Author : Bilyn Abdull Category : Romance
yabi wayar da kallo yana mamakin Galadima da halinsa, kiransa yakuma yi shi dan bai fahimci inda maganar tasa ta dosaba. sai dai harta yanke bai d'aukaba, yana k'ok'arin sake kira yaji ana Knocking d'in k'ofar.
Amsawa yay da yes tareda izinin shigowa.
Wani dogari ya bud'ema Galadima k'ofar yashiga, da hanzari Dr Jalal yamik'e yana murmushi da masa welcome.
Hannu kawai ya iya d'aga masa ya zauna kujerar gaban decks d'in.
Shima Dr jalal saiya zauna, ¡°ranka ya dad'e lafiya dai ko?¡±.
Saida yaja wasu Seconds sannan yafara ma Dr jalal bayanin damuwarsa, ya sanar masa mararsa namasa ciwo tun jiya, kuma ada bata masa kamar hakan.
Shiru Dr jalal yay yana nazarin maganar tasa, saida yakai aya sannan yace ¡°ranka yadad'e kokasha pills ne?¡±.
Kallonsa Galadima yayi, ¡°pills kuma? wane irin tambaya kakemin haka?¡±.
¡°afuwa ranka ya dad'e, matsalar taka tayi kama da wanda yasha tablet ne, mikaci na k'arshe jiya?¡±.
cikeda nazarin maganar Jalal yace ¡°fresh milk ne last abinda nasha jiya da daddare¡±.
¡°to amma bayan shi kafara jin matsalar?¡±.
¡°kusan haka gaskiya¡±.
Dr jalal dai shiru yayi, dan ya tabbatar wannan aikin desire tablets ne, amma koya fad'a dawuya Galadima ya yarda, sai kawai yashare ya had'a masa drugs da injection yamasa, yace yad'an kwanta na kamar 20 minutes a office d'in. bai musa masaba ya shiga inda jalal kan huta idan yaso, saiya kwanta kawai, dan shima bazai iya tafiyarba, d'akin ma da taimakon jalal d'in yashigo.
Ni bansan hidimar da akeyiba, dan rabona dashi tun bayan munyi maganar saki, abinci ma tun Wanda doctor tabanine a cikina, sai kusan 8 Samha takawo min kayan fruits dawani Abu mai dad'i daban san mineneba?.
Ta zauna mund'anyi hira kafin tafice. a bakin ta nakejin wai jibi Friday zasu koma India.
Na danci abinda takawo nasha magani nayi kwanciyata cikeda kewar 'Yar uwata dana kanyi akowanne dare.
Galadima kam bai dawo ba sai kusan 1pm, yana shigowa sashensa yawuce yay shirin barci ya kwanta, Alhmdllh zuwa yanzu yaji k'arfin jikinsa, sai dai zuciyarsa nata cud'a masa tunanin ina yasamo pills? dan shima yafara yarda da maganar jalal, musamman idan ya tuno furucin Munaya na d'azun da safe.
To kenan wani ya zuba masa bai saniba? to amma wazai zarga shikam? duk wad'anda suka shigo wajensa a jiya amintattun sane, Sauban, Samha, Harun, Muftahu, duk sun shigo wajensa a jiya, amma Muftahu shine last shigowa, shiru yay yana nazari, can kuma saiya cije lips d'insa ya lumshe idanu yana shafa gurin Dana cijesa.
A haka barci ya kwasheshi.
¡ï¡ï¡ï¡ï
Munubiya tashiga damuwa sosai akan rashin jina a waya, takira number ta yafi sau goma amma switch up, gashi yaa Marwan ya hanata kiran number dana kirasu a ranar, yace wai number Galadima ce bai kamata su damesa ba.
Haka taci kukanta a yinin ranar, saikace mara lafiya haka ta yini, zuwan su Ayusher ne ma yad'an sanyaya ranta har suka janye mata hankali da yawan tunani, a ranar gidan suka yini cir, sunsha hira da labarina, kowacce tana missing d'ina.
