HURIYYA 1&2 COMPLT BY KHADEEJA CANDY

Author :  KHADEEJA CANDY Category :  Romance

Chapter   38 / 86

111K to 114K   out of 257.5K words

matsalar ne? Da yanzu za a haifi Hurriya har ta fara hada munafurci ne? Da take kwance bata da lafiya ni na saka mata ne? Mugun bakin kwadayinta ne ya ja mata”

“Momy ma Appa take aure, amman baki mata masifa kamar yadda kike yi ma Amma, Amma tana son mu tana nuna mana kulawa tsabanin Momy da ko bangarenta bata son mu shiga, kuma idan har suna da laifi to duk laifinsu daya ne domin Appa suka aura”

“Ke yarinya ki iya bakinki, idan baki san gari ba saurari daka, banbancin Iyami da Nafisa ai a bayyane yake, Nafisa a can ya ganta ya auro, Iyami kuma sai da ta gama cin duduniyata ta san sirrin gidana da na mijina sannan ta kulla min gadar zare ta zubar da ni a kasa, ke ba zaki gane abun da ake ji ba, saboda ke yarinya ce baki san me duniya take ciki ba sai nan gaba”

“Ko da hakan ta kasance a gareni, ba zan tsaneta kamar yadda kika tsani Amma da Hurriya ba, da ina ganin kamar ke ce mao gaskiya amman daga lokacin da aka kashe Hamad, sai tunani ya canja wane irin tsana ce zata saka a kashe rai? Idan Amma tana da laifi Hamad fa? Me ya aikata? Yaron nan yana kuka yana kiran sunan Appa da mahaifiyarsa suka fitar da shi, kansa na jini yana ihu yana fadar ayi hakuri yana rike kansa dake jini yana kiran sunan Hurriya daga karshe ma sunana ya koma yana kira, Hajiya na kasa manta wannan duk lokacin da na kalleki wannan abun nake gani, amman ni cewa kika kar a taba ni saboda ina yarki wace irin zuciyata ce wannan?”

Hajiya Kaltume na mikewa tsaye Khairy na turo kofar falon ta shigo da sallama. Hajiya ta yi saurin kallon kofar idonta kamar za su fado saboda razana.

“Wa'alaikussalam”

Ta amsa mata muryarta na yin kamar zata yi rawa. Khairy ta karaso cikin falon tana musu kallon tuhuma domin jiki da fuskar Hajiya Kaltume ya nuna alamar ba lafiya ba, ga Ruma sai kuka take sosai.

“Lafiya?”

“Lafiya Kalau”

Hajiya ta amsa mata da sauri, Ruma ta tashi tana kuka ta nufi stairs, Khairy ta bita da kallo har ta haye sannan ta kalli Hajiya da hantar cikinta ke kadawa ta ce.

“Me ya faru take kuka?”

Abun ka da makiri kuma wanda karya bata yi ma wahala a take Hajiya ta juye abun domin bata son kowa ya ji.

“Munafurcin da Hurriya ta yi ne ya taba ta”

“Munafurci?”

A tsaye Hajiya Kaltume ta zubewa yarta komai da Namra ta fada har ma da wanda bata fada ba, daman ai ba zata bar miya haka nan ba sai ta kara mata gishi da magi.

“Wallahi kawai ki fadawa Appa shi zai yi maganinta idan ba haka ba, shi ma kansa sai ta hada shi da Hajiya, waya sani ma ko ta zugota ta zo tace ba ta yafe masa ba, ko kuma ta rantse sai ya sake ki, daman tana da haushin barin gidan nan da uwarta ta yi, shiyasa ni gaba daya fa bana kaunar yarinyar nan, ga iya jan hankalin maza na bala'i kamar wata rikakkar karuwa”

“Wannan kuma ba banza ba, ai kin san uwarta sai ta wanke ta bata sha, kamar yadda ta sha ta dauke hankalin Alhaji har ya aureta”

“Gaskiya ni ma i doubt wannan farin jini da jan hankalin ba banza ba ne, ba zai yuyi ace kowane namiji farar mace mai kyau yake so ba, to mu ayi yaya da mu bakake?”

