HURIYYA 1&2 COMPLT BY KHADEEJA CANDY

Author :  KHADEEJA CANDY Category :  Romance

Chapter   83 / 86

246K to 249K   out of 257.5K words



“Haka Jarabawar ta zo mana Yaya? Ni gidan aure babu dadi Hajiya kuma nata auren ya kare, Khairy an fasa yanzu kuma wannan ya biyo baya?”

Yasir ya daka mata tsawa kamar zai daketa.

“Laifi duk na waye ba naku ba? Idan ta kauce ko zata aikata wani abun da ba daidai ba kun fi kowa sani, me yasa ba zaku nuna mata illar hakan ba? Amman ke kuke zugata kuna tayata kishi ku nuna abunda take daidai ne, ke Khairy lokacin da kika aikatawa Hurriya haka bata ma sani ba, saboda zuciyarku babu kyau, ke kuma idan abun kwarai ne gashi yanzu kin yi aure kin girba, kar wanda ya sake saka min baki akan lamarin uwata kar wanda ya sake wata magana ku bar ni na ji da zafi daya”


Ya share hawayensa ya fice daga dakin, ya sauko kasa wayarsa tana ringing da ya duba sai yayi arba da number Appa, and for the first time sai ya ji ba zai iya amsa kiran ba, a yayinda wayar yake rike a hannunsa tana ringing. Ya jingina da kofar falon ya cije bakinsa ya buga ginin ya girgiza kai. A karo na biyu wayarsa ta sake yin ringing ya dago ya duba wayar Appa ya sake kira wannan ya dauka sai dai yana kara wayar a kunnesa sai ya fashewa Appa da kuka kamar mace.

“Subhanallahi... Yasir.. Lafiya kana ina?”

“Ina gida Appa.. Amman ba lafiya, ji nake kamar na bar garin nan kamar na tafi a inda babu kowa na rayu a yau, duk na ji duniya ta isheni”

“Toh gani nan zuwa gidan”

Appa ya sauke wayar yana jin karin wata damuwar, daman ya kira ya fada masa yadda suka yi daman ya kira ne ya fada masa yadda suka yi da Amma da kuma Captain sai dai jin halin da dansa yake cike har yana kuka ya saka shi jin babu dadi domin be san Yasir da bayyana damuwa idan ma akwai.
Yasir ya share hawayensa yana kokarin ganin yayi halin maza wajen hana kansa kuka da jin tsanar duniya da halin da yake ciki, ya nufi bangaren Appa, a Balcony ya zauna kamar dai dazun yana jiran Appa, sai dai Yayyun Hajiya Kaltume da Maama ta kira ta fada musu halin da ake ciki sun riga Appa zuwa, hakan kuma be saka Yasir tashi ya koma bangaren ba, domin baya son ya sake kallon mahaifiyarsa a cikin wannan halin. Direban Appa ya fakawa Yasir ya mike tsaye Appa kuma ya fito mota da sauri yana kallon Yasir.

“Mu shiga ciki”

Yasir ya wuce gaba sannan Appa ya bi bayansa, a babban falonsa suka fara zaunawa Appa ya dubi ďansa cike da damuwarsa ya ce.

“Lafiya Yasir? Me ya faru..?”

Nauyin furucin da kunyar abun da mahaifiyarsa ta aikata sai ya saka shi kasa furta komai a gaban Appa.

“Yasir daga kanka ka kalleni mana fada min damuwarka ni kaina da nake mahaifinki wani abun ai kai nake samu mu tattauna balle kuma kai da kake ďana me yake faruwa?”

“Appa a game da Hamad ne... Dazun ban mun gama magana da kai na shiga cikin gida na fadawa Hajiya abun da ya faru...”

Ya kwashe abun da ya faru ya fadawa Appansa domin be san a inda zai bude damuwarsa bayan nan ba. Appa ya mike tsaye yana ambaton Allah yana jin kamar duniya zata rikito ta fado masa tsabar tsorata da abun da Hajiya Kaltume ta aikata.

