Author : KHADEEJA CANDY Category : Romance
gaba dayansu, sai Daddy ya sa a kira masa Captain dake dakin sama tun safe be fito ba, kamin ya fito Daddy ya kalli Momy Ikilima ya ce.
“Ikilima ki shiga gurin Turai a cikin kayana akwai wata shadda irin wannan ta jiki sabuwa ce a cikin leda, a dauko ta ta hado miki da sabuwar hula, da turaren da ba a fasa ba”
“Toh Yaya”
Ta tashi ta fice, domin bangaren da Daddy yake sauka dabam idan ya zo gidan. Fitarta da minti biyu Captain ya shigo falon, a kasa ya zauna ya gaishe da iyayensa.
“Ya karfin jikin Captain”
“Alhamdulillah daman stress me kawai Abba na ji sauki”
Ya amsawa Alhaji Munzali, kamin ya daga kansa yana kallon dinkakkiyar Shaddar dake Ikilima take mika masa, ya saka hannu biyu ya karba.
“Shiga ka yi wanka ka saka wannan shaddar ka feshe turaren nan gaba daya a jikinka”
“Daddy why?”
Ya tambaya da confused.
“Ina son ka raka ni airport ne kuma ina son mutane su ga yarona cikin mutunci, kuma karka dade ka fito yanzu nan ina jiranka”
“Toh Daddy”
Captain ya mike tsaye ya fice daga falon na Nene. Dakin da ya zama masaukinsa ya shiga ya cire tufafin jikinsa yayi wanka ya fito ya shafa mai ya saka shaddar ya dauko turaren ya feshe jikinsa gaba daya sai da kwalbar turaren ta kai kasa sannan ya dauki hula ya saka a kasan shi kansa, ya dubi kansa a jikin madubi shi kanshi ya san yayi kyau abun da ake kira da kyau, farar shaddar ta haske shi matuka... Wayarsa ya dauka ya saka aljihu da wallet dinsa sannan ya nufi kofar dakin ta bude ya fita yana wani irin kamshi mai sanar da zuwansa tun kamin ya iso. Ga mamakinsa sai ya samu babban falon na kakarsa a cike da mutane ciko har da mahaifiyarsa da kakarsa da abokiyar zamanta da duka wanda yake gidan a lokacin. Da mamaki ya sauko falon yana kallon kowa kowa kuma yana kallonsa...
“Zo nan Jamal...”
Daddy ya fada yana murmushi, Captain ya nufi gurinsa sai Daddy ya mike tsaye ya saka hannunsa aljihu ya ciro goro da dabino ya ce.
“Bude min hannunka... ”
Captain ya bude tafin hannunsa na dama ya mikawa Daddy, sai Daddy ya zuba masa dabino da goro dake hannunsa.
“Mun je jaje, kuma mun roki iri, kuma an ba mu, na nema maka auren Hurriya a yau, kuma an daura mun bada zinari na miliyan 50, a matsayin sadakinta, saboda dka fada mana mai tsada ce, shiyasa muka siye ta da kima, yau mai tsada ta zama mallakinka, Hurriya ta zama matarka halak malak...”
Kamar an aje hoto haka falon yayi tsit kamar babu wani abu mai rai a ciki, daga Captain har iyayensa babu mai motsi....
MASU KARATU BA BIYA A ZO A BIYANI HAKKINA A SAUKE NAUYI A HUTA
500 to Zenith Bank
Hadiza Abubakar
2451879008
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
Da farinciki Appa ya shiga dakin Momy ya nufo inda take zaune fuskarsa da annuri ya zauna gefen gado. Da mamaki yake kallonsa daman kam mamakin kiran da Daddy yayi mata ya karbi sarka be gama fita mata ba.
“Alhamdulillahi”
“Allah abun godiya”
Ta amsa sannan ta kalli goro da dabinon da ya shigo da su gabanta na faduwa.
