HURIYYA 1&2 COMPLT BY KHADEEJA CANDY

Author :  KHADEEJA CANDY Category :  Romance

Chapter   32 / 86

93K to 96K   out of 257.5K words

Kaltume da take jin idan har Khairi ta auri Fadeel ta yi sa'a domin namiji ne mai kyau ga hankali ga kudi ga iya kula da gidansa, musamman ma idan aka kure matarsa yaransa kuma a maida su hannun uwarsu ko Hajiya Fatee gida ya zama na yarta ita kadai.

“Matukar kika auri Fadeel Khairi kin yi dace, amman na lura ke ma kamar kina son raba min hankali biyu toh ba zan dauka ba”

Magana take da kanta, ta sake daukar wayarta ta kira Malaminta ta fada masa abun da ya faru har tana zargin ko aikinsu ya fara karyewa ne, sai ya bukaci ta bashi minti goma zai sake kiranta, after ten minutes ya kira yana fada mata abun da ya faru.

“Daman na san ba zai karye ba, ai ba karamin aiki na yi ba, haba Hajiya duk bayan sakamakon da kika min ga kudi ga Makka da kika kai ni, sai kuma na bari ki ji kunya? Sam ai ba zan yarda ba, kawai dai abun yana dan fisgo masa ne, kin san fa ya fi son yarinyar nan fiye da sauran yayansa domin na duba na ga haka a zuciyarsa musamnan ma yanzu da abubuwan nan suke faruwa, kawai dai mun danne son ne a zuciyarsa ba zai iya nunawa, kuma muka kawo tsana muka saka a tsakaninsu”

Hajiya Kaltume ta ji dadi sosai.

“Haka nake son ji, amman Malam ta bangaren Nafisa fa Malam, matar nan ta zame min karfen kafa, na rasa ya zan yi da ita, amman maganar gaskiya tana jefani a damuwa sosai, ka duba ka gani kirikiri an mata sata amman sai ni ta dorawa, kai ba dan gidan nan ba ne ai sai na yi kararta”

“Karki damu, ita ma zamu maida hankali a gurinta, kuma zamu zafafa na Alhaji ta yadda ba zai iya yanke shawarar komai ba, sai dake, kuma zan saka masa tsananin tsoronki sannan mu cire Nafisar a zuciyarsa kamar yadda muka cire iyami”

“Haka nake so Malam, anjima kadan zaka ji sako mai nauyi”

Ya amsa da dariya.

“To Maa Shaa Allahu, sai dai kuma ina son na fada miki ki maida hankali gurin Hurriya, domin yanzu haka da na duba matsalalolin gidan na duba na duba na kasa ganin komai ta bangarenta”

“Kamar ya Malam?”

“Idan na je gurin bincikenta sai wani haske ya zo ya tare yadda ba zan iya ganin komai ba sai ma na yi saurin kawar da ido saboda kar ya illata ni, kuma na duba na ga ko ta can bangaren mahaifiyarta ake mata wani abu ban ga sun mata komai ba, wata kila wannan haske ne ma ya hana Mijinki hukunta ta, na rasa gane ko minene Wallahi”

“Toh Malam ko wani lakani ta samu kuma? Shiyasa ta fara sata? Zan saka a bincike min dakinta tsab a duba ko'ina idan ma wani abun ne ta yi a dauke shi”

“Ba ita ta yi sata ba, a cikin masu aikinta ne wata ta dauka, wata yar guntuwa baka mai jiki ita ta sata, kudin da sarkar suna nan bayan dakunansu ta boye a cikin itacen fulawa”

Hajiya Kaltume ta rike baki.

“Lallai Malam ka kai Malam wannan da kudi na ne sai kawai na je na dauko kuma na kori mai aiki, amman ina.... Sai dai ma na yi addu'ar Allah ya kara bata sa'ar daukar wasu”

Malam yayi dariya yana jinjina muguntar Kaltume.

“Hajiya na lura ke ma ba ƙyale ba ce”

“Malam mutane ai sai da haka, na gode sosai sai ka ga sakona”

“Toh shikenan Hajiya sai na jiki”

Ta sauke wayar da mamaki a ranta, me Hurriya ta yi? Gashi yarinya ce balle tace ta fara shige shige kuma gashi Malam yace ba Iyami ce ta bata komai ba.

“Toh minene? Bari Khairy ta zo zan saka bincika min yarinyar nan, ni kam na san ba a banza ba Alhaji ya wanke ta a gaban mutane”

Ya cije baki ta kashe ido tana motsa kafa.



HURRIYA POV.