“Yanzu da saka hannun Kaltume aka dauke ďana? Da sa hannunta a rabuwata da Iyami? Me na... Me.. Mena rage ta da shi? Akwai ta inda na canja mata ne bayan auren nan? Ba Iyami da yayanta kadai ba har da Sapna? Ita me ta yi mata? Wace irin mata ce Kaltume? Me yake damunta? Innalillahi Wa'inna ilaihirraji'un”

Duk yadda Yasir yake tunanin abun ya gigita shi sai ya tarar ya gigita Appa fiye da shi domin sai da ya tsorata da yadda Appa ya rike kirjinsa ya dafe saitin da zuciyarsa take, tsoron rasa mahaifinsa ya saka shi nadamar sanar masa abun da yake faruwa.

“Appa dan Allah ka zauna”

Yasir ya rika shi ya zauna yana girgiza mai shi ma abun ya daure masa kai, ya san be rage Hajiya Kaltume da komai ba, akan wane dalili zata azantar da kanka ta azabtar da shi kuma ta bi ta yayansa da matarsa? Ta wani bangaren kuma yana ganin laifin ba nata ba ne nashi ne saboda be rike addu'a ba tun farko, kuma be tsaya ya zabo mai addini ba da bata so ta masa wannan aika aikarba a gidansa. Hankalinsa be kara tashi ba sai da ya shiga da kansa ya duba halin da Hajiya Kaltume take ciki, a nan ya tabbatar da abun da dansa ya fada masa yan'uwanta kuma suka bukaci tafiya da ita gida a tare da su, Appa ua daga hannunsa sama yace ba su bukatar umarninsa domin ba aurenta yake a yanzu ba. Momy da Namra sai suka shigo suna kallonta a lokacin da labarin ya isa kunensu, Momy wani sabon tsoron Allah ya kamata daman can ta san Kaltume zata iya aikata fin haka ma, amman ba ta yi zaton da hannunta dumu dumu a satar Hamad ba, a nan ta gane ita kanta Allah ne kadai ya tsare wata kila ita din ma ta an sace mata Namra ko Miwan ko Musib.

Ta bangaren Iyami ma haka ta kasance cikin mamaki ta tashin hankali a lokacin da Appa ya sanar mata halin da Kaltume take ciki, sai ta fashe da kuka tana mamakin tsananin kiyayya da zafin kishi da zai saka mace aikata irin wadannan munanan abubuwan, daman can sun yi tsammanin da hannu a cikin lamarin saboda yadda ta nuna bata damu ba kuma yake nunawa yaran kiyaya ta zahiri. Hakan sai ya kara sanyaya guiwar Amma dake shirye shiryen tarewa a gidan Appa, duk kuwa da ta ji cewar a yanzu Hajiya Kaltume bata cikin hayyacinta, kuma ita ma ta rike addu'a da tsarin jiki ba kamar da can ba, ta wani bangaren Gwaggo da Iyami suna ganin kamar Hajiya Kaltume ta yi haukan karya ne saboda ta san asirinta yana daf da tonuwa. Faruwar hakan ya sakawa Amma yarda cewar yaron da zai baro Ethiopia tare da Hurriya da surukinta da kanwarta lallai danta ne wata kila Allah ya raya shi ne saboda zuwan wannan ranar da asirin Kaltume zai tonu, domin wani abun tun a duniya yake bayyana. Ba sai an je ba, lahira karbar sakamako ne kawai da sanin makoma.



HURRIYA POV.

Cikin tsoro Mama Rukayya take kallon Hamad da ke zaune a masaukinsu, Hurriya na zaune a kusa da shi tana kuka shi kuma yana hawaye.

“Taya wai za ace wanna Hamad ne ni fa ban gane ba..”

“To ke da kika san kan labarin kenan balle ni da ban san komai akai ba”

Cewar Momy Ikilima. Captain ya dan dago ya kallesu kamin ya dauke kai ya cigaba da amsa wayar Appa.

“Hakan nake tunanin zai fi, sai mu dunguma gaba daya mu dawo tare, saboda bana son karatun nasa ya samu matsala ka san su nan sai da doka suke komai ba kamar kasarmu ba”

“Shikenan za'ayi haka, zan kira ka duk yadda ake ciki”

“Na gode Appa...”

Ya sauke wayar ya kalli Hamad.