“So da yawa kanyi abu basan alherinsa ba sai a gaba, wani abun kuma Allah ya barwa kansa sani, ban tana jin farinciki da alfahari da aurenki ba sai yau, Allah ua miki albarka Nafisa sanadinki yau na fita bakinciki an shafe min duk wata damuwa da nake jinta a raina saboda faruwar abubuwan nan”
Momy ta yi murmushin rashin gamsuwa.
“Daman ai Yaya akwai karanci, wani abun yayi maka ko?”
“Ďanki Jamal kuma dansa ya nemawa auren Hurriya, kuma be bar gidan nan ba sai da aka daura auren”
Momy ta kyalkyale da dariya har da daga kafa sama da buga a kasa.
“Yau kuma ni ake yi ma zolaya, taya za'ayi daurin aure a cikin gida ba mu sani ba kuma daga kai sai yan tairarun mutane? Kila dai aurenka ne za a daura ko kake min kwano kwano”
Appa yayi murmushi mai kyau.
“Shi aure ai ba dole sai an tara mutane ba, amman amsu aikin gidan nan da yayanta Yasir sun shaidin auren Hurriya aka daura da Jamal a yau, kuma yayanki ya bada Zinari a matsayin sadaki”
Ya aje mata goro da dabino na daurin auren a gadonta.
“Kin ga goro da dabino nan!”
Ta kalli goron da dabino har lokacin dariya take domin maganar Appa ba magana ce mai kama kai ba, sai dai kume? Appa ba zai mata wasa ba, ba zai ce anyi ba alhalin ba ayi ba. A take dariyar ta bace mata bat ta daga kai ta kalli Appa.
“Da gaske Alhaji? Yayana ya zo gidan nan ya nemawa Captain auren Hurriya?”
“Har an daura, yace ba zai iya da rigimarki ba, dan haka ya wuce yace ni na sanar miki....”
Momy ta mike tsaye wayar dake cinyarta ta fadi kasa.
“Aure Alhaji? Auren Hurriya aka daura da Captain?”
“Kwarai, kowa ya ji zai yi mamaki, kuma tabbas Alhaji Turaki ya kai mutumen kirki har ya wuce, ya yaye min bakinciki kuma na yarda zai rike yata da amana”
Momy ta dafe zuciyarta.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
La'ilaha Illallahu Muhammad Rasulullahi Sallalahu Alaihi Wassalam”
Appa ya bita da kallon al'ajabi ganin yadda ta yi kamar wadda aka fadawa mugun abu.
“Yanzu duk matan duniyar nan Captain ya rasa wa zai aura sai Hurriya? Yarinyar da duniya ta gama ganin tsiraicinta? Yarinyar da ko ido bata shi a yanzu? Anya Captain yana cikin hayyacinsa?”
“Ita Hurriya ba mace ba ce? Da kike fadar ya rasa wa zai aura sai ita? Wane irin magana kike haka ne Nafisa?”
“Captain ya fi karfin Hurriya bata cancance shi ba, rantsuwa fa na yi cewar Captain ba zai auri Hurriya ba, shi ne Yaya zai shammace ni? Kuma ya biya sadakinta da zinarina da ban taba sakawa ba? Naira miliyan hansi akan makauniya yarinyar da duniya ta gama da ita?”
Appa ya mike tsaye ya daga hannu kamar zai mari Momy sai kuma wata zuciyar ta hana shi, a madadin haka ya nunata da yatsansa.
“Ki san abubuwa da kike fada akan Hurriya, kamar kin mace a gaban waye kike tsaye ni fa na haifi Hurriya, a madadin ki yi farinciki jininki ya auri jini sai ya zama abun bakinciki a gurinki”
“Idan kai ne mahaifin Hurriya sai me? Na yi farinciki ďan ďan'uwana ya dauko yar kishiya ya kawo a matsayin suruka? Ya tsallake Namra ya tsallake duk yaran family ya fada gurin Hurriya”
Appa yayi murmushi yayi girgiza kai.
