Kanwar Maza 1&2 Complete Hausa Novel

Author :  Ayshacool Category :  Love

Chapter   50 / 61

147K to 150K   out of 182.7K words

yi shiru da bakinsu".

Ya girgiza kai ya ce "Ammi, kin manta gidan nan ne, lokacin da aka fitar da zancen ina shaye-shaye na yi yin?urin yi wa iman fyaWe, mutum nawa ne a wurn, wa zaki kama ki tuhuma ki ce shi ne? Haka wannan Win ma, dole zan matsa lamba yarinyar nan ta yi mini bayani, na san in da zan nemi mafita"

Ammi ta yi shiru, abubuwa sai sake cakuWewa suke yi, ba a warware wannan ba wancan sai ya kunno kai.

"Ammi, meyasa ki ka amince da sakawa yaron nan Mahmud? Ni ba sunan da zan saka masa ba kenan, sunan Alhajinmu na so mayarwa, ni bana son sunan nan"

Ammai tayi murmushi mai ciwo ta ce "Haba babban mutum, ban ji daWin jin wannan maganar daga bakinka ba, a bar wannan zancen dan Allah, ina ro?a mata alfarma, a bar mata wannan sunan tun da shi take so".

Takawa ya Wan du?ar da kai ya ce "Tuba nake".

Bayan tafiyar su takawa kuwa Abdallah ne a Wan hasale ya ce wa ruma "Dan ubanki ba a yi wa masu mulki magana yadda ki ke yi musu, gatse-gatse babu Wa'a, wai ma ke kowa sa'anki ne da zaki din ga magana son ranki? Na fuskanci ba ki yi laushi ba haryanzu. To wallahi sai an basu Wan su, ke gama rainonki aka yi da zaki janyo mana wani? Ki kuma cewa Wanki ne ki ga yadda zan yi da ke" Jin Abdallah kawai take yi, amma gani take idan zasu mayar da ita ?uli, babu wanda zai rabata da jaririn nan.

Washegari 'yan Katsina su gwaggo da iya, da sassafe suka yi dirar mikiya a Kano, yayin da 'yan uwa da abokan arziki, malaman islamiyya da makarantar bokonsu rumaisa, haka mutane daga lungu da sa?on unguwa, suka din ga zuwa dubiya gami da jajen abun da ya samu rumaisa, sai dai fa unguwarsu rumaisan ta Wauka a kan jaririn da rumaisa ta dawo shi, nan da nan zantuka kala-kala suka hau zagaya cikin unguwa, masu daWi da marasa daWi a kan rumaisa.
Aliyu ya cika al?awari, ya kawo Habiba har Wakin da rumaisa take na jinya,ita da babarta, suka rungume juna suka din ga kukan farin ciki.

Gwaggo kuwa sai da ta yi kuka tana neman mama ta yafe mata da ta sanya a ka kai ruma aka Soye, ta Wora alhakin faruwar komai a kan ta, har da su lawisa duk aka zo, rumaisa ta yi farincikin yadda mutane ke ta shiga suna fita duk saboda ita.

Sai dai duk rawar kan rumaisa ta?i sakin jiki ta basu labarin abun da ya faru a zamanta a hannun 'yan ta'adda, ko zancen aka Wauko sai ta haWe rai ta hau kuka, gashi haryanzu lokaci zuwa lokaci tana razana, haka kurum tana zaune sai ta hau ihu, tana kiran sunayen 'yan bindigar ta ce zasu yi mata wani abu, har sai da mai sunan Baba ya hana yi mata zancen gaba Waya.

Tun da aka rubutawa rumaisa hoto, mama ta aika Abubakar ya tambayo kuWin hoton, aka ce masa dubu arba'in da uku, mama ta Wan shiga damuwa, domin kuWin da yawa, ba ta son yawan Worawa yaran Wawainiya, dan ma kuWin asibiti da na magani ba biya suke yi ba, an riga an Wau nauyin lafiyar rumaisa a aljihun takawa, dan tun da bashir ya ji yaron nan na Adam ne, ya sanya aka canza musu asibiti zuwa babban asibitin kuWi, domin samun kulawa ta musamman tun da ya san adam yana da kuWin biya, ko magani likita ya rubutawa ruma, sai dai kawai a Wauko a kawo musu, sai dai wanda babu su je waje su saya.