“Hawayenka su suke saka yar'uwarka kuka kuma kasan yadda idonta yake”

Hamad ya kalleta sai ya mike tsaye da sauri Hurriya ta rike hannunsa ganin take kamar idan ya fita ba zai sake dawowa ba.

“Dan Allah karka tafi..”

“Hurriyana sake ki babu inda zai je tare zamu koma nigeria, na yi magana da Appa zai yi magana da jami'an tsaron can a matsayinsa na Mahaifin Hamad sai su aiko da takarda zuwa ga Ambassador Nigeria da yake nan shi kuma zai yi magana da makaranta su ba mu aron Hamad mu tafi tare da shi a can za a warware komai”

Ta sake shi ba dan ta gamsu zai dawo ba idan ya fita sai dan babu yadda ta iya.

“Bana son ya sake tafiya ya bar ni..”

“As long as you're with me you're not alone, you will never be, babu sauran damuwa Hamad ba zai sake tafiya ba..”

Captain ya fada mata yana kokarin kwantar mata da hankali. Hamad ya share hawayensa ya ce.

“Idan ace Hajiya bata mutu ba, sai na kashe ta da hannuna...”

“Baka bukatar yin haka, jami'an tsaro da kotu zasu yi aikinsu”

Captain ya fada sannan ya karasa ya zauna kusa da matarsa ya kama hannunta ya rike sai ta kwantar da kanta jikinsa.

“Da gaske wai Hamad din ne dai? Innalillahi Wa'inna'ilaihirraji'u, wannan wane irin abu ne? Hamad...”

Mama Rukayya ta fada sannan ta nufe shi ta rumgume tana kuka sosai shi ma kuka yake yana kewar kanwar mahaifiyarshi...

Sai da suka sake yin two days a garin saboda processing din da Appa ya bi na ganin an samu dawowa tare da Hamad ba tare da wata matsala ba, a tsawon kwanan biyun nan kullum Hurriya tana tare da Hamad sai idan ya bar hotel din zuwa school, idan ya dawo Hurriya tana tare da shi tsawon wunin ranar tana labarta masa abubuwa da suka faru bayan baya nan yadda rayuwa ta zame mata a gidan Appa bayan tafiyarsa har zuwa aurenta da sherin da aka yi mata. Duk abun da suke Captain sai da yayi ta kallonsu gwanin sha'awa domin shi dai be san dadin dan'uwa ba.

“Na yi kewarki sosai Hurriya na fi jin kewarki fiye da kowa, saboda ina yawan dukanki ina zalintarki, da Captain ya fada min cewar bani da kowa a yanzu, sai na tuna abubuwa da nake miki na ji kamar na akashe kaina abun yana ta damuna...”

Hurriya tana hawaye ta ce.

“Yanzu duk mun girma Hamad, daman can kurciya ce, kana da zafin zuciya ni kuma bana iya raba kaina da kai, shiyasa har Amma ta yi maka takwara ban yarda ka mutu ba..”

Captain ya mika mata waya.

“Cry Cry Baby Ammy zata yi magana dake”

Ta karbi wayar ta kara a kunne.

“Hello Ammy ina wuni..?”

“Lafiya kalau, ya idon naki?”

“Alhamdulillahi ina ta samun sauki”

“Ya na ji muryarki wani iri? Ko Captain din ne yayi miki wani abun?”

“Aa ba shi ba ne”

“Ba shi wayar”

Hurriya ta mika masa wayar sai ya zauna kusa da ita ya kara wayar a kunne.

“Ammy”

“Wani abun ka yi mata ne? Na ji kamar tana kuka?”

“Ban mata komai ba, ya za'ayi na mata wani abu Ammy yaushe muka yi auren ma da za'ace har mun fara samun tsabani?”

“To waye be san halin maza ba? me take yi ma kuka?”

“Tana tare da dan'uwanta ai na fada miki abun da ya faru, kuma idan suna tattauna labarin baya tana yawan kuka shi ne kawai”

“Ayyah ba ka ce gobe za su dawo ba?”

“Eh in Sha Allah daman amincewar makaranta Muke jira kuma sun ba mu takardar a rubuce za mu taso gobe da safe da yardar Allah”

“Allah kawo ku lafiya, ku kula da kanku”

“I will i love you Ammy”

Ta gwatsale shi.