“Yanzu na fahimci komai, Allah ya huci zuciyarki yara kuma Allah ua ba su zaman lafiya... ”
Appa yayi dariya mai sauti ya fice daga dakin. Momy ta dora hannu a kai tana ta rawa kamar mai jin sanyi.
“Daman wannan ne dalilin zuwa? Har kana fada min Captain ya hakura? Ni kake yi ma wayon Yaya? Ko ba zai auri Namra ba me yasa zaka amince masa ya auri Hurriya? A cikin falona za a nemi auren yar kishiyata ba yata ba, duk tarin dukiyar Yaya da ta matarsa ďa ďaya da suke ji da shi ya rasa wa zai aura a duniya sai Hurriya? Yarinyar ido ya rufe mata? Aka tallata tsiraicinta, yarinyar da uwarta ma ga aiki ta yi, talakawa maskakanta, tarin dukiyar Yaya Yau Hurriya ce yarinyar da zata raba a jiki a dukiyar gidanmu, kuma ta bangaren da ya fi gwabi”
Daki cinyarta tana jin kamar ta zaga tufafin jikinta, a matukar fucece ta fice daga dakin ta shiga dakin Hurriya ta fara yaye Bedsheets dinta ta jefar tana debo kayanta ta watsarwa abubuwan da ke fashewa kuma tana ta fashe su tana watsar tana kuka.
“Ashe sheri ne ya kawo ki bangaren nan, ashe mugun abu na karba na aje gashi nan kina bibiyata”
“Momy lafiya”
Namra ta tambaya tana kallon yadda ta watsar da kayan Hurriya ta fasa abubuwa. Momy ta juyo a lokacin da ta kalli Namra sai tausayin yarta ya kamata.
“Yayana ya daureni ya ci amanata Namra, na ci mutunci na ya watsa min kasa a ido, kuma ya nuna min ďansa ya fi yar'uwarsa”
“Momy dan Allah ki fada min me ya faru?”
“Auren Hurriya ya nema a gurin Appanku, Appanku kuma ya amince aka daura auren a cikin gidan nan yanzu nan”
Namra ta ji kanta ya dara da karfi.
“Aure abun kamar yar tsana? Ban gane aka daura ba, an taba daura auren haka babu kowa?”
“Daga mahaifinku sai Yayana da Yasir aka daura auren”
Wani abu ta ji mai sanyi ya ratsa kanta ya sauko har kafafuwanta.
“Momy da gaske...?”
“Me zai sa na miki karya.? Yaya yayi min abun da ban yi tsammani ba, da ace wani ne yayi min ba yayana ba zan ji zafi haka ba, amman ba komai kowa yayi mai kyau zai gani kuma Wallahi Hurriya ba zata sake zama bangaren nan ba”
Namra ta yi baya baya ta fice daga dakin daman a bakin kofa take tsaye. Dakinta ta shiga ta rufe kofar ta zauna hawaye suka silala mata a hankali.
“Aure?”
Ya tambayi kanta abin dai kamar ba zata fahimta ba. Shi ke nan duk wani fata da take da kuma wanda iyayensu suke yi ya tashi a banza yanzu? Hurriya ta shiga tsakaninta da Salim yanzu kuma ta raba ta da Captain ta aureshi? Ta mike tsaye ta isa gaban madubin dakinta ta zauna a stool tana kallon kanta, shi ita bata kai ba ne da Captain be yi hauka a kanta ba? Taya idonsa zai rufe ya tsallake ta ya fada kan yar'uwarta bayan duk abun da ya faru da Hurriya, to da bata aikata ba ai ta yi abin kunya, ta yi abun da cikaken namiji mai aji irin Captain zai guje ta zama matarsa ko dan saboda kunyar duniya. Salim ma ya kusa hauka akanta amman Captain ya goge mata hadda, ta saka hannayenta ta share hawayenta har yanzu jin take kamar dai ba gaske ba ne. Momy ta turo kofar dakin ta shigo ita ma tana kuka.
