RAINA KAMA Tagwaye Cikin Gidan Fitina by Bilyn Abdull

Author :  Bilyn Abdull Category :  Romance

Chapter   30 / 36

87K to 90K   out of 107K words

maganar tasa, saida yakai aya sannan yace ¡°ranka yadad'e kokasha pills ne?¡±.
Kallonsa Galadima yayi, ¡°pills kuma? wane irin tambaya kakemin haka?¡±.
¡°afuwa ranka ya dad'e, matsalar taka tayi kama da wanda yasha tablet ne, mikaci na k'arshe jiya?¡±.
cikeda nazarin maganar Jalal yace ¡°fresh milk ne last abinda nasha jiya da daddare¡±.
¡°to amma bayan shi kafara jin matsalar?¡±.
¡°kusan haka gaskiya¡±.
Dr jalal dai shiru yayi, dan ya tabbatar wannan aikin desire tablets ne, amma koya fad'a dawuya Galadima ya yarda, sai kawai yashare ya had'a masa drugs da injection yamasa, yace yad'an kwanta na kamar 20 minutes a office d'in. bai musa masaba ya shiga inda jalal kan huta idan yaso, saiya kwanta kawai, dan shima bazai iya tafiyarba, d'akin ma da taimakon jalal d'in yashigo.
Ni bansan hidimar da akeyiba, dan rabona dashi tun bayan munyi maganar saki, abinci ma tun Wanda doctor tabanine a cikina, sai kusan 8 Samha takawo min kayan fruits dawani Abu mai dad'i daban san mineneba?.
Ta zauna mund'anyi hira kafin tafice. a bakin ta nakejin wai jibi Friday zasu koma India.
Na danci abinda takawo nasha magani nayi kwanciyata cikeda kewar 'Yar uwata dana kanyi akowanne dare.

Galadima kam bai dawo ba sai kusan 1pm, yana shigowa sashensa yawuce yay shirin barci ya kwanta, Alhmdllh zuwa yanzu yaji k'arfin jikinsa, sai dai zuciyarsa nata cud'a masa tunanin ina yasamo pills? dan shima yafara yarda da maganar jalal, musamman idan ya tuno furucin Munaya na d'azun da safe.
To kenan wani ya zuba masa bai saniba? to amma wazai zarga shikam? duk wad'anda suka shigo wajensa a jiya amintattun sane, Sauban, Samha, Harun, Muftahu, duk sun shigo wajensa a jiya, amma Muftahu shine last shigowa, shiru yay yana nazari, can kuma saiya cije lips d'insa ya lumshe idanu yana shafa gurin Dana cijesa.
A haka barci ya kwasheshi.


¡ï¡ï¡ï¡ï



Munubiya tashiga damuwa sosai akan rashin jina a waya, takira number ta yafi sau goma amma switch up, gashi yaa Marwan ya hanata kiran number dana kirasu a ranar, yace wai number Galadima ce bai kamata su damesa ba.
Haka taci kukanta a yinin ranar, saikace mara lafiya haka ta yini, zuwan su Ayusher ne ma yad'an sanyaya ranta har suka janye mata hankali da yawan tunani, a ranar gidan suka yini cir, sunsha hira da labarina, kowacce tana missing d'ina.
Sunce suna son zuwa amma an hanasu, wai gidan danake ba gidan da ake zuwa any how bane ba, babu yanda suka iya haka suka hak'ura.