“Dan Allah can ko kunya baka ji a gaban matarka da kanenta sai ka ce wani yaro”

Yayi dariya ya sauke wayar. Hamad ya kalleshi.

“Kai mutumen kirki ne Captain ka kula da ni yadda ya kamata, Hurriya ta ba ni labarin yadda ka yi mata yaki, amman me yasa ka ce min kowa ya mutu?”

“Idan mun je zaka ji”

Captain ya juyo da fuskar Hurriya

“Mai tsada me za miki order?”

Ta juya ta kalli Hamad.

“Hamad me zaka ci?”

“Haba Baby ina lallabaki ki ci abinci ke kuma da wannan gwaskan kike? Babu inda be sani ba a garin Addis Ababa ki daina damun kanki da cinsa”

“Ko a gida haka muke, inda har zan ci abinci to zan zuba masa ne ya ci, ka yi hakuri

Yaja hancinta yana murmushi.

“Tsokanarki nake, tambaye me yake so sai na siyo muku”

Hamad yayi murmushi yana ganin kamar mafarki ne, wai yayarce da mijinta zaune tare da shi a yau.

“Yayata mai kaunata yar'uwata abar alfaharina”

“Ba ka ce ni ba yayarka ba ce?”

Ta tambaya tana hawaye shi ma hawayen yake yana murmushi.

“Ada kenan yanzu na bar miki girman”

Ta yi murmushi cikin hawaye, Captain ma Murmushi yayi ya tashi ya fita.

Ya sake daukarsu awa biyar da mintuna kamin su iso Nigeria daga babban birnin Ethiopia. A Abuja suka sauka, ba su tsaya komai ba suka sake booking flight from Abuja to Kaduna, Ammy ta yi musu tarba ta musamman tana ta na'am na'am da matar danta kamar daman can babu wani abun da ya taba shiga tsakaninsu. Sai da suka yi wanka suka huta sannan suka hadu a teburin cin abinci da yake gidan. A nan Hurriya ta gane ubanta Alhaji Haruna Mai Yadi karyar arziki yake domin falon Ammy ma ba tile ba ne wani abun ne aka shimfida mai kamar ruwa, ga manyan kujerun da bata taba ganin kalarsu ba a rayuwarta, dinning din ma wani abun kallo ne a gurinta balle kuma dakin da suka sauka. Ko'ina na gidan kyalkyale ni kamar an watsa zinari. Bakauya ta zama a gidan komai ta gani sabo yake zama mata, a nan ta yarda da Momy take ganin kamar bata dace da auren Captain ta bangaren arziki. Masu aikin gidan ma kansu abun kallo ne basa barin komai ya zuba a kasa da zarar an aje abu za su zo da gudu su dauke.

Captain da kansa yaja mata kujera ta zauna, sannan ya zauna yana magana da mahaifiyarsa da ta zabi serving din matarsa da kanta ba kamar Momy Ikilima da Mama Rukayya da masu aiki suke zuba musu abinci ba, sai da ta fara ajewa Hurriya plate din abinci sannan ta zubawa Captain ta aje masa warin kwai dake kan salad ya saka shi jin tashi zuciya da sauri ya kawar da fuska yana yunkurin amai.

“Me ya faru wani abu ka gani a abinci?”

“No kwan ne na ji shi wani iri, bana son warinsa”

Ammy ta dauke plate din ta zuba masa wani abinci babu kwai har ya fara ci sai kuma ya ji baya son abinci kawai wani abun kwadayi yake so.

“To ko dan kun yi tafiya a jirgi ne?”

“Ammy karki sa na ji kunya mana, yau na saba hawan jirgi?”

Hamad ya kalleshi.

“Ko dai baka da lafiya ne?”

“I think so, jikina ma yayi zafi, tun da muka je ba wani lafiya nake ji ba, kawai dai ina daurewa ne saboda akwai abubuwa da yawa a gabana”

Ammy ta kalli Hamad.

“Wannan ne yaron? Shi da wanda kake yawan zuwa Ethiopia gurinsa daman? Da zarar ka samu sarari sai ka tsallake ka tafi Ethiopia ashe duk saboda shi ne?”