Sunce suna son zuwa amma an hanasu, wai gidan danake ba gidan da ake zuwa any how bane ba, babu yanda suka iya haka suka hak'ura.
*********
A gidanmu ma yau sukayi niyyar kawo min akwatinana da abinda ba'a rasaba, amma ankira wayata akashe, wannan yasa Abba yace abarni akaima su fauziyya nasu. ni daga baya idan an sameni akai min nawa d'in.
Duk inda akaje da innaro ake zuwa, kowacce ta taima gidanta kallon kwaf kenan, sotake taga gidan wacce tafi acikin sauran 'yan uwana.
ALLAH ya taimaki munubiya lokacin dasukaje gidanta yaa Marwan yana gidan, hakama su Ayusher.
Fita yayi yasiyo musu abubuwa yakawo, sannan suka zuba musu girkin da sukayi, babu ko kunya suka mik'e kafafu suka ci abinsu, to dama gidan Fauziyya ne kawai suka samu sukaci abinci, su Safara'u kam casukai basu fara girkiba, dan ita haleematu ma ruwa wannan bata basuba, banda innarmu akaje, dayake kowacce idan za'aje gidan 'yarta banda ita ake zuwa.
Zasu taho kuma yaa Marwan yabasu kud'in mota, dukda kuwa a mortar Dady yaa Anas ya kaisu.
Tunda suka dawo gida aka shiga labarin yanda aka iske gidan kowa, nanfa wad'anda gidan 'ya'yansu ba'a samu wani abun kuzo aganiba sai suka fusata, kunsan dai halin jama'ar gidan namu?, wannan Abu saida yakawo rikici, fad'a sosai sukasha abinsu, itadai innarmu k'ala bata ceba, saima ta maida hankalinta ga girkin dare datakeyi, ga innaro sai habaici takeyi, saida gwaggo Safiyya tazo da k'yar ta lalla6ata tafita.
Matan anguwa makwafta kam sun masa kunne suna saurare da kwasar dariya, dan lamarin gidanmu yazama kamar na 'yan wasan kwaikwayo.
Duk tsiyar dasukeyi dady yana gidan yana jinsu, amma ko lek'owa bai yiba, danshi bashida hayaniya ko kad'an, balle daya fahimci abin yashafi 'yan bani na iya d'in gidan ne, dariya kawai yayi yace ALLAH ya k'yauta. kad'anma kenan ai, bakuga komaiba tunda yanzu kuka fara aurarwar, kuma har yanzu da sauran 6ur6ushin amarci ga yaran harsu Aunty khaleesa kam dake cikin watanni na hud'u da auren.
¡ï¡ï¡ï¡ï¡ï
Alhmdllh yanzu kam naji dad'in jikina, dan ko ciwonma banaji, sai shirye-shiyen kayana nakeyi dan yau nakeson tuna masa batun sakina, tun shekaran jiya rabona da ganinsa, harma na d'auka baya gidan sai d'azun da safe Samha take cemin ai tare suka fita itada Uncle Sam da Sauban birnin gayu da asibiti zagayen marasa lafiya, sune har Asibitin mahaukata, tace duk atsorace take ALLAH yasa kartayi mafarki.
Ni dariya ma tabani yanda take bani labarin kamar a firgice take.
Komai nagama had'ashi tsaf, Galadima kawai nake jira, amma abin haushin har kusan 4pm babu labarinsa, gani nayi zan zauna jiran gawon shanu, dan haka na mik'e zuwa sashensa.
Nayi sallama yafi 7 amma babu amsa, sai kawai natura na shiga, a zatona rainin wayonsane da mulkin ya motsa, babu kowa a falon sai wani k'amshi dake tashi na musamman, ko ina kuma need a gyare,, a yanda naga yanayin falon kamar babu kowa a sashen gaskiya, dan komai akashe yake har AC, dawuya kuma yana nan kaga AC n sa a kashe, duk da haka saina d'an zauna ina k'arema ko ina kallo, kai kace yau nafara shigowa, hotunansa da bana gajiya da kallo naketa kallo yanzun ma, idona nacikin zageye-zagaye saina hango wani k'aramin frame na photo, bana ganin mutanen jiki sosai dan haka namik'e tsaye, ga hoton na isa, yana a kusurwar d'akinne ta gabas, saman wani d'an katako da aka k'awata wajen, bayan foton akwai flower babba mai k'yau, sai aka jigina hoton jikin flower d'in.
