."To yanzu zamu 'bata dake kuma bana son wannan d'abi'ar taki ta zage-zage da rashin ganin girman manya." Cikin fusata! ta mike ta nufi toilet tana surutai da 'kananun maganganu, kallo ya bita dashi, Al'amarin Halisa dai sai gyaran Allah, yaji dadi sosai da ya shawo kanta cikin ruwan sanyi *(Tabbas haka maza ya kamata su dinga rarrashin matansu idan zasu 'kara aure, sau tari wasu mazan sune suke ingiza zuciyoyin matansu ga aikata abinda ba shikkenan ba, idan ya kasance zaka 'kara aure to yana da kyau ka dinga nuna kulawarka a kan matarka ta gida, kuma banda kiran wayar amarya a cikin gidan dan hakan ma na iya janyo muku samun sa'bani a tsakaninku*) Mikewa yayi ya fita daga dakin yana dan jin sassauci a cikin zuciyarsa tunda ya gama da matsalar Halisa yana ganin duk abinda zai biyo baya mai sauki ne.
Yana fitowa palon ya gansu a zaune duk sunyi tsuru-tsuru Mussadiq ma gyangyadi yake, Ya kalli Saddiqa data had'a tagumi hannu bibbiyu har yanzu zuciyarta na jin ciwon abinda Naja'atu tayi musu a d'azu duk da take yarinya wacce bata gama mallakar hankalin kanta ba ta gane ba 'karamar 'kiyayya Naja'atu keyi wa Abbansu ba, sai ta dinga tunanin to wai meye aibunsa da har zata dinga 'kinsa da kuma zaginsa, sam bata ta'ba tsammanin haka daga gareta ba...... a nutse yace."Saddiqa kuje ku kwanta kinji ko, dukkaninku ku daina damuwa ku saki jikinku a gidan nan gidanku insha Allah ba zaku samu wata matsala ba." Saddiqa murya na rawa tace"To Abbah." Ya sunkuya yana d'an tashin Mussidiq ya tashi yana mutsika ido, ganin Abbansa yasa ya bude idonsa sosai, Abba Abbas d'in ya rike hannunsa ya mike tsaye.........Shi da kansa ya rakasu d'akin dama gado uku ne mai dauke da madaidaiciyar katifa da pillo da bargo, Mufida ta gyara nata ta kwanta, Abbah Abbas da kansa ya shimfidawa Saddiqa da Mussadiq sabon bedshirt ya gyara musu sosai sannan suka kwanta, Ya tsaya kansu yayi musu addua sosai kana ya fita daga dakin tare da kulle musu kofa.............To bayan barin Abbah Abbas daga gurin Malam Baba shima Abbah Magaji sallama yayi masa kancewar kafin ya shiga gidansa zai tsaya ya siyi dik abinda za'a bukata gurin daurin auran, Malam yaji dadin hakan yace."Dashi kafin ya tafi ya shiga gidan Alhaji domin ya sheda masa abinda ke faruwa, koda Alhaji yaji bayanin da Abbah Magaji yayi masa sai ranshi ya 'baci! ya za'ayi sun riga sun gama magana da Abbah Abbas din kan cewar ya janye maganar auran yarinyar kuma dan yaga baya gurin zai sauya magana, yaji haushin hakan ya dauki laifi kacokan ya d'orashi kan Abbah Abbas d'in, Dan 'kin tsayawa ma yayi ya saurari bayanin da Abbah Magaji ke masa, ya sauko daga samansa, kai tsaye futa yayi daga gidan, Abbah Magaji na binsa a baya........Malam Baba yayi mamakin fusatar Alhajin kasancewar yasan shi d'in mutum ne mai saurin fahintar abu da kuma sau'ka'kawa cikin ko wane al'amari.......Da 'kyar Baba Malam da Abbah Magaji suka fahimtar dashi ya gane cewar ba laifin Abbas din bane sune suka tursashi......Alhaji Sama'ila yayi shuru yana ta nazarin al'amarin, daga bisani kuma addua yayi da fatan alkairi tabbas tunda Allah yayi haka to babu alkairi a cikin auran Naja'atu da Salim d'in,......Shine ya sake 'karfafawa Abbah Magaji, cewar yayi 