***
Tana zaune a kan katafaren gadonta, sai shirya mata kayanta mai aiki take a cikin akwati, dan ta ?allafa ranta a kan tafiyarta Abuja nan, sai ba wa mai aikin umarni take cikin isa da kuma gadara gami da wula?anci.
Samha kenan akwai gayu da ?walisa, sai dai babu hali mai kyau, Waya daga cikin wayoyinta ta duba ba ta gani ba, ta js Wan gajeren tsaki, ta fita ta tafi Wakin mama.
Mama ta tarar tana ta ?ananan surutai tana mita. "Mama na bar Samsung Wina a Wakin nan ne?".

"Ke ni rabu da ni da wata wayarki, turaki ya Sata mini rai".

Samha ta ce "Too ikon Allah, mai Baban kuma yayi miki?"

"Manta kawai, jirgin ?arfe nawa zaki bi?"

Samha ta Wan yi ajiyar zuciya ta ce "?arfe biyar na yamma, amma ki din ga ha?uri mama, kin san tsufa yana taka muhimmiyar rawa a kansa yanzu, idan ki ka matsa zaki yi ta damuwa ne ranki yana Saci".

?an shiru mama tayi sannan ta ce "Abun nasa dai ba tsufa bane, ba wani tsufa kawai halinsa ne, ina yi masa maganar wani abun daban, amma yana nuna mini maganata ba ta da muhimmanci yana kawo mini nasa zancen da bai shafeni ba".

Samha ta yi murmushi ta Wau wayarta ta ce "Na san tatsuniyar gizo ba ta wuce ?o?i, yakamata ace zuwa yanzu kin saba mama, ki yi ha?uri, bari na je na cigaba da shirina" daga haka ta fice ta koma Wakinta.

***
Abubuwa suka cakuWewa Adam gaba Waya, kallo Waya zaka yi masa ka san a cikin tashin hankali yake da matsananciyar damuwa, Ammi ta ce sam ba ta yarda ya je gidansa ya zauna shikaWai ba, don tun da ya shiga damuwar nan take cikin fargaba, kar ciwonsa ya tashi abu ya ?ara haWe musu.
Yau da safe Ammi da kanta ta je ta saka Adam a gaba a kan ya ci abinci amma ya kasa ci, sai da ya ga ta matsa sosai da sosai sannan ya Wan cakali kaWan ya bar shi.

Ammi ta dube shi a tsanake sannan ta ce "Takawa" ya Waga kai ya dubeta.

"Yanzu meye abun yi ne? Me ka yanke a kan lamarin nan, kuma ya ake ciki game da binciken?"

Ya Wan yi jimm sannan ya ce "Dama Bashir ne incharge Win da case Win yake a hannunsa, sannan police Win da case Win yake hannunsu suna ta ?o?ari, ina ga in anjima za su je asibitin da kansu, su yi mata tambayoyi".
Ammi ta Wan sauke numfashi sannan ta ce "Bana son a cigaba da yawan matsawa yarinyar ne a kan maganar, na ga haryanzu tana cikin razani, dole a bita a hankali".

Adam a ransa ya ce "Babu wani razani, tsagwaron iskanci ne, kuma da ni take zancenta, ba zan lamunci iskancinta a kan rayuwar matata ba'

Amma a zahiri ya ce "Amma Ammi dole ta yi magana domin gaggauta ceto Aisha".

"Eh haka ne, amma ita ma 'ya ce, kuma yakamta a bita a sannu, saboda lafiyar ?wa?walwarta, kana kallona gabanka jiya take ihu wai an harbe wani" Ammi ta dafe goshi ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ya shiga tsakanin na gari da mugu, dole yarinyar nan ta shiga ruWu, ayi kisan kai a gaban yarinya ?arama kamar wannan"

Shiru Adam yayi, yana ta addu'a Allah ya sa Aisha tana lafiya.

Ya kalli ammi ya mi?e tsaye ya ce "Ammi, bari na je asibitin nan da kaina".

"A'a kar fa ka je ka nuna musu zafin zuciya da zafin kai, ka bi komai a hankali".

Ya girgiza kai ya ce "Ba wani abun zan yi ba, kin san yau za'a kai ta x-ray, so nake na je na ga yaron, in kuma jarrabawa ko zata yi magana".