“Auren nan ba zai je ko'ina ba, Captain da yake da zuciya da saurin fushi kwana biyu ne zata fita ransa, kuma na san Hajiya Turai ba zata yarda ďanta ya aikata wannan abun kunyar ba, aure ba zai je ko'ina zai lalace”
Namra ta mike tsaye da sauri ta shige bandakinta domin bata son Momy ta ga kukanta, ganin take bata cancanci zubar da hawaye akan namiji ba, sai dai wadannan sun zame mata dole ne. Zaunawa ta yi a kasa bayan ta rufe bandakin tana kuka marar sauti. Momy na ganin hakan ta san yar gudaliyar yarta kuka bakinciki take, ita ma sai rauninta ya karu, jikin bandakin ta tsaya tana buga kofar.
“Namra bude kofar karki saka kanki a damuwa kinji, na san babu dadi amman ki yi hakuri karki wa damuwa kofa dan Allah ki kwantar da hankalinki, ni kaina ba zan bar maganar nan ba ba zan kyale lamarin nan ba”
Kalaman na Momy sai suka zama kamar makamashi mai hura wutar bakincikin dake zuciyar Namra, sai dai hakan be saka ta bude kofar ba, har Momy ta gaji da tsayuwa ta fice daga dakin, tana shiga dakinta mayafi ta dauka da key mota ko jaka bata tsaya dauka ba ta nufi family house dinsu.
CAPTAIN JAMAL POV.
A hankali ya fara rankwafa yatsunsa har ya jimke dabinon dake hannunsa yana kallon Daddynsa har lokacin an rasa mai cewa komai. Daddy yayi murmushi yana kallon dansa cike da alfahari kamar yadda Captain din ma yake kallon mahaifinsa ya kasa gasgata kalamansa.
“Da alama dai kuna bukatar na maimaita kaina, abun da nake nufi a nan.... ”
Ammy bata bari ya fadi ba ta mike tsaye cikin tsawa da hargagi ta ce.
“No bana bukatar ka maimaita mana sautin da fadij mutuwa ya fi shi dadin ji”
Ta tofar da yawu.
“Touf! Allah ya tsare gatari na da saran shuka, har abada ďana ya fi karfin wulakantacciya yarinyar yar talaka kuma wanda duniya ta gama ganin tsiraicinta Wallahi”
Alhaji Sadiq ya mike tsaye tana dagawa Ammy hannu.
“Hajiya Turai sai dai hakuri amman Wallahi an daura auren Jamal da Hurriya yau, idan baki yarda ba ki kira Nafisa ki tambaye ta”
Ammy ta kalli Daddy da sauri tana son kara tabbatarwa. Captain yayi murmushi ya rufe idonsa har lokacin hannunsa na rike da dabinon ya kasa maida hannun kuma ya kasa sauke shi kasa.
“Munafuntata ka yi Captain? Ka ce min ka hakura kuma sai ka juya ka shirya wani abun da mahaifinka?”
Cikin kuka Ammy take tambayarsa, sai ya bude idonsa da sauri ya kalleta raunace.
“Wallahi Allah ban san komai akai ba Ammy”
Hajiya Turai ta juyar da dubanta gurin Daddy.
“Saboda me? Saboda me zaka aura masa wannan yarinyar? Be fada maka ya hakura ba? Baka duba illar hakan ba a cikin zuri'arka?”
Daddy ya daga mata tsaya uku yana nuna mata daya vayan daya.
“Saboda na isa! Saboda yana sonta!! Saboda Allah be haramta ba!!! Kin ga dalilin nan uku su suka saka na je na nemi auren Hurriya a yau, mahaifinta kuma ya bukaci a daura auren a yau”
“Ikon Allah abu dai kamar a shirin film?”
Cewar Nene, Momy Ikilima ta ce
“A littafi dai wannan ai ya fi karfin shirin film”
Ammy da idonsa ya cika da hawaye har wasu za su zubo ta hau masifa.
