Author : Bilyn Abdull Category : Romance
na matso gareta, banyi musuba na matsa, hannuna takama tana murmushi, ¡°yaya bak'unta gimbiyarmu?¡±.
Muryata a kunyace na amsa da ¡°Alhmdllh ranki ya dad'e¡±.
Murmushi sarki dake kallonmu yayi, ya maida kallonsa ga Galadima da shima idonsa na kanmu. ¡°yarona babu dai wata matsala ko? ¡±.
¡°Alhmdllh Abba babu komai¡±.
¡°to Alhmdllh ai haka muke fata mu dama, ALLAH yayi muku albarka, yabamu zaman lafiya na har abada da zuri'a d'ayyiba, wadda musulunci da Muslims zasu alfahari da ita............¡± Nan yashiga mana nasiha mai ratsa jiki da 6argo, har lokacin hannuna na rik'e ga matar sarki, wadda k'amshin turarenta kemin dad'i sosai a hanci.
Mun dad'e anan, dan sai kusan 9pm muka fito, tare da gagarumar k'yauta ta mukullin mota da sarki ya bani, matar kuma tace zata aikomin da tata insha ALLAH.
daga ni har Galadima munyi godiya sannan muka fito, sai juya keys d'in nake ahannu inajin wani makahon dad'i, wai nice da mota har biyu, yanzu Abbana da Dady sun samu kenan, saura baba k'arami, dan nikam babu abinda zanyi dasu, iyayena zan baiwa.
Daga nan munje 6angaren sauran Matan sarki, sai kuma na k'annen babansu Galadima d'in, mune har sashen da aunty Mimi ta sauka,, k'yaututtuka dai nasamesu sosai, harda masu sark'ok'i da sauransu, mun dad'e annan fiyema da ko ina, dan har 12 muna can, sunata hira tsakaninsu, danni dai ban iya cewa komai, sai sun sakoni ne nakanyi murmushi, musamman Sauban sarkin tsokana da Samha sarkin surutu, galadima kam ba komai yake tankasuba, shida aunty Mimi ke maganarsu jefi-jefi, khaleel ma sanda mukaje yayi barci. saida aunty Mimi tace mutashi muje sannan muka dawo namu 6angaren.
Sai da yarakani har d'akina sannan ya juya yafita batareda yace uffanba.
Binsa kawai nayi da kallo ina sauke ajiyar zuciya. Ni ban ta6a ganin murd'ad'd'en mutum irin wannan mutuminan ba, wlhy miskili yafishi dad'in zama, danshi na lura ba muskili baneba, tsabar jin kai ne kwai ke d'awainiya dashi.
¡ï¡ï¡ï
Shikam har yayi shirin barci yagama yay shafa'i da wutiri maganar Mama Fulani na caccakar masa rai, ya murmusa kawai saboda takaici, ya zauna saman kujera d'akin, Syringe d'in d'azu ya d'akko da k'yallen yana jujjuyawa a hannu, wani sashe na zuciyarsa na cewa kawai yayi dabaran Aunty Mimi, wata kuma nacewa kar yayi tunda ba addini baneba, koma Dan ya k'ular da zuciyar mama Fulani, to amma kuma ita yarinyar za ana kallonta wani iri ai kuma a masarautar, harma sudunga tunanin ta zubar da mutuncinta a wajene kamar yanda mama Fulani tace, gara yayi kawai dabarar Dan fatansa harsu rabu baya son wani abu na family d'insa ya shafeta. Wannan shawarar da zuciyarsa ta yanke masa yasashi jawo charger ya d'aure hannunsa, jijiya ta bayyana, ya rintse idonsa yayinda ya tsira allurar, cikin cije lips yaja jinin kad'an sannan ya zare ya danne da auduga yanajan tsaki, charger d'in ya kwance yay wurgi da ita saikace itace tamasa laifin??.
d'aukar gyallen yayi ya yamutsashi da hannu duk yayi Squeezing sosai sannan ya matse jinin ajikinsa yad'an yayyarfa bayan yazuba shi awaje d'aya da yawa. sai wani yamutse fuska yakeyi tamkar yaga kashi, kokuma jinin ba daga jikinsa yafito ba. ya ajiyeshi gefe sannan yamik'e yafito, a duzben d'in falo ya saka syringe d'in da kad'ar yakoma ciki, saida ya wanke hannunsa sannan ya haye gadonsa ya kwanta yana wani 6ata rai.