Tana fada tana bata rai kamar ta ci magani.

“Ba farin ne kawai ba, har da asiri”

“Daga gani ma ba banza ba, Hajiya tafi ki fadawa Appa ya daukar mata mataki tun wuri”

Ta zauna saman kujera tana ta fushi kamar an mata wani abu, kamin ta shiga Gallary wayarta ta kamo hoton Hurriya ta kura ido tana son tantance abun da Adam ya gani a fuskarta da jikinta da ya nace sai ita, ga Fadeel ma ko a jiya da ya zo sai da ya nemi yin magana da ita.
Hajiya Kaltume da har lokacin a tsaye take ta juya ta nufi kofar dake gefen dinning wanda zata sadata da bangaren Appa, zuciyarta fal da tsoro na maganar Ruma, yanzu ba kisan ne abun da ke ranta ba, fallasar asirinta ne abun da yafi damunta, shekara uku amman Ruma ta kasa mantawa ta saka sakewa gaba daya ta canja tun a lokacin da wannan abun ya faru, idan kuma har zata rika sakin baki haka wata rana dole asirinta zai tonu, ita ta san har ga Allah bata ce a kashe Hamad ba, ba saka an dauke shi dan a kashe shi ba, hasalima ba shi aka je dauka ba, Hurriya ta ce a dauka, tsaitsayi ya biyo ta kan Hamad ashe da rabon ya bar mata baya da kura. Bata san ta isa bangaren Appa ba sai da ta ji ta bugi kofar shiga, a nan ta sauke ajiyar zuciya ta rufe ido ta dafe kanta da hannu daya.

_Kai wayyo Allah... Da na sani ban aikata wannan abun ba, da ma ta asiri na bi kamar yadda na yi ma Iyami, duk gajin hakuri ne ya ja min, yanzu ko yaran nan aka kama suka fadi sunana ai na shiga uku sunana zai bace a duniya, yarana su ji kunya musamman ma matan nan_

A ranta take ta sake sake rashin natsuwa da tashin hankali na kara kusantar ta, ta sauke ajiyar zuciya ya kai sau takwas sannan ta sauke hannunta ta murda kofar ta shiga, babu kowa falon dan haka ta nufi karamin falon Appa da ya fi yawan zama. Yana ganinta yayi saurin sauke wayar da yake ya yanke kiran murmushin dake fuskarsa ya bace.

“Hajiya”

Ta zauna kusa da shi tana fada.

“Na'am Alhaji a nan ake hutawa, Nafisa bata shigo ba?”

“Ina tunanin sai an jima kadan zata shigo”

Yayi saurin rejecting kiran dake shigo masa ya saka wayar silent ya aje ta a gafe.

“Toh bari na yi magana ta kamin ta shigo, wata kila ma ita ce take kiranka kasan sarauniya ce wani lokacin sai dai ta kira ta tambaya abun da kake so ta zo maka da shi, ba kamar mu da bama raina lada ba”

“Aa ba ita take kira ba, wani.... Sakatarenmu ne... ”

Ya amsa kamar marar gaskiya. Cikin rashin kuzari na abun da ya faru ta kora masa da bayanin abun da Hurriya ta yi har Hajiya Binta ta aiko musu da sako. A take Appa ya hade fuska ya bata rai sosai daman a yanzu baya ganin farin Hurriya sai bakinta.

“Wai yarinyar nan me take son zama ne?”

“Toh ka gani dai idan baka daukar mata mataki ba, sai ta lalace kuma nan gaba ba a san me zata yi ba, kai kanka idan baka dauki mataki ba sai ta hada ka da Hajiya, kara tun wuri ka rabata da gidan Hajiya ka maida ita can gurin uwarta ko kuma ka dawo da ita nan din, domin ni dai ina jin tsoron shairin yarinyar nan, kara nan tana karkashin kulawarka zaka saka mata ido”

“Bana bukatar Hurriya a gidana”

Appa ya fada a fusace.