K'yak'yk'yawan mutum ne ajiki Wanda kallo d'aya zaka masa ka hango tsantsar kamaninsa da Galadima, saikuma mace a gefensa itama masha ALLAH, Galadima kuma yana satar kamanninsa da ita, musamman idonsa ha6arsa dawasu abubuwa, saikuma wadda nake k'yautatama zaton aunty Mimi Ce kusada matar, shima namijin ina tunanin Galadima ne, yana cinyar mutumin, bazai wuce 5 to 6 years ba a picture d'in, Anty Mimi kuma bata wuce 10 ba, sai tsohon ciki ajikin matar, dukda ban saniba sainayi tunanin iyayensane, duk cikin kayan sarauta suke.
Samha ta fad'amin iyayensa suna india, Abbansa bashida lafiya, ban wani tambayeta komaiba, iyanan naji kawai.
Hoton na maida na ijiye ina murmushi, sun birgeni gaskiya sosai, flower d'in nabi da kallo, itama tamin k'au, gawani k'amshi mai dad'i datakeyi, kuma nalura da dare kamar tana wuta haka. Hannuna na kai na ta6a ganye d'aya ajiki, sainaji Ashe ta roba Ce ma, mamaki ya kamani, banyi zaton ta roba bace wlhy, dan tayi k'yau.
Har zan bar wajen, kamar ance na d'aga kaina saman p.o.p d'in ta jikin kusurwar sainaga tamkar CCTV camera, amma bakowa zai iya fahimtar hakanba, domin ansata cikin tsantsar kulawa, gabanane yafad'i, nayi azamar kauda idona tamkar ba ita nake kalloba, saina d'an gyara zaman flower d'in kawai nabar wajen zuciyata na tsitstsinkewa, toshi miye nawani saka CCTV camera a falonsa?, komawa nayi na zauna, zuciyata nawasu tunane-tunane daban.
Sai lokacin tunanin koma bayanan yazomin, abinda Nagano ya hanani lek'a bedroom d'insa, dan nasan zai iya ganin komai ta CCTV camera d'insa.
Sai kawai natashi na fice nakoma nawa d'akin.............??
Hum masu karatu kuna zaton Galadima bai fahimci Muftahu namasa zagon k'asaba kuwa??. kuduba yanda ya shashantar da binciken ya akayi yasha desire tabs a fresh milk?.
To koma dai miye kumuje zuwa, ai masu iya magana kance *Karshen alewa k'asa*???.
Humm ya kuke ganin sakin da Munaya ta nema? Shin zata samu? kokuwa zai bita bazai bayarba??.
Kumuje zuwa dai a page nagaba my guys????¡â???¡â???¡â
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*???
[4/30, 7:46 PM] Sis Naja Atuh: *_Typing?_*
*_HASKE WRITERS ASSO...?_*
_(Home of expert and perfect writer's)_
*_?RAINA KAMA......!!?_*
_{Kaga gayya}_
*_Bilyn Abdull ce??_*
??2?4?
............ Tunda muka fito masu hidimar sashensa suketa zubewa suna gaishemu, hannu kawai yake d'aga musu, nikam ma ba amsawa nakeba.
Wata mota aka bud'e mana muka shiga, mamaki ya kamani, shin ba'a cikin gidan bane?. banida mai bani amsa dan haka nayi gum.
Duk da darene muna ganin bayi dake yawo tsilli-tsilli, ga ko'ina kwanyar da haske, a k'ofar wani sashi ya tsaya da motar.
