HURIYYA 1&2 COMPLT BY KHADEEJA CANDY

Author :  KHADEEJA CANDY Category :  Romance

Chapter   35 / 86

102K to 105K   out of 257.5K words

ta samu kanta tsaye tana fuskantar madubin dake gabanta, wata macen mai kama da ita take gani, mai tsananin rauni da damuwa, cikin zuciyarta take hangowa mai cike da kunci da bakinciki. Takawa ta yi kamar mai koyon tatata ta isa gaban madubin dake dakin tana kallon Innocent face dinta.

“Rarrashi nake so, babu mai yi min, gata nake nema na rasa shi ta ko'ina, rayuwa a gidan da babu uwa akwai wahala ko da tana raye, farinciki neman gagarata yake yi, me na tare musu ne? Wane laifi na aikata wa kowa yake ta tsanata? Dan wannan abun har ya kai Appa ya koreni? Kuma babu wanda zai bashi hakuri?”

Magana take da kanta tana kallon kyakkyawar fuskarta dake zube a jikin madubin.

‘Ba komai yake bukatar kuka ba Hurriya, wani abun jajircewa yake bukata, ki karfafawa kanki guiwa, ki goyi bayan kanki, sannan kuma ki saurari zuciyarki, idan babu mai kaunarki ki kaunaci kanki, nuna musu zaki iya karki yi kasa a guiwa, wata rana ke uwa ce, irin wannan matsalolin ke zaki magancewa yayanki...’

Wani ne ya kamata ace ya tsaya a gafenta ya fada mata wannan, akasin haka zuciyarta ce ke karanta mata karantun da a yanzu ta shirya daukarsa, domin a yanzu ne idonta ya bude zuciyarta kuma take kokarin waraka da rauni. Hannu ta saka ta share hawayenta na dama zuwa hagu, sannan ta yi murmushi ta juya cikin kuzari ta fara hada kayanta. Abubuwan da ta san zata fi bukata ta hada a luggage ta ta dauki Qur'anenta ta fito daga dakin, ta fara saukowa a hankali sai da ta sauko falo sannan ta kalli Momy ta ce.

“Momy zan tafi?”

“Ina?”

Momy ta duba ta da mamaki.

“Ina?”

“Appa ya ce na bar masa gidansa”

“Saboda wannan abun?”

Hurriya ta yi shiru bata ce komai ba. Momy ta tashi tsaye.

“Ina zuwa, ki bar gidan ki tafi ina?”

Ta nufi hanyar da zata sadata da bangaren Appa, kamin ta karasa Hurriya ta ce.

“Momy ko kin tafi ba zai hakura ba, ransa ya bace sosai”

Momy ta juyo.

“Daman na san za a rina, yadda Kaltume ta kori uwarki wata rana sai ta koreki a gidan nan, ke ma kuma baki jin magana tun da kin san halin mahaifinki a yanzu ai ya kamata ki kiyaye, miye na zuwa ki yi tseguminsa da kawarki har magana ta dawo kunnensa”

Hurriya ta sauke kanta kasa, ita kanta bata san yadda zata warware wannan abun ba, balle kuma su da suke kallonta a munafuka. Namra ta sauko rike da leda ta mikawa Hurriya dake tsaye.

“Gashi Ethiopian ya ce a baki”

Hurriya ta kalleta, tana tsammanin zata taya ta jimamin korar da Appa yayi mata ko ta tausayawa mata amman bata ga alamar ko daya a fuskarta ba.

“Ki rike na bar miki”

Ta juya ta ja Luggage dinta ta cigaba da tafiyarta, sai da ta fice daga bangaren na Momy sannan ta ci hawaye ya cika idonta duk yadda ta so ta hana su zubowa abun sai ya gagareta, domin bata iko da hawayenta a yanzu hasalima su suke da iko da ita. Har ta isa gate masu gadin suka bude mata suna tambayarta lafiya, bata hararo babban dalilin Appa na korarta a gidan ba. Idan ma mahaifin Husna ya same shi da zancen, be kamata ya koreta saboda wannan ba. Tana tafiya tana karfafawa kanta guiwa hawaye na zubo mata, har ta isa babban titin dake sokoto gusau road, a gurin ta tari napep ta hau zuciyarta bata raya mata zuwa ko'ina ba sai gidan kakarta mai kaunarta Hajiya Binta.



Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar  MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne  cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai  shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻

𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘


Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲


𝐏𝐚𝐠𝐞 1️⃣8⃣



Hajiya Binta dake aikin dama shuwaka ta dago ya kalli Hurriya wanda shigowarta kenan da kaya niki niki.

“Subhanallahi Hurriya lafiya”

“Appa ya koreni Hajiya”

“Kora? Kora fa kika ce Hurriya”

Ta daga kai idonta na zubar da hawayen da bata son zubarsu, sai dai kuma bata isa ta hana su zuba ba.