“To ya muka iya da abun da ya fi karfin wuta, in ji kishiyar konanniya, hakuri zaka yi tun da hannunka baya rubewa ka yanke ka yar kar dai ta zauna gurin uwarta ko gidan nan, nan din ma zai fi saboda Hajiya zata iya cewa ba zata zauna gurin uwarta ba, kuma idan ma ta zauna can zata iya sulalawa ta koma gidan Hajiyar ba tare da saninka, kara tana gabanka kana ganinta, albashi ka samu ko masinja ne cikin ma'aikanta ka aura masa ita mu huta...”

Uffan Appa be sake cewa ba ya bata rai sosai, domin sam maganar da Hajiya ta fada masa na abun da Hurriya ta yi be masa dadi ba.
𝐊𝐇𝐀𝐃𝐄𝐄𝐉𝐀 𝐂𝐀𝐍𝐃𝐘


Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲


𝐏𝐚𝐠𝐞 2⃣1️⃣



Appa be raba dayan biyu ba Momy ta turo kofar dalon ta shigo, yadda ta tararda Appa da Hajiya Kaltume a kujera daya ya saka ta daure fuska ta fara wani kallo na uku saura kwata.

“Miye haka Alhaji? Ina ce yau dai girkina ne, ko kuma irin abun da ake yi ma Iyami shi za'ayi min?”

Hajiya Kaltume ta tabe baki, har ta juyar da fuska sai kuma ta juyo ta kalli Momy.

“Magana ce ta kawo ni, maganar da zata taimake ke ki ta taimake ni kuma ta taimaki wanda muke neman aljanna karkashin kafarsa, magana ce akan Hurriya kuma yarki aka aiko da sakon shi nake fadawa Alhaji”

Momy dake tsaye ta dauke kai domin haka be gamsar da ita ba, cikinsu babu wanda yake son ganin abokin zamansa a bangaren mijinsa idan ba girkinsu ba ne, sai dai Iyami suna mata haka, su kam shiga su yi magana da Appa ko da tana ciki wani lokacin har sai Appa da kansa ya nuna musu baya so, ita kuma tana kiyaye yin haka idan ba girkinta ba ne.

“Toh tun da kin fada ai sai ki kama hanya ko kuma maganat bata kare ba ne”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi kamar ba ita ba.

“Nafisa... Hajiya Nafisa... Ya fa kamata ace mun aje kishi a yanzu, ya kamata ace mun san girma ya kama mu a yanzu, ni idan ma kina son kwanan idan girkina ya zagayo ai sai na yafe miki, ni dai ina neman mafita ne acikin lamarin nan, domin Hurriya ba ni kadai ta sako a gaba ba har da ke.. Da kuma mahaifinta, wata kila nan gaba kadan idan tana zaune a gidan Hajiya zata iya sakawa ta tsine mana gaba daya, ko kuma ta cilastawa Alhaji rabuwa da mu”

Appa yayi karaf ya ce.

“Aa Hajiya ai tana da hankali da tunani, ba zata yi haka ba”

“Baka da tabbaci kai kanka idan aka fada maka Hurriya zata aikata abun da zai saka ka koreta a gidan nan zaka yarda? Amman da yake butuluce kamar uwarta ai gashi nan ta je ta zage ka a wani gurin ta saka makota suna maka kallon azzalumi, nan gaba kadan kuma baka san abun da zai biyo daga gurin Hajiya ba, kasan dai yadda take son Hurriya take daukar shawararta”

Sai a lokacin Momy ta kai zaune, bayan Hajiya Kaltume ta gama rattaba bayannanta.

“Ni abun da nake gani kawai ka yi hakuri ka dawo da ita gidan nan, idan ba haka ba ma zata iya lalacewa”

Momy ta dubi Hajiya Kaltume ta ce.