Nima can bayan na kammala hidimata kwanciyar nayi cikeda kewar 'Yar uwata, yauma nadad'e banyi barciba, sai daga baya ya saceni.
Washe gari bansan miya faruba naji busar algaita na tashi a k'ofar sashenmu, yayinda aketa cillara gud'e-gud'e dake tashi, ina niyar fitowa domin ganin abinda ke faruwa Galadima yashigo da d'an hanzarinsa, hannunsa d'auke da k'aramin tire da kofin shayi akai. ¡°hau gado ki kwanta¡± yay maganar yana ajiye kofin a table d'in gaban gadon.
¡°miya farune?¡±. na tambaya cikin binsa da kallo.
¡°ok zauna tambayata har su shigo ciki, oya malama ki hau¡±.
Nidai duk mamaki ya isheni, kamar wadda aka make haka na hau gadon na zauna, kallon face d'ina yayi yaga babu wata alamar dawani zaiga nashiga wani hali, dolene ya canja yanayina kenan idan har yanason ya tsira daga kwakwaf d'in wannan shirmen kafin su shigo.
Kawai sainaga ya hayo gadon shima, kuma kaina yayo gadan-gadan, na bud'e baki da nufin tambayarsa dalili, kawai naji bakinsa cikin nawa. tsorone ya kamani da fargaba, sai kawai nahau dukan bayansa da k'ok'arin turesa, haka dama yakeso, yazam nayi yunk'urin kwatar kaina har nad'an jigata yanda kowa zai d'auka wahalar daren jiyanne. kuma rikicewa nayi saboda wasa daya fara da wasu 6angare na jikina,, so kawai nake na kwaci kaina awajensa, tun ina iya yunk'urin turesa harna kasa, dama nima nasan ganganne na iya da wannan basamuden mutumin?? (munaya tafad'a ba niba????¡â).
Sai da yaga nayi lakwas ina hawayene kawai na daina tureshi sannan ya d'agani yana sauke numfashi, nikam saina kuma fashewa da sabon kuka, (kai jama'a Galadima akwai bariki??) yanajin takun isowar su Fulani da kirarin kuyanginta sai yayi saurin jan bargo ya rufamin zuwa cikina, yawani kwantar da murya yana fad'in ¡°please my jannat kiyi hak'uri hakanan, kukan ya isa kinji, tun daren jiya kike Abu d'aya, haka ai kowacce mace tayi sannan tazama uwa, ALLAH dai yayi miki albarka, kifad'amin wace kauta kikeso saboda tukuycin budurcinki daki kawomin har gidana¡±.
Idanu nad'an zaro saboda tsorata, mi wannan gayen yake nufi? wai ko dai Galadima yana shaye-shayene ban saniba, abunda yazo yamin daban sannan yakuma d'akkomin wani zancen daban.........
Gyaran muryar da akayice yasamu waigawa ni da shi, kakarsa ce ta jiya a atsaye dawasu mutane biyu, gabana ya fad'i da matsananciyar kunyar su, Dan inada tabbacin sunji ko sunga abinda yamin, ko dai saboda su yake wannan abun? da sauri naja bargon na rufe fuskata saboda kunya.
Yayinda shikuma ya kalli mama Fulani yana wani susar gefen wuya kamar gaske, ¡°o ranki ya dad'e kune? bar kanku da zuwa Ku shigo mana, saima Ku tayani lallashi ai¡±.
Matannan buyu gud'a suka callara a tare, yayinda mama Fulani ta kafama Galadima idanu, alamun tuhuma. kansa ya d'ago shima suka kalli juna ya sakar mata wani lallausan murmushi, kafin ya janye idonsa ya maida a kaina danake k'udundune cikin bargo.
d'aya cikin matan ta rissinar da kanta, cikin girmamawa tace, ¡°Ranka ya dad'e ko zaka bamu waje mu k'imtsa ta?¡±.