“Me kika masa?”

“Kawata ce ta yi”

“Kuma a gidan aka rasa wanda zai yi wani abu har kika fito?”

“Hajiya Mai Napep yana waje yana jira”

Hajiya ta sauke ajiyar zuciya.

“Shiga dakins ki dauko kudi a jaka ki ba shi”

Hurriya ta nufi dakin, bata dade ba ta fito rike da one thousand ta fice ta sallami mai Napep din sannan ta dawo ta zauna kusa da Hajiya Binta.

“Hajiya yanzu kowa baya so na gidan nan, ban san me na yi ba, kowa ya tsane ni”

Hajiya Binta ta bude robar gishi ta diba kadan ta zuba a cikin shuwakar data dama ta dauka ta sha sannan ta kalli Hurriya ta ce.

“Nasara ce take tare da ke jikata, duk gurin da kika ga tsanani yayi yawa, to wani alherin ne babba zai taho, wata kila nan gaba sai kin zama wata abar kwatance a cikin familynku, duk sai kin fi su daukaka da nasarar rayuwa Hurriya karki ji komai a ranki, kar wannan abun ya dame ki”

A lokacin ne wani kukan shagwaba ya rufe Hurriya ta tabe baki tana kallon kakarta abar kaunarta.

“Hajiya ai yace ba zan yi karatu ba, wai ba da yawun bakinsa ba”

“Idan yana takamar haihuwarki yayi shi ma ai haihuwarsa aka yi! Kuma wanda ya haife shi yana raye, kina can ma nake miki yaki balle kin dawo gurina? Ba dan yana gidan mahaifinki ba ai da sai na ce haka ya fi, daman na yi nayi ya bar min ku na rike ke da Hamad ya ki, yanzu kuma kin ga ya koreki da kansa”

Hurriya ta kwanta jikin Hajiya tana zuba shagwaba kamar ba ita ba.

“Cewa yayi wai na tafi gidansu baban kawata na zauna saboda ...”

Hajiya Binta ta girgiza kai cike da takaicin bayan ta gama sauraren dalilin korar da aka yi ma Hurriya.

“Kin yi tunani da baki tafi gidan Iyami a wannan yanayin ba, sai abun ya kara mata yawa a zuciya, idan ma zaki fada mata sai ki ce mata ni na dawo da ke nan gurina”

“Shiyasa na taho nan ai”

“Kim kyauta daman ina neman abokiyar zama, shi kuma Allah ya warware masa duk wani abu da yake cikin kansa, gaba daya an juye masa hankali ya canja kamar ba shi ba, gidan nan ma sai ya dauki wata uku biyu be zo ba, kiran waya kuma sai idan na kira shi, babu ruwansa da kowa sai Kaltume, gaba daya ta dauke masa hankali sai abun da tace yake yi”

“Kuma ni ban ce Babanta yayi masa magana ba fa Hajiya, ni ban yadda aka yi ma Babanta ya ji ba”

“Wata kila tana tausaya miki ne, sai ta aika hakan da kyakkyawar niya, shi kuma ya kasa fahimtar abun, daman kowaye zai ji haushi amman be kamata idonsa ya rufe har haka ba, maraicinki ya kamata ya duba, yanzu da baki da ni ko baki da uwa a raye sai dai ki koma wani gurin rabe gurin yan'uwa ko kuma wadanda baki hada komai da su ba?”

Ta kara gyara kwanciyarta jikin Hajiya.

“Allah ma yasa ina da ke”

Hajiya Binta ta yi murmushin dake kara bayyana tsufanta, ta shafa kan Hurriya.

“Kar Allah ya raba mu har sai na damkaki ga miji mai amana Hurriya”

“Ameen”

Ta amsa tare da rufe idonta tana dariya.

“Ja'irar yarinya wato har da cewa Amin ko?”

Ta saka dariya sosai sannan ta tashi ta dauke kayan ta shiga da su dakin Hajiya.

“Aa daki dabam zamu yi, wake zama da kishiya daki daya”

“Dole ne ki yi hakuri da ni Hajiya daki daya zamu zauna”

“Toh aje kayan ki fito ki ci abinci, na san cikin nan naki yana nan dauke da yunwa”

Kusa da gadon Hajiya Binta Hurriya ta aje luggage dinta sannan ta cire hijab dinta ta jefa saman gado ta juyo ta fito.

“Hajiya me aka dafa miki?”

“Zai wuce tuwo ne Hurriya kin san abincin tsufi ai ba kamar ku ba, idan ma baki son tuwon ki shiga Kitchen ki dafa indomie”

“Toh”

Ta amsa sannan ta nufi hanyar Kitchen din, tun da ta shiga bata fito ba har sai da Indomie dinta ta dahu ta zuba a plate ta dauko ta fito. Aje plate dinta yayi daidai da shigowar Yasir falon hankalinsa a tashe yana ganinta ya dafa zuciyarsa ya nemi guri ya zauna.