'kokarin tana dar duk abinda ake bukata a gurin daurin aure tabbas babu makawa gobe auran Naja'atu da Abbas sai ya d'auru.........Sai misalin goma da rabi sukayi sallama da juna kowanne ya shiga gidansa cikin fatan alkairi ga junansu.........Baba Malam kafin ya kwanta sai da ya sanar da Baba Talatu abinda ake ciki na irin hukuncin da suka yanke cewar Za'a daura aure gobe dan jan lokacin bashi da amfani, Baba Talatu taji dad'in hakan sosai kuma tayi fatan alkairi dangane da al'amarin.....Naja'atu dake takure kan shimfidarta a lokan rumfar luf!! tayi kamar mai bacci tana sauraran maganganunsu, sai da taga sun shiga daki, da niyar kwanciya sannan ta mike a hankali ta dauki wayarta dake kusa da ita ta mike ta fita daga dakin ........Daya dakin ta nufa tana shararar da hawaye, xaman 'yan bori tayi tana toshe bakinta domin kada sautin kukan da take ya fita suji, wayar ta kunna hannunta na kyarma ta shiga laluben numbar Abbah Abbas d'in, tana jin idan bata zageshi ba zuciyarta na iya bugawa.........Yana zaune a palo shi kadai da Loptop a gabansa yana duba sa'konnin abokan kasuwancinsa na 'kasashen waje, Kiran wayar ta ya shigo wayarsa dan duban wayar yake hankalinsa na kan typing din da yake cikin loptol din, koda yaga numbar Naja'atun baiyi gaggawar dauka ba, ya janye idonsa ya cigaba da abinda yake Naja'atu! ta dingi kiran wayar tamkar zata kashe masa dodon kunne dole ba yanda ya iya ya daga wayar tare da gyaran murya babu wasa a cikin muryarsa yayi sallama....
'Dif! tayi gabanta na wata irin fad'uwa! sakamakon jin sautin muryarsa mai cike da kwarjini da rashin wasa yasa ta mance abinda yasa ta kiransa a wayar sai mazari jikinta yake tana sha'kar hanci had'e da sauke ajiyar zuciya irin na wanda yaci kuka ya 'koshi........'Dan gyaran murya yayi a karo na biyu yace."Dota ya akayi ne dare yayi baki bacci ba."......Murya na rawa tace"Me yasa ka san ni 'yar kace kake shirin aurena."? Shuru yayi yana nazarin maganarta, Yace."Eh abinda yasa nake kiran ki da Wannan suna (Dota) saboda nasan a matsayin shekaruna da Allah ya bani haihuwa da wuri dana haife ki kamar ki ko wacce ta fiki so ina ganin babu laifi dan na kira ki da wannan suna."!A hasale! tace." To tunda dai da bakin ka ka fad'a cewa a matsayin shekarunka da Allah ya baka haihuwa zaka iya haifeta ko wacce ta fini me zai sanya ka zubar da k'ima da mutunka a gurina ni da ka 'rike kamar 'yar cikin ka, ka sani ba da badan mutuwa ta ratsa tsakanin ka da matarka ba da kowa yana maka kallon matsayin uba a gare ni." Murmushi yayi wanda har sai da taji sautinsa a kunanta Yace."Nifa ban haife ki ba ki daina kirana Ubanki yanzu sunan da yafi kamata ki kirani dashi shine Mijin ki dan gobe idan Allah ya kaimu iwar haka kin zama matata"! Taji tamkar ta d'ura masa ashar! sai dai ta daure taja wani matsiyacin tsaki! mai 'karfi! da fad'in "Amma dai anji kunya wallahi."!! Kit! ta kashe wayar tana wani irin huci!!! Abbah Abbas ya dinga bin wayar da kallon mamaki! Yau shi yarinyar nan take jawa tsaki har tana kokarin zaginsa, Kasa hakura yayi ya sake kiran wayar! A fusace! ta d'aga ta bud'e baki za tayi magana, ya buga mata wata masifaffiyar tsawa! da fad'in " Dan Ubanki ni kike zagi ashe baki da mutunci dama."