Kallona ya juyo yayi, cikin muryar nan tasa ta k'asaita yace, ¡°basai na fad'a mikiba, kinsan yanda ya kamata ace kowa ya ganmu, nan sashen kakarmu ne mai suna mama Fulani ¡±.
Kai na na gyad'a masa, sannan muka fito saboda anbud'e mana dama tuni.
Tunda muka fito ake kwasar gaisuwa, nikam sai binsu da kallon tausayi nakeyi, su shikenan a bautama wasu zasu k'are, basu da wani 'yancin Kansu......
Tunanina ya kakare, lokacin danaji tattausan hannunsa cikin nawa, kowannen mu saida yaji shock, nad'an rumtse idanuna, yayinda shikuma ya cije lips.
Saida aka mana iso sannan muka shiga. kata faren falone na alfarma, iyakar k'yau da tsaruwa yayi, saikace ba falon tsohuwa ba, ga k'amshin turare na musamman na tashi,.
Bafulatanar tsohuwace mai jikin fulanin asali, dankuwa akwai k'yawu iya k'yawu, tabbas wannan a zamanin k'uruciya anyi asalin k'yak'yk'awa, sai dai gajarta tamata tsiya kam??.
A kishin gid'e take, yayinda hadimai ke zagaye da ita, kowanne da aikin dayakeyi. Shigowar mu tasakasu kowa tasaki tanemi hanyar fita kamar yanda tabasu umarni. Bai saki hannuna ba har muka k'arisa gabanta, yayinda ita kuma idonta ke akan hannayenmu dake sark'e dana juna ko k'yaftawa batayi.
Saida ya taimaka min na zauna bisa tattausan carpet d'in dake falon, gaf da mama Fulani kad'an, sannan shima ya zauna kusa dani.
¡°Ranki ya dad'e barka da hutawa¡±. Nima sai bayi saurin gaisheta.
Cikeda izza da tak'ama ta d'ago idanu tana kallonmu, a raina nace (ga wadda tafi Galadima izza ashe, ko dai itace sarkin??)..
Kamarma bazata amsaba, saikuma naga ta gyara zamanta, idonta a kaina tana k'aremin kallo, ¡°sai yanzu ka gadamar zuwa gaida mutanen saboda giyar amarci na kwasarka?¡±.
Wani k'asaitaccen murmushi Galadima yasaki, Wanda ban ta6a Sanin ya iya shiba, ¡°kusan haka ranki ya dad'e, kinsan masu iya magana kance amarya kota buzuzu? ce d'okinta akeyi, bare ni kuma mai wannan dirarriyar macen doguwa k'yak'yk'yawa abun buk'atar kowanne namiji¡±.
Idanu na zaro domin mamakin maganarsa, kakarsa yake fad'ama hakan?. maganarta Ce yaja hankalina itama........
Saida ta yamutsa fuska tana guntun murmushi, duk da maganar Galadima ta daki zuciyarta kwarai da gaske, ta kalleni da k'yau, ¡°to ke dirarriyar mace abinda mijin naki yafad'a gaskiyane kuwa? dan mu bamu gani a k'asa ba¡±.
Gabana yashiga fad'uwa, dan bansan mizan Ce mataba, 6oyayyiyar ajiyar zuciya na sauke saboda jin Galadima na bata amsa, dukda kuma amsar tashi itama tazomin a rud'ani.
¡°to ranki ya dad'e miye amfanin gani a k'asan?, tunda nida ALLAH ya halattama ganin naga kayana¡±.
Yanzu kam a kufule tace, ¡°a titi ko?¡±.
Ya murmusa yana kallona, ¡°tunda Nina gani ai babu damuwa ranki ya dad'e, koda a titinne kuwa, bawai dole bane saike kin gani a gida ba¡±.
Rasama mizata cemasa tayi, sai can tace inbanga na matarka ba ai naga na Uwarka da yayar uwarka ko?¡±.
¡°well hakanefa ranki ya dad'e, amma nasan kafin kiga nasu, kema anga naki, so banga laifin hakanba ai¡±.