“To miye amfanin korarta da Alhaji yayi? Ai sai ta dawo ta cigaba daga inda ta tsaya tana hada mutane”

“To ai mun san halinta yanzu, ko da ta fada ba zamu yarda kuma dole a ja mata kunne”

“To sai dai idan bangarenki zata zauna, ni dai na gaji da zamanta a gurina, balle kuma yanzu”

“Aa ni da take kallon a matsayin makiyiyarta, ta ina ma zata yarda ta zauna a gurina”

Appa ya gyara zama ya kallesu one after the other ya ce

“Kar wanda ya sake bani shawara ko zabin gurin da Hurriya zata zauna, idan har zan dawo da ita cikin gidan nan a inda nake son ta zauna zata zauna, daga gidan har ku da yayanku a karkashin ikona kuke, musamman ke Nafisa na lura da bakinki ba shi da linzami akan irin wannan maganar, kai tsaye kike furtawa, na yi miki kashedi amman baki ji ba, wata kila sai kin ga zahiri... ”

Da mamaki Momy ta kalleshi bakinta a sake ta ce.

“Allah da iko yake, in ba dan ana son a maida laifi gareni ni da aka raina ba, ai Kaltume ma ta yi maganar ba zata zauna a bangarenta ba, amman sai ni kake yi ma radda wato ga ni itace mai dadin hawa, to Allah ya baka hakuri ta zo ta zauna, daman korar ai ba ta Allah da Annabi ba ce, tun da ga shi har kuna son a dawo da ita”

Appa ya dakawa Momy tsawa domin ita kadai ce yake yi ma fada a yanzu, Hajiya Kaltume kuma an saka masa tsoronta ko da ta yi ba daidai ba ba zai iya magana ba, and ba zai iya bijirewa umarninta ba.

“Nafisa... Akan yayana zaki iya janyo wa kanki masifar da zata daukeki daga gidana, bana son ana aibanta min yaya dukansu, ki sani Hurriya ko kisan kai ta aikata Hurriya Haruna Mai Yadi haka za a kirata babu wanda ya isa ya kankare wannan, kin fara kai min hanci kuma ina daf da fyatoki, idan baki rike rike girmaki ba, baki dauke idonki akan Yayana ba za ki sha mamaki”

Hajiya Kaltume dake murmushi cikin rai, ta kalli Appa da ciki wani yanayi dake nuna da gaske take yi ta ce

“Haba Alhaji yanzu saboda Hurriya sai ka ce zaka fadi wani abu marar dadi akan Nafisa, adai yi hakuri shekara nawa ana tare, yanzu ga yaya sun girma ana zancen aure kuma zaka bari shaidan yayi tasiri akanka? Kara dai ayi hakuri duniyar ma duka duka nawa take? Ni ko Iyami ban jidadin rabuwa da ita ba, tun da ga yaya biyu ko da yake yanzu Hurriya ce kadai ta rage, amman dai ba dadi ai, da yanzu tana nan da duk ba zamu samu wannan tsabanin ba, tun da yarta taba hannunta”

Cikin fushi Appa ya ce
“Ko yanzu ai zan iya kai mata ita, ba dole sai ta zauna nan gidan ba”

“Aa kara dai ta dawo nan din, can ga uwa tana jinya abun ai sai ya taru ya zama biyu, wahalar ta yi musu yawa, kana ganin wannan halin da hurriya ta fara idan ba a nan take ba ai kara baci zata yi, ni da kaina zan shirya mu tafi tare a daukota daga gidan Hajiya, ko yanzu ai ta horu”

Momy dai bata sake cewa komai ba, domin bata son Appa ya sake furta mata wata maganar marar dadi a gaban Hajiya Kaltume.

“Ni zan tafi bangarena sai da safe...”

Appa ya mike tsaye ya nufi dakinsa, kama yadda Hajiya Kaltume ma ta fice daga falon bayan ta yi musu sallama. Duk wani damuwa da tunanin tonuwar asirinta ya gushe a zuciyarta saboda farincikin ganin fadan Appa da Momy. Da murmushi ta shigo bangarenta tana maida kofar dakin ta rufe Kulu ta mike tsaye hannunta biyu a hade tana murzawa.