"To shikenan, ka gaishe su, ni sai zuwa dare in Allah ya kaimu na je" ya jinjina wa ammi kai ya fice.

Likita ne a tsaye a kan rumaisa da take ta bacci, tun bayan da mama ta yi mata wanka, ta yi wa jaririn, ta kwantar da shi a kusa da rumaisa suke ta bacci, haka nan mama ma yaron ya shiga ranta, ga yaron da matu?ar ha?uri, idan yayi kuka ko dai ya gaji da kwanciya ko kuma yana jin yunwa, daga bacci sai cin hannu kawai yake yi, mama ba ta taSa jin ta gaji da Wawainiyar da take da Wan da bata da ala?a da shi ba, ji take yi hakkinta ne na uwa ta kula da shi, gefe guda kuma tana matsanancin jin tausayinsa tare da fatan Allah ya kuSutar da mahaifiyar sa, ita kanta da ta Waukowa rumaisa zancen uwar yaron, sai ta hau zabure-zabure.

Likita yana duba file Win ruma yana kallonta, mama ta ce "Likita babu dai matsala ko?".

Ya ce "Eh babu, duk wasu gwaje-gwaje da yakamata ayi mata mun yi mata, babu wani mummunan ciwo a tare da ita, sai dai zan rubuta wata allaura a sayo ayi mata, saboda ciwon ha?ar?arin da take kuka da shi, kan ku yo hoton".

"Eh, in anjima za aje yin hoton in Allah ya yarda, dan sai daf da asuba ta samu bacci, da gari ya waye na tasheta, tana ta kuka da wurin".

Ya ce "In sha Allah idan aka yi allurar, za ta samu releif, kan muga sakamakon".

Mama ta Wan nisa sannan ta ce "Amma likita ba su yi mata wani abu ba dai ko? Basu taSa ta ba kun duba?".

Ya jinjinawa mama kai ya ce "Ki kwantar da hankalinki, akwai report da police suka bamu, tun daga asibitin farko da aka kaita, da na biyu zuwa nan, muma da namu binciken, komai lafiya ?alau".

Mama so take ya bata amsa ?arara, amma kamar bai fahimci me take nufi ba, ba ta son ya ga kamar ta matsa masa, dan haka ta ?yale shi".

Ganin yadda rumaisa ke kuka da ciwon ha?ar?arin nan ya sanya ta ce bari ta yi sauri ta je ta sayo allurar, gashi da wuri Abdallah ya tafi, yau yana da jarrabawa a makaranta, gwaggo kuma daga ita har iya suna fama da jikin girma, suma mama cewa tayi su tafi gida su huta, dan haka ganin ruman na barci ya sanya ya fito nursing station ta ce musu dan Allah ga rumaisa nan, za ta je sayo allura.

Mama na fita takawa ya iso asibitin, dan direba ya saka ya kawo shi, shi ba zai iya tu?in ba.

Yana daf da shiga Wakin da rumaisa take, likita ya fito daga Wakin kusa da nata, suka tsaya suna gaisawa.

Takawa ya tambayi likitan ya jikin jaririnsa?.

Likita ya ce "Baby yana nan lafiya Alhamdilillah, shi ya samu sau?i sosai Alhamdilillah, mamansa ce dai iya rigima haryanzu muna fama ba ta warware ba, muna jiran sakamakon hoton da zamu turata mu san abun yi na gaba".

Adam ya ce "Haryanzu ta ?i magana a kan in da mahaifiyar yaron nan take, da an yi maganar sai ta hau ihu, dan Allah hakan yana da nasaba da razani ko kuma iskanci ne kawai"

Sai da doctor yayi dariya ya ce "To kowanne ma zai iya kasancewa, amma razani kam tabbas tana cikinsa haryanzu, wasu lokutan tunanin ya kan ?wace mata ta zaci tana hannunsu haryanzu, amma abi komai a hankali, sannan dan Allah idan ku ka tashi karSar yaron nan, ku bita a hankali ta sha?u da shi sosai, kar ku rabata da shi lokaci Waya".