*********


A gidanmu ma yau sukayi niyyar kawo min akwatinana da abinda ba'a rasaba, amma ankira wayata akashe, wannan yasa Abba yace abarni akaima su fauziyya nasu. ni daga baya idan an sameni akai min nawa d'in.
Duk inda akaje da innaro ake zuwa, kowacce ta taima gidanta kallon kwaf kenan, sotake taga gidan wacce tafi acikin sauran 'yan uwana.
ALLAH ya taimaki munubiya lokacin dasukaje gidanta yaa Marwan yana gidan, hakama su Ayusher.
Fita yayi yasiyo musu abubuwa yakawo, sannan suka zuba musu girkin da sukayi, babu ko kunya suka mik'e kafafu suka ci abinsu, to dama gidan Fauziyya ne kawai suka samu sukaci abinci, su Safara'u kam casukai basu fara girkiba, dan ita haleematu ma ruwa wannan bata basuba, banda innarmu akaje, dayake kowacce idan za'aje gidan 'yarta banda ita ake zuwa.
Zasu taho kuma yaa Marwan yabasu kud'in mota, dukda kuwa a mortar Dady yaa Anas ya kaisu.
Tunda suka dawo gida aka shiga labarin yanda aka iske gidan kowa, nanfa wad'anda gidan 'ya'yansu ba'a samu wani abun kuzo aganiba sai suka fusata, kunsan dai halin jama'ar gidan namu?, wannan Abu saida yakawo rikici, fad'a sosai sukasha abinsu, itadai innarmu k'ala bata ceba, saima ta maida hankalinta ga girkin dare datakeyi, ga innaro sai habaici takeyi, saida gwaggo Safiyya tazo da k'yar ta lalla6ata tafita.
Matan anguwa makwafta kam sun masa kunne suna saurare da kwasar dariya, dan lamarin gidanmu yazama kamar na 'yan wasan kwaikwayo.
Duk tsiyar dasukeyi dady yana gidan yana jinsu, amma ko lek'owa bai yiba, danshi bashida hayaniya ko kad'an, balle daya fahimci abin yashafi 'yan bani na iya d'in gidan ne, dariya kawai yayi yace ALLAH ya k'yauta. kad'anma kenan ai, bakuga komaiba tunda yanzu kuka fara aurarwar, kuma har yanzu da sauran 6ur6ushin amarci ga yaran harsu Aunty khaleesa kam dake cikin watanni na hud'u da auren.


¡ï¡ï¡ï¡ï¡ï


Alhmdllh yanzu kam naji dad'in jikina, dan ko ciwonma banaji, sai shirye-shiyen kayana nakeyi dan yau nakeson tuna masa batun sakina, tun shekaran jiya rabona da ganinsa, harma na d'auka baya gidan sai d'azun da safe Samha take cemin ai tare suka fita itada Uncle Sam da Sauban birnin gayu da asibiti zagayen marasa lafiya, sune har Asibitin mahaukata, tace duk atsorace take ALLAH yasa kartayi mafarki.
Ni dariya ma tabani yanda take bani labarin kamar a firgice take.
Komai nagama had'ashi tsaf, Galadima kawai nake jira, amma abin haushin har kusan 4pm babu labarinsa, gani nayi zan zauna jiran gawon shanu, dan haka na mik'e zuwa sashensa.
Nayi sallama yafi 7 amma babu amsa, sai kawai natura na shiga, a zatona rainin wayonsane da mulkin ya motsa, babu kowa a falon sai wani k'amshi dake tashi na musamman, ko ina kuma need a gyare,, a yanda naga yanayin falon kamar babu kowa a sashen gaskiya, dan komai akashe yake har AC, dawuya kuma yana nan kaga AC n sa a kashe, duk da haka saina d'an zauna ina k'arema ko ina kallo, kai kace yau nafara shigowa, hotunansa da bana gajiya da kallo naketa kallo yanzun ma, idona nacikin zageye-zagaye saina hango wani k'aramin frame na photo, bana ganin mutanen jiki sosai dan haka namik'e tsaye, ga hoton na isa, yana a kusurwar d'akinne ta gabas, saman wani d'an katako da aka k'awata wajen, bayan foton akwai flower babba mai k'yau, sai aka jigina hoton jikin flower d'in.
K'yak'yk'yawan mutum ne ajiki Wanda kallo d'aya zaka masa ka hango tsantsar kamaninsa da Galadima, saikuma mace a gefensa itama masha ALLAH, Galadima kuma yana satar kamanninsa da ita, musamman idonsa ha6arsa dawasu abubuwa, saikuma wadda nake k'yautatama zaton aunty Mimi Ce kusada matar, shima namijin ina tunanin Galadima ne, yana cinyar mutumin, bazai wuce 5 to 6 years ba a picture d'in, Anty Mimi kuma bata wuce 10 ba, sai tsohon ciki ajikin matar, dukda ban saniba sainayi tunanin iyayensane, duk cikin kayan sarauta suke.
Samha ta fad'amin iyayensa suna india, Abbansa bashida lafiya, ban wani tambayeta komaiba, iyanan naji kawai.
Hoton na maida na ijiye ina murmushi, sun birgeni gaskiya sosai, flower d'in nabi da kallo, itama tamin k'au, gawani k'amshi mai dad'i datakeyi, kuma nalura da dare kamar tana wuta haka. Hannuna na kai na ta6a ganye d'aya ajiki, sainaji Ashe ta roba Ce ma, mamaki ya kamani, banyi zaton ta roba bace wlhy, dan tayi k'yau.
Har zan bar wajen, kamar ance na d'aga kaina saman p.o.p d'in ta jikin kusurwar sainaga tamkar CCTV camera, amma bakowa zai iya fahimtar hakanba, domin ansata cikin tsantsar kulawa, gabanane yafad'i, nayi azamar kauda idona tamkar ba ita nake kalloba, saina d'an gyara zaman flower d'in kawai nabar wajen zuciyata na tsitstsinkewa, toshi miye nawani saka CCTV camera a falonsa?, komawa nayi na zauna, zuciyata nawasu tunane-tunane daban.
Sai lokacin tunanin koma bayanan yazomin, abinda Nagano ya hanani lek'a bedroom d'insa, dan nasan zai iya ganin komai ta CCTV camera d'insa.
Sai kawai natashi na fice nakoma nawa d'akin.............??