Kallonta yayi, fuskarsa d'auke da murmushin Dana sakama suna na rainin hankali, cike da k'asaitarsa yace, ¡°na hutasheku jakadiya, danni tun a daren jiya na gyara matata¡±.
Mama Fulani dake kallonsa a zuciyarta tace amma dai yaronnan d'an rainin wayone wlhy, gaba d'aya ya shirya komansa dai-dai ta yanda babu wanda koda ta k'aryata zai yarda da ita, Dan tabbas tasan duk k'arya yakeyi gameda wannan k'yallen, gashi lungu da sak'o na gidan angama nuna k'yallen, saboda ma ya raina mata wayo ba 6angarenta aka kaiba, sashen matan sarki ya aika da k'yallen, zancennan ma da akeyi ita bataga k'yallen ba har yanzun, Dan ba'a kai mataba, kowa ya d'auka daga sashenta ya fito, tunda ita ake fara kaimawa tagani sannan Matan sarki.
Had'a ido sukayi da Galadima, bakin ya ta6e mata, tareda d'age gira sannan yasaki murmushin Dake k'ular da mama Fulani aduk lokacin da yayisa.
Ta had'iye wani yawun bak'in ciki tareda kauda kanta gefe, su jakadiya kam tuni sun yi nisa wajen kar6o k'yaututtukan da kuyangin kowane sashe ke kawowa daga Matan gidan da iyaye, duk abama Munaya.
Dole mama Fulani ta k'arasa gaban gadon tasakama munaya turare da Sanya mata albarka tamkar yanda al'adar gidan ta tanadar, sannan takama hannunta ta saka mata bangles na goal masu k'yau da d'aukar idanu. Ta shafa kan munaya tana murmushin yak'e. sannan tadawo gaban Galadima shima takama hannunsa ta d'aura masa agogon Azurfa mai k'yau.
Salute nata yayi yana fad'in thanks my sweet Granny ¡±.
Uffan batace masaba tajuya tafice daga d'akin. yayinda su jakadiya suka take mata baya.
Suna fita ya sauke ajiyar zuciya tareda dafe kansa yana jan tsaki, nima kaina na bud'e amma nakasa tashi saboda kunyarsa data dabaibayeni.
Kusan mintuna 5 muna a haka, ni inata hawaye da jamasa ALLAH ya isa a zuciya, ga la66ana sai zugi sukemin saboda Sumbata d'inma na mugunta yamin. shikam yana dafe da kansa har yanzun yana sauraren kukan danake rairawa.
Zamansa ya gyara ya juyo yana kallona, fuskarsa a matuk'ar d'aure yace ¡°tashi ki zauna muyi magana¡±.
Yanda yay maganar yasani tashi zaune batare da na musaba.
Yad'an kalleni ya janye idonsa sannan ya mik'amin Handkerchief d'insa daketa tashin k'amshi alamar na goge hawayena. Kamar bazan kar6aba dai saikuma na kar6a na goge fuskata.
Nanma shiru mukai nawasu mintuna da basufi 2 ba, nakula magana yakeson min amma yanata mulmulata a zuciya saboda jin kai, kuma d'agowa yayi ya kalleni saikuma yay gyaran murya kad'an, ¡°em kiyi hak'uri, bamuda wata mafita sai wannan, munada wata kidahumar al'adane a masarautarnan, dolene randa katare da matarka sai kowa yasani ta hanyar ganin jini ajikin k'yallen da aka shinfid'a muku a gado. mukuma namu auren yasha banban dana saura, banida niyyar zalintarki na maidaki bazawara sannan na sakeki, inason idan mun rabu duk mijin daya aureki yasameki cikin mutuncinki, shiyyasa bazan aikata abinda suke buk'atar ba. ajiya anta surutu saboda bamu bada wannan shaidar ba, shiyyasa a Daren jiya nayi wata dabarar daban, fitowata kenan daga wanka najiyo busar algaita da gud'a alamun k'yallen yagama zaga masarautar, shiyyasa nayi azamar d'akko coffee d'in da aka had'amin zansha nanufo nan dashi, Dan Muftahu yakirani ya sanarmin zafa azo har sashena domin sanyamiki albarka da k'yaututtuka dakika samu saboda kin kawo mutuncinki, yanayin dana ganki nasan zasu gane shirina, shine dalilin yimiki wannan abun dan fidda zuciyarsu daga zargi, karki d'auka nayi mikine da niyya koki kalleni cikin mutane masu sa6a alk'awari¡±.