Kutt, tsantsar 6acin rai na hanga a fuskar mama Fulani kuwa, nidai kam sun d'aure kai na da wannan zantuka nasu masu kama da gugar zana, wannan dai baza'a kirashi wasan jika da kaka ba, dan baimayi kama da wasanba, nataso gidanmu na yawa da tun ina k'aramata nagama sanin miye habaici miye gugar zana ko shagu6e. tabbas naji a raina akwai lauje cikin nad'i gameda wannan masarautar, dan tundaga zuwana zuwa yanzu naci karo da abubuwan mamaki bila adadin, ashe ba'a rabu da bukarba an haifi habu kenan, nabaro guguwar gidanmu na fad'a tarnak'in gidan sarauta mai wahalar zama, ni dai ALLAH ka taimakeni komai yafita filima kafin shekara d'ayarnan na kama gabana, bazan iya da kitimurmurar wannan gidan sarautar ba gaskiya.
Mun mata sallama muka fito tana jifan Galadima da kalmar ¡°fand'arrare mara mutunci, wlhy zanyi maganin kane, amma zan kira uwar taka naji idan itace ta baka wannan sak'on kabani¡±.
Baice uffanba sai murmushi daya saki yakamani na tashi, munje bakin k'ofar zamu fita yajuyo yana kallonta, salute nata yayi sannan yace, ¡°da safe za'a kawo miki jinin budurcin matata OK?¡±.
Gaba nane yafad'i, da mamakin yanda yay furucin babu ko kunya bare shakka. nidai kam narasa yanda zan fassara wannan lamari, har muka shiga motar ina juya zantuttukansu a raina.
Mun isa sashen dayafi kowanne sashe girma a gidan, sannan ya had'u iya had'uwa shima, Hadimai sunfi yawa anan fiye da ko ina, anan d'inma dai gaisuwar ce aketa mana.
Mun isa wani k'ofar mai azabar k'yau, matar dake zaune a k'aramin falon farko ta rissinar da kanta tana fad'in ¡°lale marhabin da Galadima, Gimbiya barkanki da zuwa fadar masarautar gagara badau¡±.
Murmushi nayi na jinjina mata kai, amma gogan naku fuska a d'inke yace ¡°Amana iso ga mai martaba idan bai kwantaba jakadiya¡±.
¡°angama ranka ya dad'e, 6auna mai tafiyar k'asaita, bajimin zaki sa d'auka sa yak'i, magajin masarautar gagara badau........
Hannu ya d'aga mata alamar ya isheshi haka..
Ruf tarufe bakinta sannan tashige wata k'ofar, kusan mintuna 5 saigata yafito tana fad'in mu shigo.
Jama'a karkuce nayi k'auyanci, tabbas ni Munaya yau naga daular duniya, dolene sarakuna suringa tunanin kamarma bazasu mutuba, yo irin wannan daular inbakayi yak'i da shaid'anba ai bautar ALLAH ma saika bari, dole suke halaka juna akan sarauta kam lallai.
Wanda nakeda tabbacin shine sarki yana kishingid'e a kilisarsa, idonsa bisa TV yana kallon labarai, sai wata hamshak'iyar mace dake cikin ado na kece raini da alfarma zaune a gefensa, koba a fad'a makaba kasan matar sarkice.
Yanzu ma har gabansu muka isa hannun na cikin nasa, dukda mutsu-mutsun kwata danakeyi yak'i saki, saima k'ara damk'ewa da yayi, nesa dasu k'ad'an muka zauna, cikeda girmama Galadima yace ¡°barka da dare Abba?¡±.
Murmushi sarki yayi, yace, ¡°Galadima sai yanzu ake ganinka?¡±.
Murmushi yayi yana shafa gefen wuya alamar jin kunya, ya kalli matar yace ¡°barka da hutawa ranki ya dad'e¡±.
Fuskarta d'auke da fara'a ta amsa masa..
Nima na rissina na gaidasu cikin tsantsar ladabi.
Sun kar6amin fiye da yanda nayi zato, matar tamik'amin hannu alamar