Tana shiga dakinta ta kalli gabas ta fadi ta yi sujadar godiya ga Allah na abun da Appa yayi mata a yau, domin ta gama katsewa ta dauka zai yarda ta aikata ne har ma yayi mata hukunci, amman sai gashi yayi abun da ba ta zata ba a yanzu. Rumgume hannayenta ta yi tana jin kamar ace Amma ko Appan Hamad suna kusa ya rumgume wani saboda jindadi. Cikin kuzari ta tashi ta fara gyara dakinta da aka yamutsa tana maida komai a yadda yake. Har ta zo kan box din da aka hargitsa da Adam ya kawo mata, takardar ciki ta fara dauka ta warware tana dubawa.

_Hey Beautiful... How are you? You're doing good i guess. Na aiko miki da wannan sakon ne just to say sorry for what happen at Mall na lura kamar baki ji dadin haka ba, i promise you ba zai sake faruwa ba matukar baki so. And duk lokacin da zaki gama karanta sakon nan ina nan waje harabar gidanku a cikin mota ba zan tafi ba ko da kuwa ko wa zai zo ya ganni_

Ta yi saurin daga kai a lokacin da ta kai gabar da yake fadar haka, sai ta nufi windows dinta gabanta na faduwa da sauri ta daga curtains din tana rike da takardar ta bude window tana kallon Motocin Momy dake gurin bata ga wata bakuwar mota ba. Ta sake maida idonta gurin takardar

_Oops... Sorry wasa nake miki na san yanzu gabanki yana nan yana faduwa, relax take a deep breath_

Ta yi taking deep breaths din kamar yadda ya bukata tana daga kanta sama ta sauke. Sannan ta sake maida idonta gurin takarsar mai kyalli da zanen heart.

_Na san kin je kin duba ko zaki ganki i fooling you_

Ta yi murmushi kadan..

_You're Smile_

Sai ta saka dariya mai sauti mai dadi.

_And you're laughing_

Ta daga kanta sama gaba daya tana dariya tare da mamakin yadda aka yi ya sani.

“Oh my God, ya aka yi ya sani?”

Ta duba karshen sakon.

_Daman muradina kenan ki yi murmushi, i just want you to be happy and healthy... Have a nice Day, ki boye teddy nan da kyau and spray that perfume, till the bottle cried out for help, and also the chocolate can't wait to be on your soft mouth_

_Adam_


“Adam”

Ta maimaita sunan kamar yadda ya ke rubuce a jikin kakardar sannan ta kalli white teddy din dake kasa, ta kalli kwalin turare da chocolate dake kasa at the same time. Gurin ta nufa ta zauna ta dauki chocolate din ta fara ci, sai gata tana lumashe ido saboda dadinsa. Ta dauki turaren ta bude ta fesa kadan tana jin kamshinsa. And his words keep rolling in her head wani be taba mata haka ba, ita da bata ma taba tsayawa da wani da sunan hira ba. Kamar an jefo mata tsawa haka gargadin Appa da yayanta ya dawo mata a rai da kuma maganar da aka fada akansa cewar ba yaron kirki ba ne. Cikin sauri ta maida komai cikin box din ta rufe ta saka shi karkashin gado.
*I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba, na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba tare da biya ba na barku da Allah...!*

Bayan Sallah Isha'i tana kwamce dakinta, Namra ta turo kofar dakin ta shigo, Hurriya ta tashi zaune da sauri tana jiran jin abun da zata karanta mata.

“Hurriya yau ba zaki ci abinci dare ba hala?”

Ta yi shiru ta sauke kanta kasa.

“Baki jin yunwa ne?”

“Ina ji i thought kun tsane ni ne”

Ta fada shagwabe, Namra ta yi murmushi ta karasa kusa da ita ta zauna.

“Why zamu tsane ki, ko da gaske ce kina sata Hurriya ke fa jinina ce dole haka zan so ki, balle ma ba halinki ba ne daman ni ban yarda kin aikata ba, baki jidadin da naji ba a lokacin da Appa ya wanke ki, ni nafi kyautata zaton masu aikin Momy ne suka dauka ko kuma wasu daga cikin gidan nan, amman ke da ake fadar kin fi mu kyau hali a gidan nan ai ba zan yarda kin aikata ba, besides Momy tace ba zata bari ga Allah ba kin ga ko waye zai bayyana kansa, ki daina damuwa tashi muje mu ci abincin dare”

Hurriya ta sauko ganin Namra ta mike tsaye suka fita tare, suka sauka kasa a plate daya Namra ta saka musu tuwon semu da miyar yauki ta saka manshanu sosai, ta dauko ruwa ta zauna a kasa.