Hum masu karatu kuna zaton Galadima bai fahimci Muftahu namasa zagon k'asaba kuwa??. kuduba yanda ya shashantar da binciken ya akayi yasha desire tabs a fresh milk?.

To koma dai miye kumuje zuwa, ai masu iya magana kance *Karshen alewa k'asa*???.


Humm ya kuke ganin sakin da Munaya ta nema? Shin zata samu? kokuwa zai bita bazai bayarba??.

Kumuje zuwa dai a page nagaba my guys????¡â???¡â???¡â








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*???[5/1, 4:25 PM] ? M B A ?: *_Typing?_*



*_HASKE WRITERS ASSO...?_*
_(Home of expert and perfect writer's)_




*_?RAINA KAMA......!!?_*
_{Kaga gayya}_




*_Bilyn Abdull ce??_*



??2?7?


...........A gajiye yadawo gidan, daga masarautar su papi yake, dan shine yamasa kiran gaggawa a daren jiya, yau tunda safe ya tafi, dan jirgin 7am yasamu, shine sai yanzu yake dawowa.
Saman kujera ya zube yana furzo iska, sarkin mota daya biyoshi dawasu kaya ya ajiye, yana niyyar fita yajiyo maganar Galadima d'in. tsayawa yayi yajuyo yana kallonsa.
idonsa a rufe yace, ¡°kunnamin AC ¡±.
¡°to ranka ya dad'e¡±. sarkin mota yafad'a yana risinar da kai alamun girmamawa.

Ya dad'e zaune a wajen idonsa a rufe, jin ana kiran salla a masallacin masarautar yasashi mik'ewa da k'yar yanufi bedroom d'insa. makunnar fitilar ya laluba, haske ya gauraye d'akin, komai normal kamar yanda yabarsa. anutse yafara zame sky blue d'in shaddar jikinsa. wanka yashiga, bai 6ata lokaci sosai ba yafito, jikinsa ya goge tsaf yajawo jallabiya fara tas mai dogon hannu yasaka, tamasa k'yau sosai, yad'an fesa turare yafita da hanzari jin za'a tada sallar magrib.