“Wallahi kuwa Ammy”

“Bari na kira Family Doctor ya dubaka kamin ku tafi”

“Okay”

Ammy ta tashi ta bar dinning din, Captain ya kalli daya daga cikin masu aikin gidan ya ce.

“Samo min wani abu mai ruwa ruwa na sha”

“To ranka ya dade”

Sai da Ammy ta kira likitansu na gida ya zo ya auna Captain ya duba shi ya fada musu fever ne kawai yayi masa allura ya kuma dorashi akan magunguna sannan suka bar garin Kaduna a business flight din Daddy da baya kasar domin ta waya ya gaisa da Hurriya yayi mata maraba da zuwa gidansa kuma ya saka Ammy ta hada mata goma ta arziki a madadinsa.
*A duk lokacin da nake littafi sai an tambaye ni minene POV saboda ina saka shi a duka books dina, POV yana nufin POINT OF VIEW. idan wata ta sake tambayata sai na cire mata hakorin gaba 🥴*

HAJIYA FATEE POV

“Hajiya jikin ne dai?”

Fadeel ya tambaya yana taba jikinta cike da damuwa Hajiya Fatee ya dago ta dubi danta, cikin bakinciki da nadama ta ce.

“Ko da jikinki bana bukatar tafiya asibiti yanzu Fadeel, ku bar ni na yi abun kunyana a nan idan ma kasheshi saku yi ku kashe, bayan na tafi”

Afrah ta girgiza kai.

“Haba Hajiya ki daina fadar hakan, abun da ya same ki kaddara ce daga Allah, kowa da yadda Allah ya rubuta masa kaddararsa, zai iya samun kowa, Allah ya tsare mu da kashe abun da kika haifa, ko me kika aikata muna son rayuwarki kuma ina sonki a haka saboda kw mahaifiyar Fadeel ce ina son miJina ba zan taba tsanar mahaifiyarsa ba”

“Na yi abun kunya, sanar matar ďana ina ta ganin kamar kin tare shi daga gareni ashe sheidan ne yake ta min gizo da sake sake, dubi yadda na zama na janyo muku abun kunya”

Fadeel ya sauke ajiyar zuciya, tabbas idan har duniya ta san halin da mahaifiyarsa take ciki zai ji kunya ba karami ba, daga lokacin da na gane gaskiyar abun da take boye masa har zuwa lokacin da ta bayyana masa gaskiyar komai da komai be sake walwala ba, ba sake kwantawa bachi ya dauke shi ba, be sake kallon wani abu yayi dariya ba gaba daya farinciki ya kaurace masa.

“Zan tafi na bar muku abun kunya Fadeel, dan Allah ka yafe min kuma ka kula da yar'uwarta, ka fahimtar da ita ban kai aikata aka min cikin nan ba sai dan kaddara ta biyo ta nan”

“Karki damu Hajiya, Zainab zata dauko kuma zaki samu sauki ki tashi da yardar Allah, ko ma miya faru mu dai muna son rayuwarki”

“Mutuwata tafi rayuwata Fadeel bana fatan rayuwa idan ma na haihu lafiya, idan kuma ban haihu ba, kun huta karku fadawa kowa abun da uwarku ta yi, Afrah ki yafe min dan Alla..”

“Na yafe miki Hajiya Wallahi ni ban rike da komai ba”

“Allah ya muku albarka... Tashi ka tafi gurin aikinka, ga matarka nan ai ta isa tana kula da ni”

“Toh Hajiya”

Ya mike tsaye ya fice daga dakin. Kusan tun da gaskiyar cikin ta bayyana shi da yar'uwarsa suka ji cewar ba kari ba ne, cikin shege ne Hajiya Fatee ta yi Zainab ta bar gidan ta koma gidan kanen mahaifinsu kuma ta kasa komawa gidan mijinta saboda uwarta ta yi abun kunya, sai kulawar Hajiya Fatee ta dawo karkashin Matar Fadeel wato Afrah wanda ya maida ita gidansa bayan fasa auren Khairy da yayi daman ba shi da burin auren kawai yana biyayya ga cilastawar mahaifiyarsa ne. Matar da take zagi take cewa ta mallake mata ďa matar da saboda ita wannan mummunan kaddara ta same ta yau ita ce take

83 / 86