“Sauko mu ci”

Hurriya ta tashi ta shiga Kitchen ta wanke hannunta ta fito ta zauna kusa da Namra, a madadin ta ci abincin kai tsaye sai ta kwantar da kanta jikin Namra.

“Yaya Namra na gode, ke da Yayana kawai kuke so na a gidan nan”

Namra ta yi murmushi.

“Ba komai yar kanwata, ni wannan abun da ake cewa yan ubanci bana miki kallon haka, ina kallonki ne kamar uwa daya uba daya muke, tashi ki ci abinci”

Ta tashi ta gyara zamanta sai dai kamin ta kai hannunta cikin abinci Khairy ta shigo sanye da karamin mayafinta wayarta a hannunta, is like kamar an mata dole haka ta tsaya bakin kofar falon babu ko sallama.

“Hurriya taso muje”

Hurriya ta kalleta.

“Ina?”

“Ki taso idan zaki taso Malama”

Namra ta daga kai ta kalli Khairy da duba na wulakancin.

“Ba zata tashi ba abinci zata ci”

“Okay sannu uwarta, bari naje na fadawa Yaya uwarta ta hanata zuwa, ita ma kuma ta ce ba zata je ba”

Hurriya na jin kiran na Yayanta ta tashi tsaye da sauri zata nufi kofar.

“Dauko mayafinki Hajiya”

Ta juya ta dauko mayafin kamar yadda Khairy ta bukata, sannan ta bi bayanta suka fice, at first ta yi zaton bangaren Hajiya Kaltume za su nufa sai kuma ta ga ta nufi gate.

“Ba yaya kika ce yana kirana ba?”

“Yana waje”

Huriyya ta bi bayanta suka fita gate, close to gate din wata mota ce fake da ba ta gidan ba. Gurin motar suka nufa ta bude ma Hurriya baya.

“Shiga”

“Amman wannan ba motar Yayana ba ce... ”

“Zaki shiga ko sai ya fito ya mareki? Ba shi ya ce mu jira shi a mota ba”

Hurriya ta shiga da sauri, Khairy ta rufe bayan sannan ta bude front seat ta shiga ta zauna tana taba wayarta. After like five minutes aka bude motar ta Driver seat aka shigo, tana leken fuskarsa yana juyo ya kalleta wa zata gani ba Adam ba.

“Thank you Khary”

“This should be the last time sa zaka cilasta min fitowa da yarinyar nan”

Ta fada a kufule. Hurriya ta kalleta fuska kamar zata fashe da kuka, murya kamar a shagwabe ta ce.

“Amman yaya Khairy kin san me Appa yace ko kuma kin san Yayana zai yi fada idan ya sani”

Adam yayi saurin tarar numfashinta.

“Ba dadewa zamu yi ba Hurriya, kawai ina son na ganki ne kuma na baki hakuri abun da ya faru, and na aiko da box an baki?”

Khairy ta watsa masa wani kallo.

“Okay ni zan hana mata box din kenan?”

“Waya sani, tun da har kika iya bata ni a gurinta ai zaki iya hana ta ganin box din”

“Ni ban bata ka ba”

“And why take min kallon mutumen banza? Ni ba iskanci ne ya kawo ni gurinta ba, ki daina fada mata bad things about me, na ga ai natsantsiya ce not like you that's why i like her”

With shock Khairy take kallonsa.

“Adam what's the meaning of all this?”

“Sonta nake yi, and I'm ready to prove it, i want to talk to her parents da duk wani mai son hana alakata da ita tafiya I'm serious”

Khairy ta tsaya kallonsa for some seconds kamin ta dauke kai ta bude motar, Hurriya ma ta bude motar zata fita.

“Fita zata yi idan kika fita, ki zauna sai na gama magana da ita”

Ya fada da kamar fada yana kallon Khairy da bata fita motar ba, jin haka ya saka ta fasa fitar ta rufe motar, Hurriya kam bata tsaya ba ta fice ta tana ganin Adam ya bude motar ta ranta a na kare ta shige gida da sauri, a fusace ya dawo motar ya rufe Khairy da fada

“Kin ga abun da kike ja ko? Kin dauki tsanata kin sakawa yarinyar har guduna take”

“Toh wai kai Adam duk yan matan duniya ka rasa wa zaka so sai Hurriya? Yarinyar da ko jami'a bata fara ba”

“Ba ruwanki”

Ya bude gurin da yake ajiyar kudi ya dauko rafar dubu daya ya mika mata

“Je ki gyara abun da kika bata ina son yarinyar nan ta so ni”

Khairy ta kalli kudin ta kalleshi, kamar ta yi magana sai kuma ta saka hannu ta karba ta bude motar ta fita.