Bayanin likitan na yanzu ya shiga ta kunnen Adam na dama, ya fita na hangu, dan bai ji zai iya saurarawa ko Waga ?afa wurin karSar Wansa ba, yanzu ma don yana cikin tashin hankali ne, da damuwa da son sanin in da matarsa take, ba dan haka ba, da tuni ya Wauk Wan sa.

"Thank you very much" ya faWa a ta?aice ya shiga Wakin rumaisa.

Sai dai yayi mamakin ganin babu kowa, baccinta take hankali a kwance, gefenta ga jaririn shi ma yana barci, kai ka ce uwarsa ce.

Ya ?arasa gaban gadon ya tsaya ya ?are mata kallo, a haka tana bacci looking so innocent, amma a zahiri halinta idan ba ka kai ziciyarka nesa ba, sai ta sa zuciyar mutum ta buga.

Ya kalli ?afarta da aka rage bandejin da ake saka mata, saboda raunukan da suke ?afar, ga wani yanka a ?waurinta, kai da gani ka san faWuwa ta yi, ga tabo a gefen goshinta, kai ba sai an gaya maka iya wannan ya isa ya tabbatar wa mutum da ruma ta azabtu kan ta kuSuta.

Hannunsa biyu ya saka a kan gadon, ya ?urawa yaronsa ido da yake daga lungu, ya tuna irin yadda suka shirya rayuwa da shi da Aisha idan Allah ya sauketa lafiya, da irin budurin da suka shirya yi, da yadda take nanata masa sai dai su bawa mutane mamaki, ba wanda ya san da cikin sai dai su ce wa mutane ga babynsu, yau ga baby amma ita ba ta nan.

"Aisha why, meyasa a karon farko ki ka tsallake umarnina abun da baki taSa yi ba, gashi kin sanya mu a wani hali" ya furta lokacin da hawayensa ya gangaro ya zuba a hannun rumaisa.

Juyi tayi zata gyara kwanciyarta, ya ga tana nema ta danne masa Wa, dan haka cikin azama ya mi?a hannu zai Wauke yaron. Caraf rumaisa ta ri?e hannunsa ta buWe ido ta kalleshi.

"Wayyo Allah zai sace mini Wa, mama kina ina" ta ware murya iya ?arfinta tana ihu.

Ayshercool.

*? 500 ne, via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143*


https://chat.whatsapp.com/G9XU8tDJMjq02zlZMHurZ5
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ?URAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHE?I KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

=?I? *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

Tsayawa yayi cak ya ?ura mata ido, sai yayi mata kwarjini sosai da sosai, hakan ya tilasata yin gum da bakinta tana cigaba da bin sa da kallo.

Hannu ya saka ya Wauko jaririn daga kusa da rumaisa, ai kuwa ta tashi zaune sosai ta tsatstsasreshi da ido, ko ?iftawa ba ta yi, dan kar ya shammaceta ya gudar mata da jariri.

Ya nemi wuri ya zauna, ya Wan tsurawa yaron ido, a hankali ya kai bakinsa kunnen yaron, yayi masa huWuba da Mahmud kamar yadda ammi ta bu?ata, ba kuma dan yayi niyyar sanya sunan ba.

Ya sauke yaron a hankali yana cigaba da kallonsa, ya Waga kai ya kalli rumaisa ya ce "A karo na babu adadi, ina sake tambayarki ina aisha take? Bana son ki kai ni bango, in yi miki abun da ba shikenan ba, ki bani amsar tambayoyin da nayi miki, matata na cikin hatsari dole na san in da take"

Kawar da kanta ta yi gefe, ta ?i kallonsa.

"Am talking to you" yayi maganar cikin tsawa ganin yadda take nema ta mayar da shi mahaukaci.

Sake kawar da kanta gefe ta yi, ta dafe kanta da hannayenta, tana ?un?uni.

"Da ke nake, ki bani amsa" ya sake maganar kamar zai kai mata duka.

"Wai dan Allah me kake so na ce maka, ni na san a in da take? Nima fa saceni a kai, ko garinmu ne da zan san ina ne, ka je da kanka mana ka duba, ni na san sunan wurin ne? Kuma wallahi kar sake yi mini tsawa bana so"

Ya yin?ura zai sake magana mama ta yi sallama. Ya haWiye maganar ya waiwaya ya kalli in da mama take.

Cikin girmamawa suka gaisa,

50 / 61