“Da alama baka yi bincike ba kamin ka aura masa yarinyar nan, mahaifiyarta aikin gida ta yi fa!, ni ba zan iya karbar ta a matsayin suruka ba, ba zan ina nunawa duniya yarinyar nan a matsayin matar Captain ba”
Daddy nade babbar rigarsa.
“Kin gani Turai ba a daura auren yarinyar da Jamal ba sai da na yi ma mahaifina alkawarin zan rike yarsa da mutunci da amana, kuma a matsayinki na matata idan ba ki taya ki cika alkwarin nan ba, to be kamata ki barar da shi ba, karki zuga kanki da yawa ki kone kanki ta hanyar haramta abun da Allah ya halatta, hargaginki da kumbar baki ba zai saka Jamal ya saki yarinyar nan ba, domin ba je na auro masa yar mutune saboda ya zubar min da mutunci ba, ina ce Alhaji Haruna ma yana da kalar nasa rufin asirin idan kuma kin raina arikin gidansu ne yanzu danki take aure make her a billion naira”
“Wayyo Allah na wannan wane irin abun kunya abun bakinciki ne? Kenan duk abun da Jamal yake so sai mu biye masa mu aikata ko da halaka ce? Yarinyar da kare da mage suka maganin siraicinta, ita zaka hannu biyu mu karba a matsayin in-law?”
“Wannan kuma ďanki kike ci ma mutunci a gaban familynsa, ina jiye miki tsoron ranar da zaki yi nadamar nuna son zuciya fiye da abun da danki yake so, ki shirya da wuri karfe biyar jirgina zai tashi”
Daddy na kaiwa ya kabe rifarsa ya fice daga falon, Hajiya Turai ta kalli Nene da kowa dake falon tana kuka.
“Nene kina gani? Babu wanda zai ce komai ni za a bari da fadan nan?”
“Hajiya Turai me kike son mu ce? Aure ne an riga da an daura, sakawa zamu yi Captain ya sake ta ko kuma mijinki zamu rufe da fada, kowa a nan yayi mamaki amman abun da kaddara ta aiko dole mu karba mu zuba ido mu ga abun da Allah zai yi a gaba”
Cewar Alhaji Munzali, kamin ya mike tsaye ya fice daga falon. Alhaji Sadiq ne kadai yake lallabata.
“Ki yi hakuri Hajiya Turai, ki bi abin da danki da mijinki suke so, ki zuba ido ba fata muke ma amman idan akwai illa a cikin lamarin nan za su gani a gaba kuma su gane sun aikata kuskure, Jamal dai shi yake auren yarinya shi yake jin zai iya daukar komai da ya shafe ta to ke mike naki a ciki? Ki yi hakuri a matsayinki na uwa ki danne duk abun da kike ji dan Allah”
“Ba zan iya ba Alhaji Sadiq, Engr ya nuna min ba ni da muhimmanci a rayuwarsa da ta dansa, shiyasa be duba shawarata ko ra'ayina ba ya aikata abub da ya aikata”
Ta fice daga falon tana kuka, Hajiyar Maru wacce ta kasance abokiyar zaman Nene ta bi bayanta tare da Momy Ikilima, Alhaji Sadiq da Alhaji ya dafa kafadar Captain yace
“Ka dauko wani aiki mai nauyi Jamal, idan baka yi hakuri ka kai zuciya nesa ba ba zaka iya karasa ba, ka bawa kowa hakkinsa matarka da mahaifiyarka, Allah ya bada zaman lafiya ya hada kanku”
Ficewa suka yi daga falon sai ya rage daga Captain sai Nene a falon har jikokin Nene yan matan da kanana duk babu ko daya.
“Ka yi hakuri Jamal kowa ya ce zai iya sai an gwada aka ko zai iya dauka saboda haka ka saka kana'a a zuciyar.... ”
Sakin baki ta yi tana kallon ikon Allah ba