“Kin daga mana hankali, na je gidan Amma baki can, na dawo gidansu Husna aka ce baki zo ba, na dauka wani gurin kika tafi”

“Allah yasa dai baka dagawa Iyami hankali ba, domin ba su san abun da ya faru ba”

“No naje gurin ne in a code way, ban fada musu abun da ya faru ba”

“Dadina da kai ai akwai hankali, ka kyauta”

Hurriya ta dube shi.

“Yaya ina wuni?”

“lafiya kalau shi ne kika kama hanya kika taho a madadin ki kirani”

“Yaya ko na kiraka Appa ba zai saurara ba saboda ransa ya bace sosai, kuma ba ni da wayar da zan kiraka ma”

“Duk gidan nan ki rasa wayar da zaki dauka ki kirani?”

Hajiya Binta ta shiga tsakani ganin kamar Yasir yana neman mada abun fitina.

“Aa ba haka ba ne, ita kanta bata cikin hayyacinta a lokacin da ta baro gidan saboda tashin hankali, ta ina zata tsaya neman wayarka ma, kuma kana jin tana fadar cewar yayi fushi ba zai saurara ba”

“Tsohuwa kokari kareta kawai kike yi, amman  da ta kira ni ai ba zata baro gidan ba, yanzu da wani abun ya sameta fa”

“Laifin waye ba na mahaifinka ba? Akan me zai korota a dare yace ta tafi ta bar masa gida kamar wadda ta yi cikin shege”

“Ita ma tana da laifi ai, Hajiya ta fada min duk abun da ya faru ba zai yiyu ka zauna ka yi ta fadawa kawa karya da gaskiya ba, gashi yanzu har mahaifinta ta dauko kafa ya zo ma Appa da wani zancen banza”

Hajiya ta tabe baki.

“Uwarka kuma dai ai ba zata fada maka gaskiya ba, karya da gaskiya zata hada ta fada maka saboda ka yarda da ita ta karyarta Hurriya ka san sai ba son Hurriya suke ba”

“Haba Hajiya wace irin magana ce wannan? Wannan ai hadin fada ne, sai ki hada Hurriya da Hajiya ta dauka ko gaske ne”

“Yasir kai ma kasani da Khairiyyah ce ko Salma ko Rumana aka kora a gidan nan kana ganin Kaltume zata yarda ta fito a dare kamar wannan?”

“Sai da na yi mata magana tace min ita ma bata san fitar Hurriya ba”

Hajiya ta tabe baki, Hurriya kuma tana cin indomie ziri ziri. Yasir ya mike tsaye ko da ace Hajiya Kaltume karya ta fada masa ba zai so ya zauna a gurin da ake zagin mahaifiytarsa ba, domin komai lalacewarta mahaifiyarsa ce.

“Alhamdulillah tun da tana nan, ni zan tafi idan Appa ya huce sai na dawo na dauketa”

“Toh a gaishe da gida”

Hajiya Binta ta fada tana raka shi da kallo, Hurriya ma ta dago kai ta kalleshi.

“Yaya sai da safe”

“Sai da safe”

Ya amsa ba tare da ya juyo ba.

“Ina zata fada maka gaskiya, wannan Kaltume ba baki na yi mata ba, amman da wahala ta gama lafiya”

Hajiya ta fada bayan ya fice. Hurriya dai bata ce komai ba, ta cire hannunta daga taliyar tana kallon wani gafen na dabam, zuciyarta na raya mata yayanta ma yayi fushi da ita a yanzu.


WASHE GARI....

_Barka da safiya Namra, fatar kin tashi lafiya ya su Mama da Daddy, And my beautiful Young Lady, hope kowa yana kalau, a mika min gaisuwa gurin gimbiyar please_

Ta aje wayar a hankali bayan ta gama karanta sakon ta manhajar whatsapp dinta, sai ta nufi windows dinta ta bude curtains din tana kallon kasan bene zuciyarta na gabato mata da wani abu na rashin dadi da bata san dalilinsa ba.
Me yasa zata ji haka, shi ne abun da ya fara zuwa mata a rai, daman ai be ce yana sonta ba balle har tace ya koma gurin kanwarta ne. But at first alamunsa sun nuna ni yake so. Wata zuciyar ta fada mata. Ta kai hannunta tana taba karamar sarkar dake wuyanta.
Yana yawan tambayar Hurriya, amman ban yi zaton ita yake so ba, ko kuma dai ya juya kanta ne saboda ya ga ta fini kyau. Sai kuma ta juyo tana kallon dakin kamar wani bakonta sai sake sake take a ranta, wai it's normal ya so Hurriya domin be furta mata so kai tsaye ba, but why take jin babu dadi so disappointed? It's because of ta fara sabawa da shi kwana biyu, the way he approached her gashi da saka nishadi da iya kula da aika ko kuma saboda tana tsamanin ita zai ce yana so.