yana gama fad'a yamik'e zai yafice, nidai kaina ak'asa jinake tamkar namasa masifa amma kwarjininsa ya hanani, saida yaje bakin k'ofar zai fita sannan ya kuma furta ¡°kiyi hak'uri, Sameer baya zalunci¡±. ya ida ficewarsa kawai.
Duk da na yarda da abinda ya fad'a, hakan bai hanani rushewa da sabon kuka ba, nace mugu kawai ALLAH ya isana wlhy, na shafa la66ana da da haryanzu zugi sukemin suda k'irjina wlhy, dan tsabar mugunta shine yama tsaya iya bakin amma harda wani wajen, ALLAH ya isana nidai.
??kujifa, mutum da sadakinsa Munaya ke kiransa da mugu da jamasa ALLAH ya isa?, yau munga auren Contract readers????¡â???¡â.
Tunda abunnan yafaru bamu sake had'uwa da shiba a ranar da yinin washe gari , kullum dai Samha kan kawomin abinci tareda kuyangin Aunty Mimi.
¡ï¡ï¡ï¡ï
Bayan sallar isha'i damuwa da rashin jin innarmu da Munubiya ya gallabi zuciyata, jinai bazan iya daurewa ba, dan haka na yanke shawarar zuwa na rok'esa ya aramin charger kona samu nayi charge wayata, duk da ma banida isashen credit aciki. na d'au turare nad'an fesa kad'an sannan nazura dogon hijjabi nafita zuciyata na d'ar-d'ar.
Na dad'e k'ofar falon tsaye ina tunanin yanda zan shiga, daurewa nayi nai Knocking, wata murya naji ta amsa sa6anin tasa, akace ¡°waye?¡±.
Saida gabana yad'an fad'i, cikin rumtse idanu nace ¡°nice¡±.
Galadima dake kwance cikin kujera idonsa a lumshe yana sauraren Muftahu yabud'e idonsa da sauri.
Shikam muftahu cewa yayi ¡°bismillah ranki ya dad'e, ki shigo¡±.
Na tura k'ofar ahankali na shigo da wata sabuwar sallamar, Muftahu ne kawai ya amsa cikin washe baki, (yayinda k'asan zuciyarsa ke wata iriyar murna ganin shirinsa zai tafi dai-dai kenan). Galadima kam idanu kawai ya zubamin cikeda mamakin miya kawoni?.
Gaisawa mukayi da Muftahu cikin mutunci. saiya mik'e yana fad'in ¡°ranka ya dad'e nikam na wuce, zuwa Safiya zamu k'arasa maganar kawai¡±.
Kansa kawai ya d'agama Muftahu n.
Muftahu ya kalleni yace ¡°gimbiya mu kwana lafiya¡±.
Na murmusa sannan na amsa da ¡°to ALLAH ya tashemu lafiya¡±.
Koda Muftahu yafita sainayi tsaye nakasa magana ganin ya zubamin idanu, ganin banida niyyar magana saiya nunamin kujera alamar na zauna. shima yana tashi zaune sosai.
Ban musaba na zauna.
¡°miya faru?¡±. ¡®yafad'a yana zuba Hollandia fresh milk a glass cup d'in gabansa¡±.
d'agowa nayi nad'an kallesa, dai-dai yasaka kofin a bakinsa zai sha, janye idanuna nayi ina kuma had'e fuska. aransa yace kai wannan yarinya akwai jan ajin tsiya.
Saida naja wasu seconds sannan nace charger zaka aramin please, nabaro tawa a gida, gashi inason waya da munubiya da innarmu.