“Why Adam why...”

Ta fada cikin yanayin damuwa da gajiyawa tana tafiya ba tare da ta juyo ba. _____________________

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘


Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲


𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣6⃣

Sai da Hurriya ta shigo gidan sannan ta daina gudu, sai dai hango Hajiya Kaltume tsaye a karamin gate din part dinta ya kara daga mata hankali sosai domin irin tsayin da Hajiya ta yi ya nuna kamar ita take jira. Rage tafiyar da take ta yi gabanta na faduwa tana ta sake sake domin ta san halin Hajiya Kaltume da ma Khairy din za su iya wanke kansu ita su jefata a ruwa. Tana daf da shigewa bangaren Momy Hajiya Kaltume ta yi kiranta da hannu, a lokacin ne tsoro ya kara cika zuciyar Hurriya, haka dai ta daure ta karasa gurin da take tsaye.

“Hajiya gani”

“Ina kika fito?”

“Yaya Khairy na raka waje gurin Saurayinta”

Hajiya Kaltume ta yi fuskar mamaki.

“Saurayinta kuma? Waye?”

“Ban san shi ba ni ma”

“Okay. Je ki BQ din Nafisa ki kira min Kulu, kuma ban ce ki fadawa Nafisa ba, sannan ki fada mata ta same ni bangarena magana ce mai muhimmanci ki kirata dabam ki fada mata ba a cikin mutane ba”

“To Hajiya”

Ta mike tsaye tana jin sanyi a ranta, na rashin zafafa bincike ko binta da zagi da Hajiya Kaltume bata yi a yau. Tana shiga gate din da nufi BQ din Momy har karamar kofar bangaren masu aikin ta fara budewa ta shiga ciki, dukansu suna waje suna hira har da dare dare.

“Mama Kulu ina wuninku”

Ta gaishesu, duk suka amsa mata har Kulu, sannan Hurriya ta ce.

“Mama Kulu wai ki zo”

“Ni”

Ta nuna kanta.

“Eh”

“In ji wa?”

Dayar dake zaune kusa da ita ta saka dariya.

“Ke ma dai da neman tsawaita zance kike, waye zai kiraki duk gidan nan ban da Momy? Kuma tun da kika ga Hurriya a kin san ita take nemanki”

Hurriya dai bata ce komai ba ta juyo ta fara tafiya, a bakin kofar ta tsaya har sai da Kulu ta fito sannan ta tare tace.

“Ba Momy ke nemanki ba, Hajiya”

“Hajiya kuma?”

She asked with shock.

“Eh nima na dawo daga waje na ganta tsaye tace na kiraki kuma kar na bari kowa ya ji, ta ce ki same ta bangarenta magana ce mai muhimmanci”

“Toh... Allah yasa dai lafiya”

Hurriya dai ban da kallonta babu abun da ta yi, domin ita ma bata san dalilin kiran ba balle ta fada mata ita kuma bata daina faduwar gaba ba har ta isa bangaren na Hajiya Kaltume. Daman Hurriya tana isar mata da sako ta shiga bangaren Momy ta bar a guri..

Cikin tsoro ta shiga falon da Momy tana sallama. Ruma ce kadai zaune a falon tana cin abinci, hannu ta sauke ta aje plate a kasa bayan ta amsa sallamar Kulu, ita kanta mamakin ganinta a bangaren take.

“Hajiya na ciki ta ce tana son ganin”

“Eh tana ciki bari na kirata”

Ta mike tsaye tana tsude hannu ta nufi stairs, slowly ta tura kofar dakin Hajiya ta lake.

“Hajiya ga Kulu mai aikin Momy a kasa tana nemanki”

“Je ki ce mata ta shigo”

“Nan eh?”

“Eh”

Ta juya ta koma, tun kamin ta karasa saukowa ta fadawa Kulu sakon Hajiya Kaltume.

“Ta ce ki shigo”

“Na shigo kuma?”

Ruma ta daga mata kai, Kulu ta daga kai ta kalli stairs din da bata taba hawa ba, tun zuwanta gidan, shigarta bangaren Hajiya Kaltume ma za a iya kidayashi domin bata zuwa sai idan Momy ta aikota, kuma ba kasafai Momy take haka ba. Da tsoro Kulu ta taka ta hau stairs sai ta rasa wane daki zata shiga domin duka dakunan a rufe suke kuma bata taba kaiwa gun ba balle ta gane wanene dakin Hajiya Kaltume. Kwatantawa

32 / 86