Nagaji da jiransa har zuwa magrib, bansan hawaye sun fara bin kumatuna ba, ahaka nayi sallar magrib, nayi alk'awarin ko yanzu yazo yabani sakina a gidanmu zan kwana, bayan na idar yau ko doguwar addu'a banyiba nadawo kan sofa na zauna tareda rabga tagumi na zubama akwatina idanu.
A wannan yanayin yashigo ya sameni, cikeda mamaki yake bin akwatin gabana da kallo, shi yama manta dawani maganar saki da mukayi.
Ban San ya shigoba saida yad'an bubbuga hanun sofa d'in, firgigit nayi ina kallonsa, bansan murmushi ya su6uce minba da ambatar Alhmdllh.
Idonsa ya janye a kaina ya zauna bakin gadon ¡°lafiya na ganki da trolley?¡±. Yay maganar cikin kuma d'aure face.
Nikam ban damu da yanayin nasaba na rashin walwala, dan narigada na fara sabawa ma da hakan, nad'an murmusa ina ta6e baki, nace ¡°kayan tafiya gida na had'a¡±.
Yi yay tamkar bai jiniba ma, ya zaro wayarsa dake ring yana kallo, a mamakina sai naga yayi murmushin gefen baki tareda saka wayar a kunne. ¡°Amincin ALLAH ya tabbata a gareki my Momma¡±.
¡°tare dakai Muh'd d'ina, yakuke? Ina d'iyata?¡±.
Murmushin yakuma yi tareda satar kallona, yace, ¡°gata a gefena Momma, Yaya jikin Abie?¡±.
¡°jiki Alhmdllh wlhy, yaushe zaku tahone? kun barmu mu kad'ai nida jakadiya¡±.
¡°kai Momma duk kuyangin gidanann kice kuna cikin kad'aici?¡±.
¡°to Muh'd ai d'a dabanne a zuciyar iyaye, musamman ma mu damuka k'agara muga sabuwar d'iyarmu¡±.
Bakinsa yad'an ta6e yana murmushi, ¡°karki damu Momma zaku ganta wataran, amma su aunty Mimi ai inaga gobe zasu taho jirgin darema suka samu¡±.
¡°haka tacemin, amma kufa to? dan banjiKu a lissafin masu tahowaba?¡±.
¡°nima insha ALLAH zan biyo bayansu bada dad'ewa ba Momma, dan nayi missing d'inku, bazan iya gama hutuna ananba gaskiya¡±.
¡°ita kuma d'iyar tawafa?¡±.
¡°nan zan barta mana Momma, duk k'arshen wata zanzo na ganta kamar yanda na saba¡±.
¡°lallaikam, to yanzu dai saika nemi tickets kafin Safiya, gobe idan ALLAH ya kaimu kutaho dasu Haneefa domin takawa yaga d'iyarsa, idan kun k'are hutun tare anan zuwa k'arshen watan saika maidatan¡±.
Tunda tafara maganar gabansa yafad'i, yawani marairaice murya tamkar yana a gabanta, ¡°please Momma wannan shawaran kumafa? dan ALLAH karkice haka ba yanzu ba sai nan gabafa zatazo?¡±.
¡°to nidai nagama magana Muh'd, za6i kuma yarage naka ai, bani ita mu gaisa time d'in gogema takawa jiki yayi zan shige¡±.
Ransa a 6ace yamik'omin wayar, banyi magana ba na kar6a dan naji yana Momma ai nasan mahaifiyarsa ce. gakuma yanda yaketa kwantar da murya irinna ladabi da shagwa6a.
Cikin nutsuwa da tsantsar girmamawa na gaisheta, daga can ta amsa min cikeda kulawa, bayanin daya firgitani naji tanamin, na waro idanu waje cikin tashin hankali, amma sai na kasa musa mata, na shiga amsawa da to cikin rawar murya.
Duk da AC d'akin zufa nakeyi, nida ke shirin fecewa gidanmu yau da takardar saki amma shine ake rok'ona nayi shiri gobe zamuje India, na taresu ni Munaya, ban kuma fahimtar dukkan sauran zantukan nataba, sai maganar k'arshe naji datace nabashi wayar.
Murya na rawa namata godiya da Addu'ar samun lafiya ga abban su Galadima, taji dad'i sosai kuwa, dan har sautin murmushinta ina jiyowa, hannuna har rawa yakeyi namik'a masa wayar, yana kwance idonsa a lumshe, damuwace a fuskasa karara, muryata na rawa nace, ¡°gashi tace abaka¡±.
Batare da yabud'e idonba ya kar6a, a kunne yasaka wayar, cikin kwantar da murya yace ¡°haba sweet Momma na a sassautamin mana¡±.
Murmushi kawai tayi daga can, tace ¡°ai iya sassaucin dazan maka kenan Muh'd, gobe idan ALLAH ya kaimu ka kaita gidansu tama iyayenta sallama da 'yar uwar tagwaicinta¡±.
¡°amma Momma..... ¡±
¡°kasan banason maida magana baya ko? kayi yanda nace kawai¡±.
Shiru yay bai iya cewa komaiba harta yanke wayar gaba d'aya.