Crossing kafarsa yayi yana cigaba da shan free milk nashi tamkar bai jini ba, harna fidda tsammanin zai tanka min, sainaji yace, ¡°ina wayar?¡±. yay maganar da mik'omin hannu alamar na bashi
Mik'ewa nayi na kai masa wayar ina tunanin mizaiyi da ita?.
Koda ya kar6a saiya mik'omin cup d'in hannunsa bayan yak'ara fresh milk d'in a ciki.
Na girgiza masa kai alamar na k'oshi.
wani kallo ya watsamin daya sani kar6ar dole. nadawo mazaunina na zauna, inata rik'on cup d'in amma nakasa sha, haka kawai naji hankalina bai kwanta da fresh milk d'in ba, bawai zargin yazuba wani Abu nakeba, haka kawai dai banjin sha.
Shikuma ya basar dani yanata juya wayar kawai a hannusa, basan miyake kalloba ajikinta.
Kallona yayi yace, ¡°kin rik'e Number su?¡±.
¡°eh¡± nafad'a batareda na kallesa ba.
Wayarsa ya d'auka guda d'aya ya had'omin da tawan ya mik'omin, ¡°kije kuyi wayar kawai, da safe sai a nemo miki charger d'in¡±.
Na tashi naje na kar6o tareda cewa ¡°nagode¡± najuya nafice da cup d'in fresh milk d'in a hannu na.
Bina yayi da kallo harna fice, ya sauke ajiyar zuciyata kafin ya cije lips nashi domin jin mararsa tad'an rik'e masa kad'an.
Koda naje d'akina saina kasa ajiye fresh milk d'in, haka kawai naji kuma sha'awar nasha, nako d'aga cup d'in na shanye tas sannan na zauna ina juya wayar tasa datamin k'yau, saina tuno wayarsa daya barmin ranar idi, na ta6e bakina kawai nafara saka number innarmu..............??
Hummm mi zai biyo baya bayan shan fresh milk kuma?. da zuwan muftahu?.?
Wannan amsar sai ranar Monday?. naso yimuku wannan weekend d'in amma munada biki gsky.???
*_hhhh naji k'orafinku sister's, ammafa ko pages biyu nakeyi ba isarku zaiyiba?, wlhy bama nida time d'in yin typing 2pages a rana, saboda inada aure, akwai nauye-nauye a kaina nima, masu kuma so nagama kafin azumi suma ina basu hak'uri, bazai yuwu nagama kafin azuminba, dan azumin kad'an ya rage, kuma banason datse labarin nan kamar yanda nayi a SIYASA KO KABILANCI, zanbi a hankali na gama, wlhy nafiku son nagama nima Na huta, Dan dana fara buk zai fara cizona a zuciya nima, so kawai nake naga nagama?, karku manta ko tarihin masarautar su Galadima sameer har yanzu bamu saniba, Dan haka zamuyi, iya inda muka tsaya saimu cigaba bayan salla idan ALLAH ya kaimu da rai da lafiya, Dan kamar yaune ai.???._*
Ngd sosai da soyayyar dakuke nunama buk d'innan, ina sonku nima har cikin raina, ina fata zaku fahimceni???.
???????
???¡â
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu???_*
[4/30, 7:46 PM] Sis Naja Atuh: *_Typing?_*
*_HASKE WRITERS ASSO...?_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_?RAINA KAMA......!!?_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce??_*
??2?5?
..........Bugu biyu ta d'auka, jinayi tamkar anmin bishara da aljanna dan dad'i, lokacin danaji muryar innarmu tayi sallama cikin sanyinta sai kawai na Sanya mata kuka.
Ita kuma daga can batasan wayeba, a sanyaye tace ¡°baiwar ALLAH ko bawan ALLAH lafiya kuwa?¡±.
Murmushi nayi, gakuma hawaye na kwaranya, nace ¡°innarmu nice fa¡±.
Cikeda d'okantuwa tace, ¡°Munaya kece? ya kuke?¡±.
Murmushi nayi mai sauti, nace ¡°innarmu ina yini? inasu Aryaan? Wlhy ina missing