!? Jikinta ya shiga karkarwa domin tsawar da ya buga mata bata ta'ba saninsa da ita ba, kashe wayar tayi gabad'aya ta kwanta tare da takure jikinta tana kuka mai tsuma zuciya, ta kirasa a waya domin ta farfad'a masa magana mai zafi 'karshe shi ya fad'a mata maganar data ya mutsa mata tunani har da zagin Ubanta..........Abbah Abbas ya ajiye wayarsa a fusace! ya rufe loptop din ya mike ya nufi bedroom d'in Halisa........... *Sorry kuyi hakuri waya ta ta d'an samu matsala wallahi zaku ga yanayin typing din ba irin yanda na sababa........Ina ro'kon Ubangiji Allah ya kawo mana zaman lafiya a wannan 'kasa tamu ta Najeria Ubangiji Allah ka bamu nutsuwa da daidaito a tsakaninmu amin.........MY FANS KADA MU MANTA DA SALATIN ANNABI A WANNAN RANA MAI ALBARKA SANNAN KUMA MU DAURE MU KARANTA ABINDA YA SAWWA'KA DAGA CIKIN SURATUL KHAFI.*
*************************GA MASU BUKATAR KARANTA BOOK DIN ZASU TURA #400 SINGLE, VIP GROUP #600 GA ACCONT D'IN DA ZA'A TURA KUDIN.......0542382124.....BINTA UMAR GTBANK.....IDAN KATIN WAYA ZAKI TURA KIYI MIN MAGANA TA WHASAP DA WANNAN NUMBAR......07084653262.....IDAN KIN SAN BA BIYAN KUDIN LITTAFIN NAN ZAKI YI BA DON ALLAH KADA KI KIRA WAYA TA KO KIYI MIN WATA MAGANA TA WHASAP

*MUTANAN MU NA NIJAR IDAN KUNA SO KU BIYA KUDIN LITTAFIN ZAKU TURA DALA DARI TA WANNAN NUMBARS.........90899076_88137740 KATIN AIRTAL KO ORANGE.*


*🗯️MADADI!!💍*
_(Ba Haram Bane!!)_

*NA*
*BINTA UMAR ABBALE🍒*
~~~~~~~~~
*MANAZARTA WRITES ASSOCIATION📚🖊️*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
~~~~~~~~~
*13*
Ranshi a 'bace! ya aje loptop din kan wani tevur ya nufi toilet alwala ya daura ya fito ya hau kan dadduma ya tayar da sallahr nafila, raka biyu yayi ya daga hannunsa sama yana rokan Allah ya za'ba masa abinda yafi alkairi a rayuwarsa, kwata-kwata ji yayi auran yarinyar ya fice masa daga rai! a sabili da irin iskancin da wulakancin da take masa da shida 'ya'yansa bai ta'ba tsammin faruwar hakan daga gurinta ba yana ganin barin auranta kamar shi yafi alkairi don baya so da girmansa da komai yarinya k'arama tazo tana fada masa maganar da duk ta gadama, mikewa yayi daga kan dadduma yaje ya kwanta kusa da Halisa, ya d'an janyo ta jikinsa,
Bude idonta tayi ta wani fizge jikinta tana jan tsaki! Al'amarin sai ya bashi mamaki! ganin cewar d'azu suka gama magana da ita kan cewar komai ya wuce amma saboda ya ra'bi jikinta tana fizgewa, bai yi zuciya ba ya sake kai hannu zai janyota ta mike zaune tana 'bata fuska tace"Nifa ba zan sake amincewa da bukatarka ba sai na yankewa kaina hukunci tukkuna dan gaskiya ni maganganunka na dazu basu shige ni ba."
Ya mike zaune yana kallonta cikin d'umbin mamaki! yace." Wane irin hukunci zaki yankewa kanki bayan wanda muka yanke d'azu na dauka yanzu dani dake mun zama d'aya, ashe duk maganar da mukayi dake dazu ta banza ce." Tace."Kawai ka rabu dani na cigaba da tunanin mafita ni ba zan sake amincewa bukatarka ba kaje idan an daura auranka da 'karamar yarinya sai ka sauke bukatarka a kanta." Cikin tsabar takaici yace."Halisa ban ta'ba ganin mara hankalin mace irin ki ba wallahi kin girma amma har yanzu kin 'ki hankali 'Yar cikin ki Mufida ta fiki nutsuwa."
Tace."Duk dai abinda za kace a kaina kace ba

11 / 17