Ta bar jikin windows din ta nufi gurin da ta aje ledar da ya kawo ma Hurriya ta bude ledar ta ciro waya tana dubawa irin wyar Momy ce sak daga kala har model. Ta sake saka hannu cikin ledar ta ciro Perfume set masu kamshi sosai. Sai da ta shaka turare sannan ya maida komai yadda yake, ta nufi wayarta ta dauka. Ta rubuta masa.
_Bata karbi komai ba, na yi try bata karba ba, tace na aje maka_

After ta yi sending sakon sai kuma ta ga kamar be dace ta yi haka ba, but me zata yi? Ta karba da sunan Hurriya ta karba, yayi ta jiran kiran Hurriya ya ga shiru, ai kara ta fada masa gaskiya, ta jefar da wayar a kan gado tsakanin faduwar wayar da shigowar kiran Salim ba za a iya fadar wanda ya riga wani ba. Hannu ta kai ta dauka ta danna picking

“Are you free mu yi magana?”

Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta amsa masa.

“Eh ina jinka”

“Me yasa bata karba ba?”

Ta daga kafadunta kamar ance nata yana tsaye gabanta yana kallonta.

“Ban sani ba, maybe she's not interested, kuma bata shirya ma hakan ba, domin wani be taba nuna yana som Hurriya ba, so ina tunanin ba abu ne mai sauki ta karbi abun ba, saboda tana da banbanci da mu, tana ganin abubuwan differently”

“Amman da kika fada mata ya kika ga reaction dinta?”

“Not good... Not Bad...”

“How do you think zan iya shawo kanta”

Ta taka zuwa gaba tana shafa goshinta.

“Ina ganin kamar ba a takurawa mutum akan soyayya she's 19yrs idan tana ra'ayinka zata sani”

“Or Maybe i can talk to her by myself? Ya kika gani na fahimtar da ita abun da ke zuciyata kuma na nuna mata ba da wasa na zo nan ba, ko kuma kina ganin sai mun fara daukar permission gurin iyaye? Maybe ita ma zata fi yarda da ni”

Ta yi shiru kamar mai tunani.

“Karka yi saurin tafiya gurin iyaye, ka fara magana da ita ka ji ta bakinta, domin Appanmu baya daukar komai da wasa”

“Okay zan yi haka, zan shigo yau da dare ko na zo yanzu”

Ya lumshe ido ta bude jin yadda yake rawar jiki.

“Da dare zai fi sirri, domin bata nan jiya ta koma gurin kakarmu da zama, zan kwatanta maka gurin”

“Zan fi jin natsuwa idan muka tafi tare, and Kakarta ma zata fi daukar abun da muhimmanci, idan kina ganin babu matsala zan fara zuwa na dauke ki sai mu tafi tare”

Samun kanta ta yi ta saka bijirewa rokonsa, duk kuwa da zuciyarta ta raya mata haka, domin tana son ta cire kanta ne daga duk wani abu da ya shafe shi a yanzu saboda ya nuna ba ita yake ra'ayi ba.

“Shikenan Allah ya kaimu”

“Ameen thank you”

Ta sauke wayar tana kallon kiransa har sai da ya yanke sannan ta dauke fuskarta tare da ajiyar zuciya. Bata kara raina kanta ba sai bayan Sallah Isha'i a lokacin da ya kira wayarta ya sanar mata yana waje yana jiranta, sanin ba dan ita ya zo ba, ya saka bata cilastawa kanta shafa ko da hoda ba, balle kuma ta canja tufafi ko saka turare. Tun bayan wanda ta saka sa rana bata sake saka wani ba, mayafi kawai ta dauka ta yafa a saman gowns din atamfar dake jikin sannan ta saka shoes din da suka yi shige da atamfar. Sannan ta fito dakinta ta nufi dakin Momy, kamar jiya yau ma waya ta same ta tana yi. Daga bakin kofar dakin ta tsaya rike da kofar

“Momy zan leka waje ina da bako?”

Wani kasaitaccen murmushi ya bayyana a fuskarsa Momy, ba tare da ya yanke kiran ba ta ce.

“Haka nake so, na jiya ne ko wani dabam?”

“Shi ne na jiya”

“Yayi kyau, amman ki sake fuskar mana, ki yi far'a ba fuskar damuwa ba”

Ta amsawa Momy da kai, Momy ta kara mata da cewar.

“Make sure kuma wanda ya cancanta ne, kin san dai waye iyayenki”

Nan da kai ta amsa mata,

35 / 86