Ransa a6ace ya tashi zaune, wayar Harun ya kira, yana d'agawa ko gaisuwar bai amsaba yace, ¡°Harun inason tickets guda biyu na India¡±.
¡°lafiya dai ko Galadima?¡±.
¡°Normal¡± kawai yace ya yanke wayar.
Harun ya girgiza kai, dan yaji alamar ransa a 6ace yake.
Mintuna basu wuce 5 ba yakirashi yace an samu naka, sai dai ita kuma batada passport ai, dolene da safe sai Anje anyo, amma na darene jirgin.
¡°yayi¡± kawai yace nanma yay shiru.
Harun nason masa wata tambayar amma babu dama, sai kawai ya yanke wayar.

Nidai ina dafe da kai abin duniya dukya isheni, shikenan an ruguza min plan d'ina.
Tashi yay yafice batareda ya kuma ko kallona ba, ban damuba, dan nima tawa ta isheni, yana fita hawayen bak'in ciki suka zubomin a fuska, ban samu damar sharewa ba na zame na kwanta a sofar.

Yana fita sashen mai martaba yaje, bayan jakadiya tamasa iso yashiga, gaidashi yayi cikin saisaita yanayinsa kafin yamasa bayanin zai koma India gobe, saboda kiran gaggawa daya samu daga doctors d'in Abie.
Fatan alkairi mai martaba yamasa, kafin ya tambayesa maganar nikuma fa.
Kansa a k'asa yace, ¡°ranka ya dad'e da ita zamu tafi, idan komai ya dai-daita saina maidota¡±.
¡°to shine nan, hakan yayi ai¡± nasiha sosai mai martaba yayi masa, tareda jan doguwar addu'a wa jikin Abie, ya dad'e a can sannan yafito.



¡ï¡ï¡ï¡ï



d'ayar wayarsa daya manta a kan gadona tashiga ring, ban d'auka ba harta tsinke, aka kuma kira ta yanke, saga nan ba'a sake kiranba, tunanin kiran Munubiya ne ya zomin, Dan haka na tashi zaune ina share hawayen fuskata na d'auki wayar nasaka number, Dan na haddace ta akai, harta tsinke bata d'agaba, saida na sake kira sannan tad'aga.
Acikin rashin sanin wanene tayi sallama a d'arare, amsawa nayi ina jan ajiyar zuciya, cikeda d'oki tace, ¡°Sweetheart kece? ykk?¡±.
¡°lafiya lau munu...., ke kad'aice a gidan dan ALLAH¡±.
¡°eh nikad'aice yaa marwan bai dawo masallaciba. miya farune?¡±.
¡°magana zamuyi Munu.... amma kiyi hak'uri da 6oye miki da nayi tun farkon matsalar, banason ki tashi hankalinkine shiyyasa¡± tun daga farkon maganar aurenmu da Galadima a randa suka saceni har

30 / 36