“Hajiya an fito, na ga ita ma Momyn ta fita shiyasa na zo da sauri, sai kuma aka ce min kin shiga bangaren Alhaji shi ne na ce bari na jiraki”

Hajiya Kaltume ta dan yamutsa fuska yayinda ta kawo gurin da Kulu take tsaye da daurin zanenta irin na masu siyar da ganye.

“Zuwanki ai ba shi da wani amfani kulu, kullum babu wani abun da kike kawo wa, tun lokacin da na saka binciken dakin Hurriya baki kawo min komai ba”

Kulu ta shiga rantsuwa.

“Wallahi Hajiya na bincike dakin Hurriya kaf har kayanta sai da na duba amman ban samu komai ba, kin ga kuma dole na fada miki gaskiya ba zan miki karya ba”

“To yanzu me ya kawo ki?”

“Dazun ne ina cikin Kitchen ina wanke kayan da suka ci abinci, kin san Momy bata son a bar kaya ya kwana ba a wanke ba, to ina cikin wankewa sai ga wani bakon Momyn ya shigo, yana ta masifar wai an kori Hurriya Momy bata yi komai ba, har umarni yake bata wai ta dawo da ita, ita kanta Namra da ta saka baki a maganar sai da yayi kamar zai mareta”

“To waye shi?”

“Ina tunanin dan yayanta domin can da yana zuwa gidan sosai kuma danta take kiransa tana nuna masa so sosai, haka suke ce masa kefin”

“Miye alakarsa da Hurriya?”

“Toh nima shi ne ya ba ni mamaki ai, na ce ko sonta yake yi, ya ma daina zuwa an fi shekara uku yanzu sai yanzu ya dawo, amman ita ma kanta Momy da Namra ina jin suna tsinewa Hurriyar suna cewa bata da albarka”

“Ai dole, tun da ta fara hada munafurci, amman duk da haka ni da kaina zan tafi na dawo da ita gobe, sai na nuna mata hankalin Babba dabam dana yaro, kuma idan za a asake korarta sai daia yi nata korar da zata tafi nesa da garin nan gaba daya, ba wai ta tsaya a kusa da Hajiya ta hada mu ko kuma Appanta ba”

“Shi ke nan Hajiya, daman na ce bari na fada miki ne abun da na ji”

“Kin kyauta kuma ina son cigaba da abun da kike yi, da zarar kin ji kyas ki zo ki fada min, tun daga kan Hurriya har Nafisa da kasuwancinta”

“Toh Hajiya na gode mu kwana lafiya”

Hajiya Kaltume ta daga mata kai, sannan ta bita da kallo tana tauna maganar da ta fada mata a ranta. Waye yaje yana masifar a dawo da Hurriya? Sonta yake ko kuma me? Waya sani ma ko kanta take bashi ko yake neman samu saboda ta zama marar aji yanzu, tun da uwarta ta bar gidan, kuma gashi har wani dan iskan ma Adam ya ce yana sonta.

“Hajiya...”

Ta juyo ta kalli Yasir dake saukowa yana sanye da jallabiyar da ya siye a Khadeeja Candy Store, sai shinning take kamar an zuba mata mai.

“Yasir ka dawo?”

“Eh, na shigo ai baki dakinki Khairy tace kin tafi bangaren Appa”

“Eh na je na yi magana da shi ne akan Hurriya, kasan kai baka son laifinta shiyasa ban fada maka abun da ta yi ba”

“Kararta kika kai gurin Appa kuma? Haba Hajiya? Duk bayan wannan abun?”

“Aa ba kararta na kai ba, sako Hajiya ta aiko mana wai muna takurawa Hurriya magana dai babu dadi ji, ni kuma na je na samu Appanku na bashi shawarar dawowa da Hurriya a gidan nan zai fi, ka ga mun guje bacin ran Hajiya kuma mun shirya ta da mahaifinta”

Yasir yayi murmushi dake fitowa har daga zuciyarsa.

“Haka na ke son ki zama Hajiya, kuma na ji dadin haka Allah ya saka miki da alheri”

“Amin”

Ta kalleshi sama da kasa.

“Yau ka

38 / 86